< Luka 21 >

1 Yesu ya tada ido sai ya ga mutane masu arziki wadanda suke saka baikonsu a cikin ma'aji.
Jeshu looked at those rich (persons) who were throwing into the house of treasure their oblations.
2 Ya ga wata gwauruwa matalauciya tana saka anini biyu a ciki.
And he saw also a certain poor widow who threw in two shomonee.
3 Sai ya ce, “Gaskiya ina gaya maku, wannan matalauciyar gwauruwa ta saka fiye da dukansu.
And he said, Truth I say to you, That this poor widow hath thrown in more than every one:
4 Duka wadannan sun bayar da baikonsu daga cikin yalwarsu. Amma wannan gwauruwan, daga cikin talaucin ta, ta saka dukan iyakar kudinta na zaman gari da take da shi.”
for all those from what abounded to them have thrown into the house of the oblation of Aloha: but this from her penury all that she possessed hath she thrown in.
5 Kamar yadda wadansu suke maganan haikali, yadda aka yi masa ado da duwatsu masu daraja da bayebaye, ya ce,
AND as some spake of the temple, (with) what beautiful stones and gifts it was adorned, Jeshu said to them,
6 “Game da wadannan abubuwa da ku ke gani, rana tana zuwa da ba dutse ko daya da zai zauna kan dan'uwansa da ba za a rushe kasa ba.”
These that you see, the days shall come (when) of them there will not be found a stone upon a stone that shall not be destroyed.
7 Sai suka yi masa tambaya, cewa, “Malam, yaushe ne wadannan abubuwan zasu faru? Menene kuma zai zama alama sa'adda wadannan abubuwa suna shirin faruwa?”
And they inquired of him, and said, Malphona, when shall these be? and what is the sign that these are nigh to be?
8 Yesu ya amsa, “Ku yi hankali kada a rude ku. Gama dayawa zasu zo a cikin sunana, suna cewa, 'Ni ne shi,' kuma, 'Lokaci ya yi kusa.' Kada ku bi su.
But he said to them, Beware lest you be seduced: for many will come in my name, and will say, I am the Meshicha; and the time hath drawn nigh: but go not you after them.
9 Sa'adda ku ka ji game da yakoki da hargitsi, kada ku firgita, dole ne wadannan abubuwa su faru tukuna, amma karshe ba zai faru nan da nan ba.”
And when you hear of wars and commotions, fear not: for these are first to be; but not yet cometh the end.
10 Sa'annan ya ce masu, “Al'umma za ta tasar ma al'umma, mulki kuma za ya tasar wa mulki.
For nation shall rise up against nation, and kingdom against kingdom:
11 Za a yi babbar girgizan kasa, a wurare dabam dabam kuma za a yi yunwa da annoba. Za a yi al'amura masu ban tsoro da manyan alamu daga sama.
and great earthquakes will be in divers places, and famines, and plagues; and there will be portents, and terrors, and great signs from the heavens will appear, and great tempests shall there be.
12 Amma kafin abubuwan nan duka, za su kama ku, su kuma tsananta maku, suna mika ku ga majami'u da kuma gidajen kurkuku, za su kawo ku gaban sarakuna da gwamnoni saboda sunana.
But before all these, they will lay hands upon you, and persecute you, and deliver you up to the synagogues, and to the house of the bound. And they will bring you before kings and governors on account of my name.
13 Zai zamar maku zarafin shaida.
And it shall be to you for a testimony.
14 Saboda haka ku kudurta a ranku kada ku shirya yadda za ku amsa,
But lay it up in your hearts that you may not be learned for the answer;
15 gama ni zan ba ku kalmomi da hikima, wadda dukan makiyanku ba za su yi tsayayya ko su karyata ku ba.
for I will give you a mouth and wisdom which all your adversaries cannot stand against.
16 Amma har da mahaifa da 'yan'uwa da dangi da abokai za su bashe ku, su kuma kashe wadansun ku.
But your fathers, and your brethren, and your kinsfolk, and your friends will betray you, and some of you they shall put to death.
17 Kowa zai ki ku saboda sunana.
And you will be hated of all men on account of my name:
18 Amma ba ko gashin kanku da zai hallaka.
yet a hair of your head shall not perish,
19 A cikin hankurin ku za ku ribato rayukanku.
but in your perseverance you shall possess your souls.
20 Sa'adda ku ka ga Urushalima tana kewaye da sojoji, sai ku sani da cewa faduwarta ta yi kusa.
But when you see Urishlem encompassed by an army, then know that its destruction hath drawn nigh.
21 Sai wadanda su ke Yahudiya su gudu zuwa kan tuddai, wadanda suke tsakiyar gari kuma su tafi, kada su bar wadanda suke kauyuka su shigo ciki.
Then let them who are in Jihud escape to the mountain, and they who are within her escape, and let not them who are in the country places enter into her.
22 Gama wadannan ranakun ramako ne, saboda duka abubuwan da aka rubuta su cika.
For those (will be) the days of retribution, that all which is written may be fulfilled.
23 Kaiton wadanda suke da juna biyu da masu ba da mama a wannan kwanakin! Gama za a sha kunci mai girma a kasan, da fushi kuma zuwa ga mutanen nan.
But woe to those who are with child and to those who suckle in those days! for there will be great distress in the land, and wrath upon this people.
24 Za su fadi ta kaifin takobi kuma za a kai su cikin bauta ga dukan kasashe, al'ummai za su tattake Urushalima, har ya zuwa lokacin al'ummai ya cika.
And they shall fall by the edge of the sword, and be led captive into every place, and Urishlem shall be trodden down of the Gentiles, until shall be fulfilled the times of the Gentiles.
25 Za a ga alamomi cikin rana da wata da kuma taurari. A duniya kuma, al'ummai za su sha kunci, za su rude saboda rurin teku da rakuman ruwa.
And there will be signs in the sun, and in the moon, and in the stars, and on earth distress of nations, and smiting of hands from astonishment at the voice of the sea,
26 Mutane za su suma da tsoro da kuma da tunanin abubuwa da za su abko wa duniya. Gama za a girgiza ikokin sammai.
the commotion hurrying forth the souls of the sons of men from fear of what is about to come upon the earth; and the powers of the heavens shall be commoved.
27 Sa'annan za su ga Dan Mutum yana zuwa a cikin gajimarai da iko da daukaka mai girma.
And then shall they see the Son of man coming in the clouds, with power and great glory.
28 Amma sa'adda wadannan abubuwa suka fara faruwa, tashi saye, sai ku daga kanku sama, saboda ceton ku ya kusato.”
But when these things begin to be, take courage, and lift up your heads, because your redemption hath drawn nigh.
29 Yesu ya bada misali, “Duba itacen baure, da duka itatuwa.
AND he spake to them a parable, Behold the fig-tree and all the trees;
30 Sa'adda su ke fitar da ganye, za ku gani da kanku cewa bazara ta yi kusa kuma.
when they bud forth, immediately from them you know that summer hath drawn nigh.
31 Haka kuma, sa'adda ku ka ga wadannan abubuwa suna faruwa, ku sani cewa mulkin Allah ya yi kusa.
Thus also you, when you see that these are, know that nigh is the kingdom of Aloha.
32 Gaskiya, na ke gaya maku, wannan zamani ba za ya shude ba, sai duka abubuwan nan sun faru.
Amen I say to you, That this race shall not pass away till all these things shall be.
33 Sama da kasa za su shude, amma maganata ba za ta shude ba.
Heaven and earth shall pass away, but my words shall not pass away.
34 Amma ku lura da kanku, domin kada ku nawaita zuciyarku da tararradin duniya da shayeshaye da damuwa ta rayuwa. Gama ranar za ta zo babu shiri
But take heed to yourselves, that at any time your hearts be not heavy with excess and drunkenness, and the care of the world, and unawares shall come upon you that day.
35 kamar tarko. Gama zai zo akan kowa da ke rayuwa a fuskar dukan duniya.
For as a net it will overtake all them who dwell upon the faces of the whole earth.
36 Amma ku zama a fadake kowanne lokaci, kuna addu'a domin ku iya samun karfin tserewa dukan wadannan abubuwa da za su faru, da kuma yadda za ku tsaya a gaban Dan Mutum.”
Be therefore wakeful at all time, and pray that you may be worthy to escape from those things that are about to be, and that you may stand before the Son of man.
37 Da rana yana koyarwa a cikin haikali, dukan dare kuma yakan tafi dutsen da a ke kira zaitun.
So in the day (time) he taught in the temple, and at night he went forth and lodged in the mount which is called the Place of Olives.
38 Dukan mutane suka rika zuwa wurinsa da sassafe domin su ji shi a haikali.
And all the people were early with him at the temple to hear his word.

< Luka 21 >