< Luka 21 >

1 Yesu ya tada ido sai ya ga mutane masu arziki wadanda suke saka baikonsu a cikin ma'aji.
Il leva les yeux et vit les riches qui mettaient leurs dons dans le trésor.
2 Ya ga wata gwauruwa matalauciya tana saka anini biyu a ciki.
Il vit une pauvre veuve qui jetait deux petites pièces d'airain.
3 Sai ya ce, “Gaskiya ina gaya maku, wannan matalauciyar gwauruwa ta saka fiye da dukansu.
Il dit: « Je vous le dis en vérité, cette pauvre veuve a mis plus qu'eux tous,
4 Duka wadannan sun bayar da baikonsu daga cikin yalwarsu. Amma wannan gwauruwan, daga cikin talaucin ta, ta saka dukan iyakar kudinta na zaman gari da take da shi.”
car tous ceux-là ont fait des dons à Dieu de leur superflu, mais elle, de sa pauvreté, a mis tout ce qu'elle avait pour vivre. »
5 Kamar yadda wadansu suke maganan haikali, yadda aka yi masa ado da duwatsu masu daraja da bayebaye, ya ce,
Comme certains parlaient du temple et de la façon dont il était décoré de belles pierres et de cadeaux, il dit:
6 “Game da wadannan abubuwa da ku ke gani, rana tana zuwa da ba dutse ko daya da zai zauna kan dan'uwansa da ba za a rushe kasa ba.”
« Quant à ces choses que vous voyez, les jours viendront où il ne restera pas ici une pierre sur une autre qui ne soit pas renversée. »
7 Sai suka yi masa tambaya, cewa, “Malam, yaushe ne wadannan abubuwan zasu faru? Menene kuma zai zama alama sa'adda wadannan abubuwa suna shirin faruwa?”
Ils lui demandèrent: « Maître, quand donc ces choses arriveront-elles? Quel est le signe que ces choses vont arriver? »
8 Yesu ya amsa, “Ku yi hankali kada a rude ku. Gama dayawa zasu zo a cikin sunana, suna cewa, 'Ni ne shi,' kuma, 'Lokaci ya yi kusa.' Kada ku bi su.
Il dit: « Prenez garde de ne pas vous laisser égarer, car plusieurs viendront en mon nom, disant: « C'est moi", et « Le temps est proche ». Ne les suivez donc pas.
9 Sa'adda ku ka ji game da yakoki da hargitsi, kada ku firgita, dole ne wadannan abubuwa su faru tukuna, amma karshe ba zai faru nan da nan ba.”
Quand vous entendrez parler de guerres et de troubles, ne soyez pas terrifiés, car il faut que ces choses arrivent d'abord, mais la fin ne viendra pas immédiatement. »
10 Sa'annan ya ce masu, “Al'umma za ta tasar ma al'umma, mulki kuma za ya tasar wa mulki.
Puis il leur dit: « Une nation s'élèvera contre une nation, et un royaume contre un royaume.
11 Za a yi babbar girgizan kasa, a wurare dabam dabam kuma za a yi yunwa da annoba. Za a yi al'amura masu ban tsoro da manyan alamu daga sama.
Il y aura de grands tremblements de terre, des famines et des pestes en divers lieux. Il y aura des terreurs et de grands signes venant du ciel.
12 Amma kafin abubuwan nan duka, za su kama ku, su kuma tsananta maku, suna mika ku ga majami'u da kuma gidajen kurkuku, za su kawo ku gaban sarakuna da gwamnoni saboda sunana.
Mais avant tout cela, on mettra la main sur vous, on vous persécutera, on vous livrera aux synagogues et aux prisons, on vous fera comparaître devant des rois et des gouverneurs, à cause de mon nom.
13 Zai zamar maku zarafin shaida.
Il en résultera pour vous un témoignage.
14 Saboda haka ku kudurta a ranku kada ku shirya yadda za ku amsa,
Mettez-vous donc dans la tête de ne pas réfléchir d'avance à la manière de répondre,
15 gama ni zan ba ku kalmomi da hikima, wadda dukan makiyanku ba za su yi tsayayya ko su karyata ku ba.
car je vous donnerai une bouche et une sagesse auxquelles tous vos adversaires ne pourront résister ni contredire.
16 Amma har da mahaifa da 'yan'uwa da dangi da abokai za su bashe ku, su kuma kashe wadansun ku.
Vous serez livrés même par vos parents, vos frères, vos proches et vos amis. Ils feront mettre à mort certains d'entre vous.
17 Kowa zai ki ku saboda sunana.
Vous serez haïs de tous les hommes à cause de mon nom.
18 Amma ba ko gashin kanku da zai hallaka.
Et pas un cheveu de votre tête ne périra.
19 A cikin hankurin ku za ku ribato rayukanku.
« C'est par votre endurance que vous gagnerez vos vies.
20 Sa'adda ku ka ga Urushalima tana kewaye da sojoji, sai ku sani da cewa faduwarta ta yi kusa.
« Mais quand vous verrez Jérusalem entourée d'armées, sachez que sa désolation est proche.
21 Sai wadanda su ke Yahudiya su gudu zuwa kan tuddai, wadanda suke tsakiyar gari kuma su tafi, kada su bar wadanda suke kauyuka su shigo ciki.
Alors, que ceux qui sont en Judée fuient vers les montagnes. Que ceux qui sont au milieu d'elle s'en aillent. Que ceux qui sont dans la campagne n'y entrent pas.
22 Gama wadannan ranakun ramako ne, saboda duka abubuwan da aka rubuta su cika.
Car ce sont des jours de vengeance, afin que s'accomplisse tout ce qui est écrit.
23 Kaiton wadanda suke da juna biyu da masu ba da mama a wannan kwanakin! Gama za a sha kunci mai girma a kasan, da fushi kuma zuwa ga mutanen nan.
Malheur aux femmes enceintes et à celles qui allaitent en ces jours-là! Car il y aura une grande détresse dans le pays et une grande colère pour ce peuple.
24 Za su fadi ta kaifin takobi kuma za a kai su cikin bauta ga dukan kasashe, al'ummai za su tattake Urushalima, har ya zuwa lokacin al'ummai ya cika.
Ils tomberont sous le tranchant de l'épée, et ils seront emmenés captifs dans toutes les nations. Jérusalem sera foulée aux pieds par les païens, jusqu'à ce que les temps des païens soient accomplis.
25 Za a ga alamomi cikin rana da wata da kuma taurari. A duniya kuma, al'ummai za su sha kunci, za su rude saboda rurin teku da rakuman ruwa.
Il y aura des signes dans le soleil, la lune et les étoiles; et sur la terre, l'angoisse des nations, dans la perplexité à cause du mugissement de la mer et des flots;
26 Mutane za su suma da tsoro da kuma da tunanin abubuwa da za su abko wa duniya. Gama za a girgiza ikokin sammai.
les hommes seront saisis de crainte et d'attente des choses qui vont arriver au monde, car les puissances des cieux seront ébranlées.
27 Sa'annan za su ga Dan Mutum yana zuwa a cikin gajimarai da iko da daukaka mai girma.
Alors ils verront le Fils de l'homme venant sur une nuée avec puissance et grande gloire.
28 Amma sa'adda wadannan abubuwa suka fara faruwa, tashi saye, sai ku daga kanku sama, saboda ceton ku ya kusato.”
Mais quand ces choses commenceront à arriver, regardez en haut et levez vos têtes, car votre rédemption est proche. »
29 Yesu ya bada misali, “Duba itacen baure, da duka itatuwa.
Il leur raconta une parabole. « Regardez le figuier et tous les arbres.
30 Sa'adda su ke fitar da ganye, za ku gani da kanku cewa bazara ta yi kusa kuma.
Quand ils bourgeonnent déjà, vous le voyez et vous savez par vous-mêmes que l'été est déjà proche.
31 Haka kuma, sa'adda ku ka ga wadannan abubuwa suna faruwa, ku sani cewa mulkin Allah ya yi kusa.
De même, vous aussi, quand vous voyez ces choses arriver, vous savez que le Royaume de Dieu est proche.
32 Gaskiya, na ke gaya maku, wannan zamani ba za ya shude ba, sai duka abubuwan nan sun faru.
En vérité, je vous le dis, cette génération ne passera pas que tout ne soit accompli.
33 Sama da kasa za su shude, amma maganata ba za ta shude ba.
Le ciel et la terre passeront, mais mes paroles ne passeront pas.
34 Amma ku lura da kanku, domin kada ku nawaita zuciyarku da tararradin duniya da shayeshaye da damuwa ta rayuwa. Gama ranar za ta zo babu shiri
« Prenez donc garde que vos cœurs ne s'appesantissent sous le poids des plaisirs de la fête, de l'ivresse et des soucis de la vie présente, et que ce jour ne vienne sur vous à l'improviste.
35 kamar tarko. Gama zai zo akan kowa da ke rayuwa a fuskar dukan duniya.
Car il viendra comme un piège pour tous ceux qui habitent à la surface de toute la terre.
36 Amma ku zama a fadake kowanne lokaci, kuna addu'a domin ku iya samun karfin tserewa dukan wadannan abubuwa da za su faru, da kuma yadda za ku tsaya a gaban Dan Mutum.”
Veillez donc en permanence, en priant pour que vous soyez jugés dignes d'échapper à toutes ces choses qui arriveront, et de vous présenter devant le Fils de l'homme. »
37 Da rana yana koyarwa a cikin haikali, dukan dare kuma yakan tafi dutsen da a ke kira zaitun.
Chaque jour, Jésus enseignait dans le temple, et chaque soir, il sortait et passait la nuit sur la montagne qu'on appelle le mont Olivet.
38 Dukan mutane suka rika zuwa wurinsa da sassafe domin su ji shi a haikali.
Tout le peuple venait de bon matin le trouver dans le temple pour l'écouter.

< Luka 21 >