< Luka 21 >

1 Yesu ya tada ido sai ya ga mutane masu arziki wadanda suke saka baikonsu a cikin ma'aji.
And he looked up, and saw the rich men that were casting their gifts into the treasury.
2 Ya ga wata gwauruwa matalauciya tana saka anini biyu a ciki.
And he saw a certain poor widow casting in thither two mites.
3 Sai ya ce, “Gaskiya ina gaya maku, wannan matalauciyar gwauruwa ta saka fiye da dukansu.
And he said, Of a truth I say unto you, This poor widow cast in more than they all:
4 Duka wadannan sun bayar da baikonsu daga cikin yalwarsu. Amma wannan gwauruwan, daga cikin talaucin ta, ta saka dukan iyakar kudinta na zaman gari da take da shi.”
for all these did of their superfluity cast in unto the gifts: but she of her want did cast in all the living that she had.
5 Kamar yadda wadansu suke maganan haikali, yadda aka yi masa ado da duwatsu masu daraja da bayebaye, ya ce,
And as some spake of the temple, how it was adorned with goodly stones and offerings, he said,
6 “Game da wadannan abubuwa da ku ke gani, rana tana zuwa da ba dutse ko daya da zai zauna kan dan'uwansa da ba za a rushe kasa ba.”
As for these things which ye behold, the days will come, in which there shall not be left here one stone upon another, that shall not be thrown down.
7 Sai suka yi masa tambaya, cewa, “Malam, yaushe ne wadannan abubuwan zasu faru? Menene kuma zai zama alama sa'adda wadannan abubuwa suna shirin faruwa?”
And they asked him, saying, Master, when therefore shall these things be? and what [shall be] the sign when these things are about to come to pass?
8 Yesu ya amsa, “Ku yi hankali kada a rude ku. Gama dayawa zasu zo a cikin sunana, suna cewa, 'Ni ne shi,' kuma, 'Lokaci ya yi kusa.' Kada ku bi su.
And he said, Take heed that ye be not led astray: for many shall come in my name, saying, I am [he]; and, The time is at hand: go ye not after them.
9 Sa'adda ku ka ji game da yakoki da hargitsi, kada ku firgita, dole ne wadannan abubuwa su faru tukuna, amma karshe ba zai faru nan da nan ba.”
And when ye shall hear of wars and tumults, be not terrified: for these things must needs come to pass first; but the end is not immediately.
10 Sa'annan ya ce masu, “Al'umma za ta tasar ma al'umma, mulki kuma za ya tasar wa mulki.
Then said he unto them, Nation shall rise against nation, and kingdom against kingdom:
11 Za a yi babbar girgizan kasa, a wurare dabam dabam kuma za a yi yunwa da annoba. Za a yi al'amura masu ban tsoro da manyan alamu daga sama.
and there shall be great earthquakes, and in divers places famines and pestilences; and there shall be terrors and great signs from heaven.
12 Amma kafin abubuwan nan duka, za su kama ku, su kuma tsananta maku, suna mika ku ga majami'u da kuma gidajen kurkuku, za su kawo ku gaban sarakuna da gwamnoni saboda sunana.
But before all these things, they shall lay their hands on you, and shall persecute you, delivering you up to the synagogues and prisons, bringing you before kings and governors for my name’s sake.
13 Zai zamar maku zarafin shaida.
It shall turn unto you for a testimony.
14 Saboda haka ku kudurta a ranku kada ku shirya yadda za ku amsa,
Settle it therefore in your hearts, not to meditate beforehand how to answer:
15 gama ni zan ba ku kalmomi da hikima, wadda dukan makiyanku ba za su yi tsayayya ko su karyata ku ba.
for I will give you a mouth and wisdom, which all your adversaries shall not be able to withstand or to gainsay.
16 Amma har da mahaifa da 'yan'uwa da dangi da abokai za su bashe ku, su kuma kashe wadansun ku.
But ye shall be delivered up even by parents, and brethren, and kinsfolk, and friends; and [some] of you shall they cause to be put to death.
17 Kowa zai ki ku saboda sunana.
And ye shall be hated of all men for my name’s sake.
18 Amma ba ko gashin kanku da zai hallaka.
And not a hair of your head shall perish.
19 A cikin hankurin ku za ku ribato rayukanku.
In your patience ye shall win your souls.
20 Sa'adda ku ka ga Urushalima tana kewaye da sojoji, sai ku sani da cewa faduwarta ta yi kusa.
But when ye see Jerusalem compassed with armies, then know that her desolation is at hand.
21 Sai wadanda su ke Yahudiya su gudu zuwa kan tuddai, wadanda suke tsakiyar gari kuma su tafi, kada su bar wadanda suke kauyuka su shigo ciki.
Then let them that are in Judaea flee unto the mountains; and let them that are in the midst of her depart out; and let not them that are in the country enter therein.
22 Gama wadannan ranakun ramako ne, saboda duka abubuwan da aka rubuta su cika.
For these are days of vengeance, that all things which are written may be fulfilled.
23 Kaiton wadanda suke da juna biyu da masu ba da mama a wannan kwanakin! Gama za a sha kunci mai girma a kasan, da fushi kuma zuwa ga mutanen nan.
Woe unto them that are with child and to them that give suck in those days! for there shall be great distress upon the land, and wrath unto this people.
24 Za su fadi ta kaifin takobi kuma za a kai su cikin bauta ga dukan kasashe, al'ummai za su tattake Urushalima, har ya zuwa lokacin al'ummai ya cika.
And they shall fall by the edge of the sword, and shall be led captive into all the nations: and Jerusalem shall be trodden down of the Gentiles, until the times of the Gentiles be fulfilled.
25 Za a ga alamomi cikin rana da wata da kuma taurari. A duniya kuma, al'ummai za su sha kunci, za su rude saboda rurin teku da rakuman ruwa.
And there shall be signs in sun and moon and stars; and upon the earth distress of nations, in perplexity for the roaring of the sea and the billows;
26 Mutane za su suma da tsoro da kuma da tunanin abubuwa da za su abko wa duniya. Gama za a girgiza ikokin sammai.
men fainting for fear, and for expectation of the things which are coming on the world: for the powers of the heavens shall be shaken.
27 Sa'annan za su ga Dan Mutum yana zuwa a cikin gajimarai da iko da daukaka mai girma.
And then shall they see the Son of man coming in a cloud with power and great glory.
28 Amma sa'adda wadannan abubuwa suka fara faruwa, tashi saye, sai ku daga kanku sama, saboda ceton ku ya kusato.”
But when these things begin to come to pass, look up, and lift up your heads; because your redemption draweth nigh.
29 Yesu ya bada misali, “Duba itacen baure, da duka itatuwa.
And he spake to them a parable: Behold the fig tree, and all the trees:
30 Sa'adda su ke fitar da ganye, za ku gani da kanku cewa bazara ta yi kusa kuma.
when they now shoot forth, ye see it and know of your own selves that the summer is now nigh.
31 Haka kuma, sa'adda ku ka ga wadannan abubuwa suna faruwa, ku sani cewa mulkin Allah ya yi kusa.
Even so ye also, when ye see these things coming to pass, know ye that the kingdom of God is nigh.
32 Gaskiya, na ke gaya maku, wannan zamani ba za ya shude ba, sai duka abubuwan nan sun faru.
Verily I say unto you, This generation shall not pass away, till all things be accomplished.
33 Sama da kasa za su shude, amma maganata ba za ta shude ba.
Heaven and earth shall pass away: but my words shall not pass away.
34 Amma ku lura da kanku, domin kada ku nawaita zuciyarku da tararradin duniya da shayeshaye da damuwa ta rayuwa. Gama ranar za ta zo babu shiri
But take heed to yourselves, lest haply your hearts be overcharged with surfeiting, and drunkenness, and cares of this life, and that day come on you suddenly as a snare:
35 kamar tarko. Gama zai zo akan kowa da ke rayuwa a fuskar dukan duniya.
for [so] shall it come upon all them that dwell on the face of all the earth.
36 Amma ku zama a fadake kowanne lokaci, kuna addu'a domin ku iya samun karfin tserewa dukan wadannan abubuwa da za su faru, da kuma yadda za ku tsaya a gaban Dan Mutum.”
But watch ye at every season, making supplication, that ye may prevail to escape all these things that shall come to pass, and to stand before the Son of man.
37 Da rana yana koyarwa a cikin haikali, dukan dare kuma yakan tafi dutsen da a ke kira zaitun.
And every day he was teaching in the temple; and every night he went out, and lodged in the mount that is called [the mount] of Olives.
38 Dukan mutane suka rika zuwa wurinsa da sassafe domin su ji shi a haikali.
And all the people came early in the morning to him in the temple, to hear him.

< Luka 21 >