< Luka 21 >

1 Yesu ya tada ido sai ya ga mutane masu arziki wadanda suke saka baikonsu a cikin ma'aji.
And Jesus looked upon the rich, who cast their oblations into the treasury.
2 Ya ga wata gwauruwa matalauciya tana saka anini biyu a ciki.
And he saw also a certain poor widow, who cast in two mites.
3 Sai ya ce, “Gaskiya ina gaya maku, wannan matalauciyar gwauruwa ta saka fiye da dukansu.
And he said: Truly I say to you, that this poor widow hath cast in more than any one.
4 Duka wadannan sun bayar da baikonsu daga cikin yalwarsu. Amma wannan gwauruwan, daga cikin talaucin ta, ta saka dukan iyakar kudinta na zaman gari da take da shi.”
For all they, from what was superfluous to them, have cast into the receptacle of oblations to God; but she, from her penury, hath cast in all that she possessed.
5 Kamar yadda wadansu suke maganan haikali, yadda aka yi masa ado da duwatsu masu daraja da bayebaye, ya ce,
And when some spoke of the temple, as adorned with goodly stones and oblations, Jesus said to them:
6 “Game da wadannan abubuwa da ku ke gani, rana tana zuwa da ba dutse ko daya da zai zauna kan dan'uwansa da ba za a rushe kasa ba.”
As for these things, on which ye gaze, the days will come, in which there will not be left a stone upon a stone, that is not cast down.
7 Sai suka yi masa tambaya, cewa, “Malam, yaushe ne wadannan abubuwan zasu faru? Menene kuma zai zama alama sa'adda wadannan abubuwa suna shirin faruwa?”
And they questioned him, and said: Teacher, when will these things be? And what is the sign that they are near to take place?
8 Yesu ya amsa, “Ku yi hankali kada a rude ku. Gama dayawa zasu zo a cikin sunana, suna cewa, 'Ni ne shi,' kuma, 'Lokaci ya yi kusa.' Kada ku bi su.
And he said to them: See, that ye be not deceived; for many will come in my name, and will say: I am Messiah and the time is near. But go ye not after them.
9 Sa'adda ku ka ji game da yakoki da hargitsi, kada ku firgita, dole ne wadannan abubuwa su faru tukuna, amma karshe ba zai faru nan da nan ba.”
And when ye shall hear of wars and commotions, be not afraid; for these things are previously to take place, but the end is not yet come.
10 Sa'annan ya ce masu, “Al'umma za ta tasar ma al'umma, mulki kuma za ya tasar wa mulki.
For nation will rise against nation, and kingdom against kingdom;
11 Za a yi babbar girgizan kasa, a wurare dabam dabam kuma za a yi yunwa da annoba. Za a yi al'amura masu ban tsoro da manyan alamu daga sama.
and great earthquakes will occur in several places, and famines, and pestilences; and there will be terrors, and trepidations, and great signs from heaven will be seen, and there will be great tempests.
12 Amma kafin abubuwan nan duka, za su kama ku, su kuma tsananta maku, suna mika ku ga majami'u da kuma gidajen kurkuku, za su kawo ku gaban sarakuna da gwamnoni saboda sunana.
But before all these things, they will lay hands upon you, and will persecute you, and will deliver you up to councils and to prison, and will arraign you before kings and governors, on account of my name.
13 Zai zamar maku zarafin shaida.
But it will be to you for a testimony.
14 Saboda haka ku kudurta a ranku kada ku shirya yadda za ku amsa,
And settle it in your hearts, that ye will not previously seek instruction for making a defence.
15 gama ni zan ba ku kalmomi da hikima, wadda dukan makiyanku ba za su yi tsayayya ko su karyata ku ba.
For I will give you a mouth and wisdom, which all your enemies will be unable to withstand.
16 Amma har da mahaifa da 'yan'uwa da dangi da abokai za su bashe ku, su kuma kashe wadansun ku.
And your parents, and your brothers, and your relatives, and your friends, will deliver you up, and cause some of you to die.
17 Kowa zai ki ku saboda sunana.
And ye will be hated by every one, on account of my name.
18 Amma ba ko gashin kanku da zai hallaka.
But a hair of your head shall not perish.
19 A cikin hankurin ku za ku ribato rayukanku.
And by your patience, will ye preserve your souls.
20 Sa'adda ku ka ga Urushalima tana kewaye da sojoji, sai ku sani da cewa faduwarta ta yi kusa.
And when ye shall see Jerusalem with an army encompassing it, then know ye, that its destruction draweth nigh.
21 Sai wadanda su ke Yahudiya su gudu zuwa kan tuddai, wadanda suke tsakiyar gari kuma su tafi, kada su bar wadanda suke kauyuka su shigo ciki.
Then let them who shall be in Judaea, flee to the mountain district; and let them, who are in the midst of it, flee away; and those in the fields, not enter it.
22 Gama wadannan ranakun ramako ne, saboda duka abubuwan da aka rubuta su cika.
For these are days of vengeance, to fulfill all that is written.
23 Kaiton wadanda suke da juna biyu da masu ba da mama a wannan kwanakin! Gama za a sha kunci mai girma a kasan, da fushi kuma zuwa ga mutanen nan.
But woe to them that are with child, and to them that nurse children, in those days; for then will be great distress in the land, and wrath upon this people.
24 Za su fadi ta kaifin takobi kuma za a kai su cikin bauta ga dukan kasashe, al'ummai za su tattake Urushalima, har ya zuwa lokacin al'ummai ya cika.
And they will fall by the edge of the sword, and be carried captive to every place. And Jerusalem will be trodden down by the Gentiles, until the times of the Gentiles shall be completed.
25 Za a ga alamomi cikin rana da wata da kuma taurari. A duniya kuma, al'ummai za su sha kunci, za su rude saboda rurin teku da rakuman ruwa.
And there will be signs in the sun, and in the moon, and in the stars; and distress of nations on the earth; and clasping of hands, from astonishment at the noise of the sea;
26 Mutane za su suma da tsoro da kuma da tunanin abubuwa da za su abko wa duniya. Gama za a girgiza ikokin sammai.
and dismay that driveth out the souls of men, from fear of that which is to come on the earth; and the powers of heaven will be moved.
27 Sa'annan za su ga Dan Mutum yana zuwa a cikin gajimarai da iko da daukaka mai girma.
And then will they see the Son of man coming in the clouds, with much power, and with great glory.
28 Amma sa'adda wadannan abubuwa suka fara faruwa, tashi saye, sai ku daga kanku sama, saboda ceton ku ya kusato.”
And when these things shall begin to be, take courage, and lift up your heads, for your deliverance draweth nigh.
29 Yesu ya bada misali, “Duba itacen baure, da duka itatuwa.
And he uttered a similitude to them. Look at the fig-tree, and all the trees.
30 Sa'adda su ke fitar da ganye, za ku gani da kanku cewa bazara ta yi kusa kuma.
When they bud forth, ye at once understand from them that summer approacheth.
31 Haka kuma, sa'adda ku ka ga wadannan abubuwa suna faruwa, ku sani cewa mulkin Allah ya yi kusa.
So also, when ye shall see all these things take place, know ye that the kingdom of God is near.
32 Gaskiya, na ke gaya maku, wannan zamani ba za ya shude ba, sai duka abubuwan nan sun faru.
Verily I say to you, That this generation will not pass away, until all these things occur.
33 Sama da kasa za su shude, amma maganata ba za ta shude ba.
Heaven and earth will pass away; but my word will not pass away.
34 Amma ku lura da kanku, domin kada ku nawaita zuciyarku da tararradin duniya da shayeshaye da damuwa ta rayuwa. Gama ranar za ta zo babu shiri
Take heed to yourselves, that your hearts be, at no time, stupefied by gluttony and ebriety and worldly care; and so that day come upon you unawares.
35 kamar tarko. Gama zai zo akan kowa da ke rayuwa a fuskar dukan duniya.
For, like a hunter's snare, it will spring upon all them that dwell upon the face of the whole land.
36 Amma ku zama a fadake kowanne lokaci, kuna addu'a domin ku iya samun karfin tserewa dukan wadannan abubuwa da za su faru, da kuma yadda za ku tsaya a gaban Dan Mutum.”
Be ye therefore vigilant, at all times, and prayerful; that ye may be worthy to escape the things that are to take place, and may stand before the Son of man.
37 Da rana yana koyarwa a cikin haikali, dukan dare kuma yakan tafi dutsen da a ke kira zaitun.
And, in the daytime he taught in the temple, and at night he went out and lodged in the mount, called the Place of Olives.
38 Dukan mutane suka rika zuwa wurinsa da sassafe domin su ji shi a haikali.
And all the people came early to him in the temple, to hear his discourse.

< Luka 21 >