< Luka 21 >

1 Yesu ya tada ido sai ya ga mutane masu arziki wadanda suke saka baikonsu a cikin ma'aji.
He looked up, and saw the rich people who were putting their gifts into the treasury.
2 Ya ga wata gwauruwa matalauciya tana saka anini biyu a ciki.
He saw a certain poor widow casting in two lepta.
3 Sai ya ce, “Gaskiya ina gaya maku, wannan matalauciyar gwauruwa ta saka fiye da dukansu.
He said, "Truly I tell you, this poor widow put in more than all of them,
4 Duka wadannan sun bayar da baikonsu daga cikin yalwarsu. Amma wannan gwauruwan, daga cikin talaucin ta, ta saka dukan iyakar kudinta na zaman gari da take da shi.”
for all these put in gifts from their abundance, but she, out of her poverty, put in all that she had to live on."
5 Kamar yadda wadansu suke maganan haikali, yadda aka yi masa ado da duwatsu masu daraja da bayebaye, ya ce,
As some were talking about the temple and how it was decorated with beautiful stones and gifts, he said,
6 “Game da wadannan abubuwa da ku ke gani, rana tana zuwa da ba dutse ko daya da zai zauna kan dan'uwansa da ba za a rushe kasa ba.”
"As for these things which you see, the days will come, in which there will not be left here one stone on another that will not be thrown down."
7 Sai suka yi masa tambaya, cewa, “Malam, yaushe ne wadannan abubuwan zasu faru? Menene kuma zai zama alama sa'adda wadannan abubuwa suna shirin faruwa?”
They asked him, "Teacher, so when will these things be? What is the sign that these things are about to happen?"
8 Yesu ya amsa, “Ku yi hankali kada a rude ku. Gama dayawa zasu zo a cikin sunana, suna cewa, 'Ni ne shi,' kuma, 'Lokaci ya yi kusa.' Kada ku bi su.
He said, "Watch out that you do not get led astray, for many will come in my name, saying, 'I am he,' and, 'The time is near.' Therefore do not follow them.
9 Sa'adda ku ka ji game da yakoki da hargitsi, kada ku firgita, dole ne wadannan abubuwa su faru tukuna, amma karshe ba zai faru nan da nan ba.”
When you hear of wars and disturbances, do not be terrified, for these things must happen first, but the end won't come immediately."
10 Sa'annan ya ce masu, “Al'umma za ta tasar ma al'umma, mulki kuma za ya tasar wa mulki.
Then he said to them, "Nation will rise against nation, and kingdom against kingdom.
11 Za a yi babbar girgizan kasa, a wurare dabam dabam kuma za a yi yunwa da annoba. Za a yi al'amura masu ban tsoro da manyan alamu daga sama.
There will be great earthquakes, famines, and plagues in various places. There will be terrors and great signs from heaven.
12 Amma kafin abubuwan nan duka, za su kama ku, su kuma tsananta maku, suna mika ku ga majami'u da kuma gidajen kurkuku, za su kawo ku gaban sarakuna da gwamnoni saboda sunana.
But before all these things, they will lay their hands on you and will persecute you, delivering you up to synagogues and prisons, bringing you before kings and governors for my name's sake.
13 Zai zamar maku zarafin shaida.
It will turn out as a testimony for you.
14 Saboda haka ku kudurta a ranku kada ku shirya yadda za ku amsa,
Settle it therefore in your hearts not to meditate beforehand how to answer,
15 gama ni zan ba ku kalmomi da hikima, wadda dukan makiyanku ba za su yi tsayayya ko su karyata ku ba.
for I will give you a mouth and wisdom which all your adversaries will not be able to withstand or to contradict.
16 Amma har da mahaifa da 'yan'uwa da dangi da abokai za su bashe ku, su kuma kashe wadansun ku.
You will be handed over even by parents, brothers, relatives, and friends. They will cause some of you to be put to death.
17 Kowa zai ki ku saboda sunana.
And you will be hated by everyone because of my name.
18 Amma ba ko gashin kanku da zai hallaka.
But not a hair of your head will perish.
19 A cikin hankurin ku za ku ribato rayukanku.
"By your endurance you will win your lives.
20 Sa'adda ku ka ga Urushalima tana kewaye da sojoji, sai ku sani da cewa faduwarta ta yi kusa.
"But when you see Jerusalem surrounded by armies, then know that its desolation is near.
21 Sai wadanda su ke Yahudiya su gudu zuwa kan tuddai, wadanda suke tsakiyar gari kuma su tafi, kada su bar wadanda suke kauyuka su shigo ciki.
Then let those who are in Judea flee to the mountains. Let those who are in the midst of her depart. Let those who are in the country not enter it.
22 Gama wadannan ranakun ramako ne, saboda duka abubuwan da aka rubuta su cika.
For these are days of vengeance, that all things which are written may be fulfilled.
23 Kaiton wadanda suke da juna biyu da masu ba da mama a wannan kwanakin! Gama za a sha kunci mai girma a kasan, da fushi kuma zuwa ga mutanen nan.
Woe to those who are pregnant and to those who nurse infants in those days. For there will be great distress in the land, and wrath to this people.
24 Za su fadi ta kaifin takobi kuma za a kai su cikin bauta ga dukan kasashe, al'ummai za su tattake Urushalima, har ya zuwa lokacin al'ummai ya cika.
And they will fall by the edge of the sword and be led captive into all the nations. And Jerusalem will be trampled down by non-Jewish people until the times are fulfilled. And there will be times of the non-Jewish people.
25 Za a ga alamomi cikin rana da wata da kuma taurari. A duniya kuma, al'ummai za su sha kunci, za su rude saboda rurin teku da rakuman ruwa.
And there will be signs in the sun, and moon, and stars, and on the earth distress of nations in perplexity because of the roaring of the sea and the waves;
26 Mutane za su suma da tsoro da kuma da tunanin abubuwa da za su abko wa duniya. Gama za a girgiza ikokin sammai.
people will be fainting from fear, and from expectation of the things which are coming on the world, for the powers of the heavens will be shaken.
27 Sa'annan za su ga Dan Mutum yana zuwa a cikin gajimarai da iko da daukaka mai girma.
Then they will see the Son of Man coming in a cloud with power and great glory.
28 Amma sa'adda wadannan abubuwa suka fara faruwa, tashi saye, sai ku daga kanku sama, saboda ceton ku ya kusato.”
But when these things begin to happen, look up, and lift up your heads, because your redemption is near."
29 Yesu ya bada misali, “Duba itacen baure, da duka itatuwa.
He told them a parable. "See the fig tree, and all the trees.
30 Sa'adda su ke fitar da ganye, za ku gani da kanku cewa bazara ta yi kusa kuma.
When they are already budding, you see it and know by your own selves that the summer is already near.
31 Haka kuma, sa'adda ku ka ga wadannan abubuwa suna faruwa, ku sani cewa mulkin Allah ya yi kusa.
Even so you also, when you see these things happening, know that the Kingdom of God is near.
32 Gaskiya, na ke gaya maku, wannan zamani ba za ya shude ba, sai duka abubuwan nan sun faru.
Truly I tell you, this generation will not pass away until all things are accomplished.
33 Sama da kasa za su shude, amma maganata ba za ta shude ba.
Heaven and earth will pass away, but my words will by no means pass away.
34 Amma ku lura da kanku, domin kada ku nawaita zuciyarku da tararradin duniya da shayeshaye da damuwa ta rayuwa. Gama ranar za ta zo babu shiri
"So be careful, or your hearts will be loaded down with carousing, drunkenness, and cares of this life, and that day will come on you suddenly.
35 kamar tarko. Gama zai zo akan kowa da ke rayuwa a fuskar dukan duniya.
For it will come like a snare on all those who dwell on the surface of all the earth.
36 Amma ku zama a fadake kowanne lokaci, kuna addu'a domin ku iya samun karfin tserewa dukan wadannan abubuwa da za su faru, da kuma yadda za ku tsaya a gaban Dan Mutum.”
Therefore be watchful all the time, praying that you may be able to escape all these things that will happen, and to stand before the Son of Man."
37 Da rana yana koyarwa a cikin haikali, dukan dare kuma yakan tafi dutsen da a ke kira zaitun.
Every day Jesus was teaching in the temple, and every night he would go out and spend the night on the mountain that is called Olivet.
38 Dukan mutane suka rika zuwa wurinsa da sassafe domin su ji shi a haikali.
All the people came early in the morning to him in the temple to hear him.

< Luka 21 >