< Luka 21 >

1 Yesu ya tada ido sai ya ga mutane masu arziki wadanda suke saka baikonsu a cikin ma'aji.
Jésus, ayant levé les yeux, vit les riches qui mettaient leurs offrandes dans le tronc.
2 Ya ga wata gwauruwa matalauciya tana saka anini biyu a ciki.
Il vit aussi une femme, une veuve très pauvre, qui y mettait deux pites;
3 Sai ya ce, “Gaskiya ina gaya maku, wannan matalauciyar gwauruwa ta saka fiye da dukansu.
et il dit: «Je vous assure que cette pauvre veuve a mis plus que personne,
4 Duka wadannan sun bayar da baikonsu daga cikin yalwarsu. Amma wannan gwauruwan, daga cikin talaucin ta, ta saka dukan iyakar kudinta na zaman gari da take da shi.”
car tous les autres ont fait offrande à Dieu de leur superflu, tandis qu'elle a donné de son nécessaire, tout ce qu'elle avait pour vivre.
5 Kamar yadda wadansu suke maganan haikali, yadda aka yi masa ado da duwatsu masu daraja da bayebaye, ya ce,
Comme quelques personnes parlaient du temple, des pierres magnifiques et des offrandes qui l'ornent, Jésus dit:
6 “Game da wadannan abubuwa da ku ke gani, rana tana zuwa da ba dutse ko daya da zai zauna kan dan'uwansa da ba za a rushe kasa ba.”
«Le temps viendra où, de tout ce que vous regardez là, il ne restera pierre sur pierre qui ne soit renversée.»
7 Sai suka yi masa tambaya, cewa, “Malam, yaushe ne wadannan abubuwan zasu faru? Menene kuma zai zama alama sa'adda wadannan abubuwa suna shirin faruwa?”
Ses disciples lui demandèrent: «Maître, quand sera-ce donc, et quel sera le signe précurseur de cet événement?»
8 Yesu ya amsa, “Ku yi hankali kada a rude ku. Gama dayawa zasu zo a cikin sunana, suna cewa, 'Ni ne shi,' kuma, 'Lokaci ya yi kusa.' Kada ku bi su.
Il dit: «Prenez garde de vous laisser séduire; car plusieurs viendront sous mon nom, disant: «C'est moi qui suis le Messie, et le temps est proche.» Ne vous attachez pas à eux.
9 Sa'adda ku ka ji game da yakoki da hargitsi, kada ku firgita, dole ne wadannan abubuwa su faru tukuna, amma karshe ba zai faru nan da nan ba.”
Quand vous entendrez parler de guerres et de troubles, ne vous alarmez pas; car il faut que cela arrive premièrement, mais la fin ne viendra pas de sitôt.»
10 Sa'annan ya ce masu, “Al'umma za ta tasar ma al'umma, mulki kuma za ya tasar wa mulki.
Alors il ajouta: «Une nation s'élèvera contre une nation, et un royaume contre un royaume;
11 Za a yi babbar girgizan kasa, a wurare dabam dabam kuma za a yi yunwa da annoba. Za a yi al'amura masu ban tsoro da manyan alamu daga sama.
il y aura de grands tremblements de terre, et çà et là des pestes et des famines; et il paraîtra dans le ciel d'effrayants phénomènes et de grands signes.
12 Amma kafin abubuwan nan duka, za su kama ku, su kuma tsananta maku, suna mika ku ga majami'u da kuma gidajen kurkuku, za su kawo ku gaban sarakuna da gwamnoni saboda sunana.
Mais auparavant l’on se saisira de vous, et l’on vous persécutera: on vous traînera dans les synagogues et dans les prisons; on vous traduira devant les rois et les gouverneurs à cause de mon nom.
13 Zai zamar maku zarafin shaida.
Cela vous arrivera pour que vous me rendiez témoignage.
14 Saboda haka ku kudurta a ranku kada ku shirya yadda za ku amsa,
Mettez-vous donc bien dans l'esprit de ne point préparer de défense,
15 gama ni zan ba ku kalmomi da hikima, wadda dukan makiyanku ba za su yi tsayayya ko su karyata ku ba.
car je vous donnerai une parole et une sagesse, à laquelle tous vos adversaires ne pourront ni répondre, ni résister.
16 Amma har da mahaifa da 'yan'uwa da dangi da abokai za su bashe ku, su kuma kashe wadansun ku.
Vous serez livrés même par vos pères et par vos mères, par vos frères, par vos parents et par vos amis; plusieurs d'entre vous seront mis à mort,
17 Kowa zai ki ku saboda sunana.
et vous serez haïs de tout le monde à cause de mon nom;
18 Amma ba ko gashin kanku da zai hallaka.
mais il ne se perdra pas un cheveu de votre tête:
19 A cikin hankurin ku za ku ribato rayukanku.
par votre persévérance vous conquerrez vos âmes.»
20 Sa'adda ku ka ga Urushalima tana kewaye da sojoji, sai ku sani da cewa faduwarta ta yi kusa.
«Lorsque vous verrez que Jérusalem va être investie par les armées, sachez que sa ruine est proche.
21 Sai wadanda su ke Yahudiya su gudu zuwa kan tuddai, wadanda suke tsakiyar gari kuma su tafi, kada su bar wadanda suke kauyuka su shigo ciki.
Alors que ceux qui sont en Judée s'enfuient aux montagnes; que ceux qui demeurent dans la ville en sortent, et que ceux qui demeurent dans les campagnes n'y entrent point;
22 Gama wadannan ranakun ramako ne, saboda duka abubuwan da aka rubuta su cika.
parce que ce sont les temps où la justice va accomplir tout ce qui est écrit.
23 Kaiton wadanda suke da juna biyu da masu ba da mama a wannan kwanakin! Gama za a sha kunci mai girma a kasan, da fushi kuma zuwa ga mutanen nan.
Malheur aux femmes qui seront enceintes et à celles qui allaiteront en ce temps-là! car une grande calamité fondra sur le pays, et un grand châtiment sera, infligé à ce peuple:
24 Za su fadi ta kaifin takobi kuma za a kai su cikin bauta ga dukan kasashe, al'ummai za su tattake Urushalima, har ya zuwa lokacin al'ummai ya cika.
les uns tomberont sous le tranchant de l'épée, les autres seront emmenés en esclavage parmi toutes les nations, et Jérusalem sera foulée par les Gentils, jusqu’à ce que les temps des Gentils soient accomplis.
25 Za a ga alamomi cikin rana da wata da kuma taurari. A duniya kuma, al'ummai za su sha kunci, za su rude saboda rurin teku da rakuman ruwa.
Et il y aura des signes extraordinaires dans le soleil, dans la lune et dans les étoiles; et sur la terre, on verra l'angoisse des nations troublées par le fracas de la mer et des flots,
26 Mutane za su suma da tsoro da kuma da tunanin abubuwa da za su abko wa duniya. Gama za a girgiza ikokin sammai.
et celle des hommes mourant de frayeur dans l'attente des événements qui menacent la terre; car les puissances des cieux seront ébranlées.
27 Sa'annan za su ga Dan Mutum yana zuwa a cikin gajimarai da iko da daukaka mai girma.
Alors on verra le Fils de l'homme venir dans une nuée, revêtu d'une grande puissance et d'une grande gloire.»
28 Amma sa'adda wadannan abubuwa suka fara faruwa, tashi saye, sai ku daga kanku sama, saboda ceton ku ya kusato.”
Quand ces phénomènes commenceront à arriver redressez-vous et levez la tête, parce que votre délivrance approche.
29 Yesu ya bada misali, “Duba itacen baure, da duka itatuwa.
Et il ajouta une parabole: «Voyez le figuier et tous les arbres:
30 Sa'adda su ke fitar da ganye, za ku gani da kanku cewa bazara ta yi kusa kuma.
dès qu'ils ont commencé à pousser, vous connaissez de vous-mêmes, en les voyant, que déjà l'été est proche;
31 Haka kuma, sa'adda ku ka ga wadannan abubuwa suna faruwa, ku sani cewa mulkin Allah ya yi kusa.
de même, quand vous verrez ces événements se produire, sachez que le royaume de Dieu est proche.
32 Gaskiya, na ke gaya maku, wannan zamani ba za ya shude ba, sai duka abubuwan nan sun faru.
En vérité, je vous dis que cette génération ne passera point, que tous ces événements n'arrivent.
33 Sama da kasa za su shude, amma maganata ba za ta shude ba.
Le ciel et la terre passeront, mais mes paroles ne passeront point.
34 Amma ku lura da kanku, domin kada ku nawaita zuciyarku da tararradin duniya da shayeshaye da damuwa ta rayuwa. Gama ranar za ta zo babu shiri
Prenez garde à vous-mêmes; craignez que vos coeurs ne viennent à s'appesantir par les excès, par l'ivresse et par les soucis de la vie, et que ce jour ne fonde sur vous à l’improviste;
35 kamar tarko. Gama zai zo akan kowa da ke rayuwa a fuskar dukan duniya.
car il viendra, comme un filet, s'abattre sur tous ceux qui habitent sur la face de la terre.
36 Amma ku zama a fadake kowanne lokaci, kuna addu'a domin ku iya samun karfin tserewa dukan wadannan abubuwa da za su faru, da kuma yadda za ku tsaya a gaban Dan Mutum.”
Mais veillez, priant en tout temps, afin d'être jugés dignes d'échapper à tous ces malheurs à venir, et de trouver place devant le Fils de l'homme.»
37 Da rana yana koyarwa a cikin haikali, dukan dare kuma yakan tafi dutsen da a ke kira zaitun.
Jésus passait ses journées dans le temple, à enseigner, et il s'en allait passer les nuits à la montagne appelée Bois d'oliviers;
38 Dukan mutane suka rika zuwa wurinsa da sassafe domin su ji shi a haikali.
et tout le peuple venait dès le matin vers lui, dans le temple, pour l'entendre.

< Luka 21 >