< Luka 21 >

1 Yesu ya tada ido sai ya ga mutane masu arziki wadanda suke saka baikonsu a cikin ma'aji.
And he looked up, and saw rich men casting their gifts into the treasury.
2 Ya ga wata gwauruwa matalauciya tana saka anini biyu a ciki.
And he saw also a certain poor widow, casting in thither two mites.
3 Sai ya ce, “Gaskiya ina gaya maku, wannan matalauciyar gwauruwa ta saka fiye da dukansu.
And he said, Of a truth I say to you, that this poor widow hath cast in more than they all.
4 Duka wadannan sun bayar da baikonsu daga cikin yalwarsu. Amma wannan gwauruwan, daga cikin talaucin ta, ta saka dukan iyakar kudinta na zaman gari da take da shi.”
For all these have of their abundance cast in to the offerings of God: but she of her penury hath cast in all the living that she had.
5 Kamar yadda wadansu suke maganan haikali, yadda aka yi masa ado da duwatsu masu daraja da bayebaye, ya ce,
And as some spoke of the temple, that it was adorned with goodly stones, and gifts, he said,
6 “Game da wadannan abubuwa da ku ke gani, rana tana zuwa da ba dutse ko daya da zai zauna kan dan'uwansa da ba za a rushe kasa ba.”
[As for] these things which ye behold, the days will come, in which there shall not be left one stone upon another, that will not be thrown down.
7 Sai suka yi masa tambaya, cewa, “Malam, yaushe ne wadannan abubuwan zasu faru? Menene kuma zai zama alama sa'adda wadannan abubuwa suna shirin faruwa?”
And they asked him, saying, Master, but when will these things be? and what sign [will there be] when these things shall come to pass?
8 Yesu ya amsa, “Ku yi hankali kada a rude ku. Gama dayawa zasu zo a cikin sunana, suna cewa, 'Ni ne shi,' kuma, 'Lokaci ya yi kusa.' Kada ku bi su.
And he said, Take heed that ye be not deceived: for many will come in my name, saying, I am [Christ]; and the time draweth near: therefore go ye not after them.
9 Sa'adda ku ka ji game da yakoki da hargitsi, kada ku firgita, dole ne wadannan abubuwa su faru tukuna, amma karshe ba zai faru nan da nan ba.”
But when ye shall hear of wars, and commotions, be not terrified: for these things must first come to pass: but the end [is] not immediately.
10 Sa'annan ya ce masu, “Al'umma za ta tasar ma al'umma, mulki kuma za ya tasar wa mulki.
Then said he to them, Nation will rise against nation, and kingdom against kingdom:
11 Za a yi babbar girgizan kasa, a wurare dabam dabam kuma za a yi yunwa da annoba. Za a yi al'amura masu ban tsoro da manyan alamu daga sama.
And great earthquakes will be in divers places, and famines, and pestilences: and fearful sights, and great signs will there be from heaven.
12 Amma kafin abubuwan nan duka, za su kama ku, su kuma tsananta maku, suna mika ku ga majami'u da kuma gidajen kurkuku, za su kawo ku gaban sarakuna da gwamnoni saboda sunana.
But before all these they will lay their hands on you, and persecute [you], delivering [you] up to the synagogues, and into prisons, being brought before kings and rulers for my name's sake.
13 Zai zamar maku zarafin shaida.
And it shall turn to you for a testimony.
14 Saboda haka ku kudurta a ranku kada ku shirya yadda za ku amsa,
Settle [it] therefore in your hearts, not to meditate before what ye shall answer.
15 gama ni zan ba ku kalmomi da hikima, wadda dukan makiyanku ba za su yi tsayayya ko su karyata ku ba.
For I will give you a mouth and wisdom, which all your adversaries shall not be able to gainsay nor resist.
16 Amma har da mahaifa da 'yan'uwa da dangi da abokai za su bashe ku, su kuma kashe wadansun ku.
And ye will be betrayed both by parents, and brethren, and kinsmen, and friends; and [some] of you will they cause to be put to death.
17 Kowa zai ki ku saboda sunana.
And ye will be hated by all [men] for my name's sake.
18 Amma ba ko gashin kanku da zai hallaka.
But there shall not a hair of your head perish.
19 A cikin hankurin ku za ku ribato rayukanku.
In your patience possess ye your souls.
20 Sa'adda ku ka ga Urushalima tana kewaye da sojoji, sai ku sani da cewa faduwarta ta yi kusa.
And when ye shall see Jerusalem compassed with armies, then know that its desolation is nigh.
21 Sai wadanda su ke Yahudiya su gudu zuwa kan tuddai, wadanda suke tsakiyar gari kuma su tafi, kada su bar wadanda suke kauyuka su shigo ciki.
Then let them who are in Judea flee to the mountains; and let them who are in the midst of it depart [from it]; and let not them that are in the countries enter into it.
22 Gama wadannan ranakun ramako ne, saboda duka abubuwan da aka rubuta su cika.
For these are the days of vengeance, that all things which are written may be fulfilled.
23 Kaiton wadanda suke da juna biyu da masu ba da mama a wannan kwanakin! Gama za a sha kunci mai girma a kasan, da fushi kuma zuwa ga mutanen nan.
But woe to them that are with child, and to them that nurse infants in those days! for there shall be great distress in the land, and wrath upon this people.
24 Za su fadi ta kaifin takobi kuma za a kai su cikin bauta ga dukan kasashe, al'ummai za su tattake Urushalima, har ya zuwa lokacin al'ummai ya cika.
And they shall fall by the edge of the sword, and shall be led away captive into all nations: and Jerusalem shall be trodden down by the Gentiles, until the times of the Gentiles shall be fulfilled.
25 Za a ga alamomi cikin rana da wata da kuma taurari. A duniya kuma, al'ummai za su sha kunci, za su rude saboda rurin teku da rakuman ruwa.
And there shall be signs in the sun, and in the moon, and in the stars; and upon the earth distress of nations, with perplexity; the sea and the waves roaring;
26 Mutane za su suma da tsoro da kuma da tunanin abubuwa da za su abko wa duniya. Gama za a girgiza ikokin sammai.
Men's hearts failing them for fear, and for apprehension of those things which are coming on the earth: for the powers of heaven shall be shaken.
27 Sa'annan za su ga Dan Mutum yana zuwa a cikin gajimarai da iko da daukaka mai girma.
And then shall they see the Son of man coming in a cloud, with power and great glory.
28 Amma sa'adda wadannan abubuwa suka fara faruwa, tashi saye, sai ku daga kanku sama, saboda ceton ku ya kusato.”
And when these things begin to come to pass, then look up, and lift up your heads: for your redemption draweth nigh.
29 Yesu ya bada misali, “Duba itacen baure, da duka itatuwa.
And he spoke to them a parable; Behold the fig-tree, and all the trees;
30 Sa'adda su ke fitar da ganye, za ku gani da kanku cewa bazara ta yi kusa kuma.
When they now shoot forth, ye see and know of your ownselves that summer is now nigh at hand.
31 Haka kuma, sa'adda ku ka ga wadannan abubuwa suna faruwa, ku sani cewa mulkin Allah ya yi kusa.
So likewise ye, when ye see these things come to pass, know that the kingdom of God is nigh at hand.
32 Gaskiya, na ke gaya maku, wannan zamani ba za ya shude ba, sai duka abubuwan nan sun faru.
Verily I say to you, This generation shall not pass away, till all be fulfilled.
33 Sama da kasa za su shude, amma maganata ba za ta shude ba.
Heaven and earth shall pass away: but my word shall not pass away.
34 Amma ku lura da kanku, domin kada ku nawaita zuciyarku da tararradin duniya da shayeshaye da damuwa ta rayuwa. Gama ranar za ta zo babu shiri
And take heed to yourselves, lest at any time your hearts be overcharged with surfeiting and drunkenness, and cares of this life, and [so] that day come upon you unawares.
35 kamar tarko. Gama zai zo akan kowa da ke rayuwa a fuskar dukan duniya.
For as a snare shall it come on all them that dwell on the face of the whole earth.
36 Amma ku zama a fadake kowanne lokaci, kuna addu'a domin ku iya samun karfin tserewa dukan wadannan abubuwa da za su faru, da kuma yadda za ku tsaya a gaban Dan Mutum.”
Watch ye therefore, and pray always, that ye may be accounted worthy to escape all these things that shall come to pass, and to stand before the Son of man.
37 Da rana yana koyarwa a cikin haikali, dukan dare kuma yakan tafi dutsen da a ke kira zaitun.
And in the day-time he was teaching in the temple; and at night he went out, and abode in the mount that is called [the mount] of Olives.
38 Dukan mutane suka rika zuwa wurinsa da sassafe domin su ji shi a haikali.
And all the people came early in the morning to him in the temple, to hear him.

< Luka 21 >