< Luka 21 >

1 Yesu ya tada ido sai ya ga mutane masu arziki wadanda suke saka baikonsu a cikin ma'aji.
Et comme il regardait, il vit des riches qui jetaient leurs dons au trésor.
2 Ya ga wata gwauruwa matalauciya tana saka anini biyu a ciki.
Et il vit aussi une pauvre veuve qui y jetait deux pites.
3 Sai ya ce, “Gaskiya ina gaya maku, wannan matalauciyar gwauruwa ta saka fiye da dukansu.
Et il dit: En vérité, je vous dis que cette pauvre veuve a jeté plus que tous [les autres];
4 Duka wadannan sun bayar da baikonsu daga cikin yalwarsu. Amma wannan gwauruwan, daga cikin talaucin ta, ta saka dukan iyakar kudinta na zaman gari da take da shi.”
car tous ceux-ci ont jeté aux offrandes [de Dieu] de leur superflu, mais celle-ci y a jeté de sa pénurie, tout ce qu’elle avait pour vivre.
5 Kamar yadda wadansu suke maganan haikali, yadda aka yi masa ado da duwatsu masu daraja da bayebaye, ya ce,
Et comme quelques-uns parlaient du temple [et disaient] qu’il était orné de belles pierres et de dons, il dit:
6 “Game da wadannan abubuwa da ku ke gani, rana tana zuwa da ba dutse ko daya da zai zauna kan dan'uwansa da ba za a rushe kasa ba.”
Quant à ces choses que vous regardez, les jours viendront où il ne sera laissé pierre sur pierre qui ne soit jetée à bas.
7 Sai suka yi masa tambaya, cewa, “Malam, yaushe ne wadannan abubuwan zasu faru? Menene kuma zai zama alama sa'adda wadannan abubuwa suna shirin faruwa?”
Et ils l’interrogèrent, disant: Maître, quand donc ces choses auront-elles lieu, et quel sera le signe quand ces choses devront arriver?
8 Yesu ya amsa, “Ku yi hankali kada a rude ku. Gama dayawa zasu zo a cikin sunana, suna cewa, 'Ni ne shi,' kuma, 'Lokaci ya yi kusa.' Kada ku bi su.
Et il dit: Prenez garde que vous ne soyez séduits; car plusieurs viendront en mon nom, disant: C’est moi, et le temps est proche; n’allez point après eux.
9 Sa'adda ku ka ji game da yakoki da hargitsi, kada ku firgita, dole ne wadannan abubuwa su faru tukuna, amma karshe ba zai faru nan da nan ba.”
Et quand vous entendrez parler de guerres et de séditions, ne vous épouvantez pas; car il faut que ces choses arrivent premièrement; mais la fin ne sera pas tout aussitôt.
10 Sa'annan ya ce masu, “Al'umma za ta tasar ma al'umma, mulki kuma za ya tasar wa mulki.
Alors il leur dit: Nation s’élèvera contre nation, et royaume contre royaume;
11 Za a yi babbar girgizan kasa, a wurare dabam dabam kuma za a yi yunwa da annoba. Za a yi al'amura masu ban tsoro da manyan alamu daga sama.
et il y aura de grands tremblements de terre en divers lieux, et des famines, et des pestes; et il y aura des sujets d’épouvantement et de grands signes du ciel.
12 Amma kafin abubuwan nan duka, za su kama ku, su kuma tsananta maku, suna mika ku ga majami'u da kuma gidajen kurkuku, za su kawo ku gaban sarakuna da gwamnoni saboda sunana.
Mais, avant toutes ces choses, ils mettront les mains sur vous, et vous persécuteront, vous livrant aux synagogues et [vous mettant] en prison; et vous serez menés devant les rois et les gouverneurs à cause de mon nom.
13 Zai zamar maku zarafin shaida.
Et cela se tournera pour vous en témoignage.
14 Saboda haka ku kudurta a ranku kada ku shirya yadda za ku amsa,
Mettez donc dans vos cœurs de ne pas vous préoccuper à l’avance de votre défense,
15 gama ni zan ba ku kalmomi da hikima, wadda dukan makiyanku ba za su yi tsayayya ko su karyata ku ba.
car moi je vous donnerai une bouche et une sagesse, à laquelle tous vos adversaires ne pourront répondre ou résister.
16 Amma har da mahaifa da 'yan'uwa da dangi da abokai za su bashe ku, su kuma kashe wadansun ku.
Et vous serez aussi livrés par des parents et par des frères, et par des proches et par des amis, et on fera mourir [quelques-uns] d’entre vous;
17 Kowa zai ki ku saboda sunana.
et vous serez haïs de tous, à cause de mon nom.
18 Amma ba ko gashin kanku da zai hallaka.
Et pas un cheveu de votre tête ne périra.
19 A cikin hankurin ku za ku ribato rayukanku.
Possédez vos âmes par votre patience.
20 Sa'adda ku ka ga Urushalima tana kewaye da sojoji, sai ku sani da cewa faduwarta ta yi kusa.
Et quand vous verrez Jérusalem environnée d’armées, sachez alors que sa désolation est proche.
21 Sai wadanda su ke Yahudiya su gudu zuwa kan tuddai, wadanda suke tsakiyar gari kuma su tafi, kada su bar wadanda suke kauyuka su shigo ciki.
Alors, que ceux qui sont en Judée s’enfuient dans les montagnes; et que ceux qui sont au milieu de Jérusalem s’en retirent; et que ceux qui sont dans les campagnes n’entrent pas en elle.
22 Gama wadannan ranakun ramako ne, saboda duka abubuwan da aka rubuta su cika.
Car ce sont là des jours de vengeance; afin que toutes les choses qui sont écrites soient accomplies.
23 Kaiton wadanda suke da juna biyu da masu ba da mama a wannan kwanakin! Gama za a sha kunci mai girma a kasan, da fushi kuma zuwa ga mutanen nan.
Mais malheur à celles qui sont enceintes et à celles qui allaitent en ces jours-là! car il y aura une grande détresse sur le pays, et de la colère contre ce peuple.
24 Za su fadi ta kaifin takobi kuma za a kai su cikin bauta ga dukan kasashe, al'ummai za su tattake Urushalima, har ya zuwa lokacin al'ummai ya cika.
Et ils tomberont sous le tranchant de l’épée, et seront menés captifs parmi toutes les nations; et Jérusalem sera foulée aux pieds par les nations jusqu’à ce que les temps des nations soient accomplis.
25 Za a ga alamomi cikin rana da wata da kuma taurari. A duniya kuma, al'ummai za su sha kunci, za su rude saboda rurin teku da rakuman ruwa.
Et il y aura des signes dans le soleil et la lune et les étoiles, et sur la terre une angoisse des nations en perplexité devant le grand bruit de la mer et des flots,
26 Mutane za su suma da tsoro da kuma da tunanin abubuwa da za su abko wa duniya. Gama za a girgiza ikokin sammai.
les hommes rendant l’âme de peur et à cause de l’attente des choses qui viennent sur la terre habitée, car les puissances des cieux seront ébranlées.
27 Sa'annan za su ga Dan Mutum yana zuwa a cikin gajimarai da iko da daukaka mai girma.
Et alors on verra le fils de l’homme venant sur une nuée avec puissance et une grande gloire.
28 Amma sa'adda wadannan abubuwa suka fara faruwa, tashi saye, sai ku daga kanku sama, saboda ceton ku ya kusato.”
Et quand ces choses commenceront à arriver, regardez en haut, et levez vos têtes, parce que votre rédemption approche.
29 Yesu ya bada misali, “Duba itacen baure, da duka itatuwa.
Et il leur dit une parabole: Voyez le figuier et tous les arbres:
30 Sa'adda su ke fitar da ganye, za ku gani da kanku cewa bazara ta yi kusa kuma.
quand ils ont déjà commencé à pousser, vous connaissez par vous-mêmes, en les voyant, que l’été est déjà proche.
31 Haka kuma, sa'adda ku ka ga wadannan abubuwa suna faruwa, ku sani cewa mulkin Allah ya yi kusa.
De même aussi vous, quand vous verrez arriver ces choses, sachez que le royaume de Dieu est proche.
32 Gaskiya, na ke gaya maku, wannan zamani ba za ya shude ba, sai duka abubuwan nan sun faru.
En vérité, je vous dis que cette génération ne passera point que tout ne soit arrivé.
33 Sama da kasa za su shude, amma maganata ba za ta shude ba.
Le ciel et la terre passeront, mais mes paroles ne passeront point.
34 Amma ku lura da kanku, domin kada ku nawaita zuciyarku da tararradin duniya da shayeshaye da damuwa ta rayuwa. Gama ranar za ta zo babu shiri
Et prenez garde à vous-mêmes, de peur que vos cœurs ne soient appesantis par la gourmandise et l’ivrognerie, et par les soucis de la vie, et que ce jour-là ne vous surprenne inopinément;
35 kamar tarko. Gama zai zo akan kowa da ke rayuwa a fuskar dukan duniya.
car il viendra comme un filet sur tous ceux qui habitent sur la face de toute la terre.
36 Amma ku zama a fadake kowanne lokaci, kuna addu'a domin ku iya samun karfin tserewa dukan wadannan abubuwa da za su faru, da kuma yadda za ku tsaya a gaban Dan Mutum.”
Veillez donc, priant en tout temps, afin que vous soyez estimés dignes d’échapper à toutes ces choses qui doivent arriver, et de vous tenir devant le fils de l’homme.
37 Da rana yana koyarwa a cikin haikali, dukan dare kuma yakan tafi dutsen da a ke kira zaitun.
Et il passait les jours dans le temple à enseigner; et les nuits il sortait et demeurait dans la montagne qui est appelée des Oliviers.
38 Dukan mutane suka rika zuwa wurinsa da sassafe domin su ji shi a haikali.
Et tout le peuple, dès le point du jour, venait à lui dans le temple, pour l’entendre.

< Luka 21 >