< Luka 21 >

1 Yesu ya tada ido sai ya ga mutane masu arziki wadanda suke saka baikonsu a cikin ma'aji.
Looking up He saw the rich putting their gifts into the treasure chest.
2 Ya ga wata gwauruwa matalauciya tana saka anini biyu a ciki.
But He also saw a certain poor widow putting in two mites.
3 Sai ya ce, “Gaskiya ina gaya maku, wannan matalauciyar gwauruwa ta saka fiye da dukansu.
So He said: “I tell you truly that this poor widow put in more than all of them;
4 Duka wadannan sun bayar da baikonsu daga cikin yalwarsu. Amma wannan gwauruwan, daga cikin talaucin ta, ta saka dukan iyakar kudinta na zaman gari da take da shi.”
because all these others put in gifts for God out of their abundance, but she, out of her destitution, put in all she had to live on.”
5 Kamar yadda wadansu suke maganan haikali, yadda aka yi masa ado da duwatsu masu daraja da bayebaye, ya ce,
Then, as some were admiring the temple, how it was adorned with beautiful stones and donations, He said,
6 “Game da wadannan abubuwa da ku ke gani, rana tana zuwa da ba dutse ko daya da zai zauna kan dan'uwansa da ba za a rushe kasa ba.”
“These things that you see—the days will come in which not one stone will be left upon another that will not be thrown down.”
7 Sai suka yi masa tambaya, cewa, “Malam, yaushe ne wadannan abubuwan zasu faru? Menene kuma zai zama alama sa'adda wadannan abubuwa suna shirin faruwa?”
So they asked Him, saying: “Teacher, so when will these things be?” and “What will be the sign when these things are about to happen?”
8 Yesu ya amsa, “Ku yi hankali kada a rude ku. Gama dayawa zasu zo a cikin sunana, suna cewa, 'Ni ne shi,' kuma, 'Lokaci ya yi kusa.' Kada ku bi su.
So He said: “Be careful, so as not to be deceived, because many will come in my name saying: ‘I am’ and ‘The time is at hand.’ Therefore do not go after them.
9 Sa'adda ku ka ji game da yakoki da hargitsi, kada ku firgita, dole ne wadannan abubuwa su faru tukuna, amma karshe ba zai faru nan da nan ba.”
But whenever you hear of wars and insurrections, do not be terrified; because these things must happen first, but the end will not come right away.”
10 Sa'annan ya ce masu, “Al'umma za ta tasar ma al'umma, mulki kuma za ya tasar wa mulki.
Then He said to them: “Nation will be raised up against nation, and kingdom against kingdom.
11 Za a yi babbar girgizan kasa, a wurare dabam dabam kuma za a yi yunwa da annoba. Za a yi al'amura masu ban tsoro da manyan alamu daga sama.
And there will be severe earthquakes in various places, and famines and pestilences; and there will be fearful events and great signs from heaven.
12 Amma kafin abubuwan nan duka, za su kama ku, su kuma tsananta maku, suna mika ku ga majami'u da kuma gidajen kurkuku, za su kawo ku gaban sarakuna da gwamnoni saboda sunana.
But before all these things, they will lay their hands on you and persecute you, delivering you up to synagogues and prisons, bringing you before kings and governors on account of my name.
13 Zai zamar maku zarafin shaida.
But it will turn out for you as an occasion for testimony.
14 Saboda haka ku kudurta a ranku kada ku shirya yadda za ku amsa,
So settle it in your hearts not to practice giving a defense beforehand;
15 gama ni zan ba ku kalmomi da hikima, wadda dukan makiyanku ba za su yi tsayayya ko su karyata ku ba.
because I will give you a mouth and wisdom such that all your adversaries will not be able to contradict or withstand.
16 Amma har da mahaifa da 'yan'uwa da dangi da abokai za su bashe ku, su kuma kashe wadansun ku.
You will be betrayed even by parents and relatives, friends and ‘brothers’; and they will put some of you to death.
17 Kowa zai ki ku saboda sunana.
And you will be hated by all because of my name.
18 Amma ba ko gashin kanku da zai hallaka.
(Not even one hair of your head will be wasted
19 A cikin hankurin ku za ku ribato rayukanku.
—you must secure your souls by your endurance.)
20 Sa'adda ku ka ga Urushalima tana kewaye da sojoji, sai ku sani da cewa faduwarta ta yi kusa.
“But when you see Jerusalem surrounded by armies, then know that her desolation is at hand.
21 Sai wadanda su ke Yahudiya su gudu zuwa kan tuddai, wadanda suke tsakiyar gari kuma su tafi, kada su bar wadanda suke kauyuka su shigo ciki.
Then let those who are in Judea flee to the mountains; let those who are in the city get out, and let those who are in the country not enter her.
22 Gama wadannan ranakun ramako ne, saboda duka abubuwan da aka rubuta su cika.
Because these are days of vengeance, that all the written things may be fulfilled.
23 Kaiton wadanda suke da juna biyu da masu ba da mama a wannan kwanakin! Gama za a sha kunci mai girma a kasan, da fushi kuma zuwa ga mutanen nan.
But woe to those who are pregnant and to those nursing babies in those days! There will be great distress in the land, and wrath to this people.
24 Za su fadi ta kaifin takobi kuma za a kai su cikin bauta ga dukan kasashe, al'ummai za su tattake Urushalima, har ya zuwa lokacin al'ummai ya cika.
Yes, they will fall by the edge of the sword, and be led away captive into all nations. And Jerusalem will be trampled by Gentiles, until the times of the Gentiles are fulfilled.
25 Za a ga alamomi cikin rana da wata da kuma taurari. A duniya kuma, al'ummai za su sha kunci, za su rude saboda rurin teku da rakuman ruwa.
“There will be signs in sun, moon, and stars; and on the earth distress of nations, with perplexity, at the roaring and tossing of the sea;
26 Mutane za su suma da tsoro da kuma da tunanin abubuwa da za su abko wa duniya. Gama za a girgiza ikokin sammai.
men fainting from fear and expectation of the things coming on the inhabited earth—because the powers of the heavens will be shaken.
27 Sa'annan za su ga Dan Mutum yana zuwa a cikin gajimarai da iko da daukaka mai girma.
Then they will see the Son of the Man coming in a cloud with power and great glory.
28 Amma sa'adda wadannan abubuwa suka fara faruwa, tashi saye, sai ku daga kanku sama, saboda ceton ku ya kusato.”
Now when these things begin to happen, straighten up and lift up your heads, because your redemption is drawing near.”
29 Yesu ya bada misali, “Duba itacen baure, da duka itatuwa.
Then He told them a parable: “Look at the fig tree and all the trees.
30 Sa'adda su ke fitar da ganye, za ku gani da kanku cewa bazara ta yi kusa kuma.
Whenever they are already budding, you see and know by yourselves that summer is now near.
31 Haka kuma, sa'adda ku ka ga wadannan abubuwa suna faruwa, ku sani cewa mulkin Allah ya yi kusa.
So you also, whenever you see these things happening, know that the Kingdom of God is near.
32 Gaskiya, na ke gaya maku, wannan zamani ba za ya shude ba, sai duka abubuwan nan sun faru.
I tell you assuredly, this generation will certainly not pass away until all has happened.
33 Sama da kasa za su shude, amma maganata ba za ta shude ba.
Heaven and earth will pass away, but my words will by no means pass away.
34 Amma ku lura da kanku, domin kada ku nawaita zuciyarku da tararradin duniya da shayeshaye da damuwa ta rayuwa. Gama ranar za ta zo babu shiri
“But keep a watch on yourselves, lest your hearts be weighed down with dissipation, drunkenness, and cares of life, and that Day come upon you suddenly.
35 kamar tarko. Gama zai zo akan kowa da ke rayuwa a fuskar dukan duniya.
Because it will come like a trap upon all those who dwell on the surface of the whole earth.
36 Amma ku zama a fadake kowanne lokaci, kuna addu'a domin ku iya samun karfin tserewa dukan wadannan abubuwa da za su faru, da kuma yadda za ku tsaya a gaban Dan Mutum.”
So be watchful all the time, praying that you may be counted worthy to escape all these things that are about to happen and to stand before the Son of the Man.”
37 Da rana yana koyarwa a cikin haikali, dukan dare kuma yakan tafi dutsen da a ke kira zaitun.
In the daytime He was teaching in the temple, but at night He went out and stayed on the mountain called ‘of Olives.’
38 Dukan mutane suka rika zuwa wurinsa da sassafe domin su ji shi a haikali.
Then early in the morning all the people would come to Him in the temple to hear Him.

< Luka 21 >