< Luka 21 >

1 Yesu ya tada ido sai ya ga mutane masu arziki wadanda suke saka baikonsu a cikin ma'aji.
Ayant levé les yeux, Jésus vit des riches qui mettaient leurs offrandes dans le trésor du temple.
2 Ya ga wata gwauruwa matalauciya tana saka anini biyu a ciki.
Il vit aussi une pauvre veuve qui y mettait deux pites.
3 Sai ya ce, “Gaskiya ina gaya maku, wannan matalauciyar gwauruwa ta saka fiye da dukansu.
Et il dit: Je vous dis en vérité, que cette pauvre veuve a plus mis que personne.
4 Duka wadannan sun bayar da baikonsu daga cikin yalwarsu. Amma wannan gwauruwan, daga cikin talaucin ta, ta saka dukan iyakar kudinta na zaman gari da take da shi.”
Car tous ceux-là ont mis, dans les offrandes de Dieu, de leur superflu; mais celle-ci y a mis de son nécessaire tout ce qu'elle avait pour vivre.
5 Kamar yadda wadansu suke maganan haikali, yadda aka yi masa ado da duwatsu masu daraja da bayebaye, ya ce,
Et comme quelques-uns disaient que le temple était orné de belles pierres et d'offrandes, il dit:
6 “Game da wadannan abubuwa da ku ke gani, rana tana zuwa da ba dutse ko daya da zai zauna kan dan'uwansa da ba za a rushe kasa ba.”
Vous contemplez ces choses! Des jours viendront où il n'y sera laissé pierre sur pierre, qui ne soit renversée.
7 Sai suka yi masa tambaya, cewa, “Malam, yaushe ne wadannan abubuwan zasu faru? Menene kuma zai zama alama sa'adda wadannan abubuwa suna shirin faruwa?”
Et ils lui demandèrent: Maître, quand donc ces choses arriveront-elles, et par quel signe connaîtra-t-on qu'elles sont sur le point d'arriver?
8 Yesu ya amsa, “Ku yi hankali kada a rude ku. Gama dayawa zasu zo a cikin sunana, suna cewa, 'Ni ne shi,' kuma, 'Lokaci ya yi kusa.' Kada ku bi su.
Et il dit: Prenez garde de ne pas être séduits; car plusieurs viendront en mon nom, disant: C'est moi qui suis le Christ, et le temps approche. Ne les suivez donc pas.
9 Sa'adda ku ka ji game da yakoki da hargitsi, kada ku firgita, dole ne wadannan abubuwa su faru tukuna, amma karshe ba zai faru nan da nan ba.”
Or quand vous entendrez parler de guerres et de séditions, ne vous épouvantez pas; car il faut que ces choses arrivent auparavant; mais ce ne sera pas si tôt la fin.
10 Sa'annan ya ce masu, “Al'umma za ta tasar ma al'umma, mulki kuma za ya tasar wa mulki.
Il leur dit aussi: Une nation s'élèvera contre une autre nation, et un royaume contre un autre royaume;
11 Za a yi babbar girgizan kasa, a wurare dabam dabam kuma za a yi yunwa da annoba. Za a yi al'amura masu ban tsoro da manyan alamu daga sama.
Et il y aura de grands tremblements de terre en divers lieux, et des famines et des pestes; et il paraîtra des choses épouvantables, et de grands signes dans le ciel.
12 Amma kafin abubuwan nan duka, za su kama ku, su kuma tsananta maku, suna mika ku ga majami'u da kuma gidajen kurkuku, za su kawo ku gaban sarakuna da gwamnoni saboda sunana.
Mais, avant tout cela, ils mettront les mains sur vous, et vous persécuteront, vous livrant aux synagogues, et vous mettant en prison, et vous menant devant les rois et devant les gouverneurs, à cause de mon nom.
13 Zai zamar maku zarafin shaida.
Et cela sera pour vous une occasion de témoignage.
14 Saboda haka ku kudurta a ranku kada ku shirya yadda za ku amsa,
Mettez-vous donc dans l'esprit de ne point préméditer votre défense.
15 gama ni zan ba ku kalmomi da hikima, wadda dukan makiyanku ba za su yi tsayayya ko su karyata ku ba.
Car je vous donnerai une bouche et une sagesse à laquelle tous vos adversaires ne pourront contredire, ni résister.
16 Amma har da mahaifa da 'yan'uwa da dangi da abokai za su bashe ku, su kuma kashe wadansun ku.
Vous serez même livrés par vos parents, par vos frères, par vos proches et par vos amis; et ils feront mourir plusieurs d'entre vous.
17 Kowa zai ki ku saboda sunana.
Et vous serez haïs de tout le monde, à cause de mon nom.
18 Amma ba ko gashin kanku da zai hallaka.
Mais il ne se perdra pas un cheveu de votre tête.
19 A cikin hankurin ku za ku ribato rayukanku.
Possédez vos âmes par votre patience.
20 Sa'adda ku ka ga Urushalima tana kewaye da sojoji, sai ku sani da cewa faduwarta ta yi kusa.
Et quand vous verrez Jérusalem environnée par les armées, sachez que sa désolation approche.
21 Sai wadanda su ke Yahudiya su gudu zuwa kan tuddai, wadanda suke tsakiyar gari kuma su tafi, kada su bar wadanda suke kauyuka su shigo ciki.
Alors, que ceux qui seront dans la Judée s'enfuient aux montagnes; que ceux qui seront au milieu de Jérusalem se retirent; et que ceux qui seront à la campagne ne rentrent point.
22 Gama wadannan ranakun ramako ne, saboda duka abubuwan da aka rubuta su cika.
Car ce seront des jours de châtiment, afin que toutes les choses qui sont écrites s'accomplissent.
23 Kaiton wadanda suke da juna biyu da masu ba da mama a wannan kwanakin! Gama za a sha kunci mai girma a kasan, da fushi kuma zuwa ga mutanen nan.
Malheur aux femmes enceintes, et à celles qui allaiteront en ces jours-là; car il y aura une grande calamité sur ce pays, et de la colère contre ce peuple.
24 Za su fadi ta kaifin takobi kuma za a kai su cikin bauta ga dukan kasashe, al'ummai za su tattake Urushalima, har ya zuwa lokacin al'ummai ya cika.
Ils tomberont sous le tranchant de l'épée, et ils seront menés captifs parmi toutes les nations, et Jérusalem sera foulée par les nations, jusqu'à ce que les temps des nations soient accomplis.
25 Za a ga alamomi cikin rana da wata da kuma taurari. A duniya kuma, al'ummai za su sha kunci, za su rude saboda rurin teku da rakuman ruwa.
Et il y aura des signes dans le soleil, dans la lune et dans les étoiles; et sur la terre, les peuples seront dans la consternation et ne sachant que devenir, la mer et les flots faisant un grand bruit.
26 Mutane za su suma da tsoro da kuma da tunanin abubuwa da za su abko wa duniya. Gama za a girgiza ikokin sammai.
Les hommes seront comme rendant l'âme de frayeur, dans l'attente des choses qui surviendront dans le monde; car les puissances des cieux seront ébranlées.
27 Sa'annan za su ga Dan Mutum yana zuwa a cikin gajimarai da iko da daukaka mai girma.
Et alors ils verront venir le Fils de l'homme sur une nuée, avec une grande puissance et une grande gloire.
28 Amma sa'adda wadannan abubuwa suka fara faruwa, tashi saye, sai ku daga kanku sama, saboda ceton ku ya kusato.”
Or quand ces choses commenceront d'arriver, regardez en haut, et levez la tête, parce que votre délivrance approche.
29 Yesu ya bada misali, “Duba itacen baure, da duka itatuwa.
Et il leur dit une similitude: Voyez le figuier et tous les arbres;
30 Sa'adda su ke fitar da ganye, za ku gani da kanku cewa bazara ta yi kusa kuma.
Quand ils poussent, vous jugez de vous-mêmes, en les voyant, que l'été est proche.
31 Haka kuma, sa'adda ku ka ga wadannan abubuwa suna faruwa, ku sani cewa mulkin Allah ya yi kusa.
De même, lorsque vous verrez arriver ces choses, sachez que le royaume de Dieu est proche.
32 Gaskiya, na ke gaya maku, wannan zamani ba za ya shude ba, sai duka abubuwan nan sun faru.
Je vous dis en vérité, que cette génération ne passera point, que toutes ces choses n'arrivent.
33 Sama da kasa za su shude, amma maganata ba za ta shude ba.
Le ciel et la terre passeront, mais mes paroles ne passeront point.
34 Amma ku lura da kanku, domin kada ku nawaita zuciyarku da tararradin duniya da shayeshaye da damuwa ta rayuwa. Gama ranar za ta zo babu shiri
Prenez donc garde à vous-mêmes, de peur que vos cœurs ne soient appesantis par la débauche, par l'ivrognerie et par les inquiétudes de cette vie; et que ce jour-là ne vous surprenne subitement.
35 kamar tarko. Gama zai zo akan kowa da ke rayuwa a fuskar dukan duniya.
Car il surprendra comme un filet tous ceux qui habitent sur la face de la terre.
36 Amma ku zama a fadake kowanne lokaci, kuna addu'a domin ku iya samun karfin tserewa dukan wadannan abubuwa da za su faru, da kuma yadda za ku tsaya a gaban Dan Mutum.”
Veillez donc, et priez en tout temps, afin que vous soyez trouvés dignes d'éviter toutes ces choses qui doivent arriver, et de subsister devant le Fils de l'homme.
37 Da rana yana koyarwa a cikin haikali, dukan dare kuma yakan tafi dutsen da a ke kira zaitun.
Or, Jésus enseignait dans le temple pendant le jour, et, la nuit, il sortait et se tenait sur la montagne appelée des Oliviers.
38 Dukan mutane suka rika zuwa wurinsa da sassafe domin su ji shi a haikali.
Et, dès le point du jour, tout le peuple venait à lui dans le temple pour l'écouter.

< Luka 21 >