< Luka 21 >

1 Yesu ya tada ido sai ya ga mutane masu arziki wadanda suke saka baikonsu a cikin ma'aji.
And looking up, he saw the men of wealth putting their offerings in the money-box.
2 Ya ga wata gwauruwa matalauciya tana saka anini biyu a ciki.
And he saw a certain poor widow putting in a farthing.
3 Sai ya ce, “Gaskiya ina gaya maku, wannan matalauciyar gwauruwa ta saka fiye da dukansu.
And he said, Truly I say to you, This poor widow has given more than all of them:
4 Duka wadannan sun bayar da baikonsu daga cikin yalwarsu. Amma wannan gwauruwan, daga cikin talaucin ta, ta saka dukan iyakar kudinta na zaman gari da take da shi.”
For they gave out of their wealth, having more than enough for themselves: but she, even out of her need, has put in all her living.
5 Kamar yadda wadansu suke maganan haikali, yadda aka yi masa ado da duwatsu masu daraja da bayebaye, ya ce,
And some were talking about the Temple, how it was made fair with beautiful stones and with offerings, but he said,
6 “Game da wadannan abubuwa da ku ke gani, rana tana zuwa da ba dutse ko daya da zai zauna kan dan'uwansa da ba za a rushe kasa ba.”
As for these things which you see, the days will come when not one stone will be resting on another, but all will be broken down.
7 Sai suka yi masa tambaya, cewa, “Malam, yaushe ne wadannan abubuwan zasu faru? Menene kuma zai zama alama sa'adda wadannan abubuwa suna shirin faruwa?”
And they said to him, Master, when will these things be? and what sign will there be when these events are to take place?
8 Yesu ya amsa, “Ku yi hankali kada a rude ku. Gama dayawa zasu zo a cikin sunana, suna cewa, 'Ni ne shi,' kuma, 'Lokaci ya yi kusa.' Kada ku bi su.
And he said, Take care that you are not tricked: for a number of people will come in my name, saying, I am he; and, The time is near: do not go after them.
9 Sa'adda ku ka ji game da yakoki da hargitsi, kada ku firgita, dole ne wadannan abubuwa su faru tukuna, amma karshe ba zai faru nan da nan ba.”
And when news of wars and troubled times comes to your ears, have no fear; for these things have to be, but the end will not be now.
10 Sa'annan ya ce masu, “Al'umma za ta tasar ma al'umma, mulki kuma za ya tasar wa mulki.
Then he said to them, Nation will be moved against nation and kingdom against kingdom:
11 Za a yi babbar girgizan kasa, a wurare dabam dabam kuma za a yi yunwa da annoba. Za a yi al'amura masu ban tsoro da manyan alamu daga sama.
There will be great earth-shocks and outbursts of disease in a number of places, and men will be without food; and there will be wonders and great signs from heaven.
12 Amma kafin abubuwan nan duka, za su kama ku, su kuma tsananta maku, suna mika ku ga majami'u da kuma gidajen kurkuku, za su kawo ku gaban sarakuna da gwamnoni saboda sunana.
But before all this, they will take you and be very cruel to you, giving you up to the Synagogues and to prisons, taking you before kings and rulers, because of my name.
13 Zai zamar maku zarafin shaida.
And it will be turned to a witness for you.
14 Saboda haka ku kudurta a ranku kada ku shirya yadda za ku amsa,
So take care not to be troubled before the time comes, about what answers you will give:
15 gama ni zan ba ku kalmomi da hikima, wadda dukan makiyanku ba za su yi tsayayya ko su karyata ku ba.
For I will give you words and wisdom, so that not one of those who are against you will be able to get the better of you, or to put you in the wrong.
16 Amma har da mahaifa da 'yan'uwa da dangi da abokai za su bashe ku, su kuma kashe wadansun ku.
But you will be given up even by your fathers and mothers, your brothers and relations and friends; and some of you will be put to death.
17 Kowa zai ki ku saboda sunana.
And you will be hated by all men, because of me.
18 Amma ba ko gashin kanku da zai hallaka.
But not a hair of your head will come to destruction.
19 A cikin hankurin ku za ku ribato rayukanku.
By going through all these things, you will keep your lives.
20 Sa'adda ku ka ga Urushalima tana kewaye da sojoji, sai ku sani da cewa faduwarta ta yi kusa.
But when you see armies all round about Jerusalem, then be certain that her destruction is near.
21 Sai wadanda su ke Yahudiya su gudu zuwa kan tuddai, wadanda suke tsakiyar gari kuma su tafi, kada su bar wadanda suke kauyuka su shigo ciki.
Then let those who are in Judaea go in flight to the mountains; and those who are in the middle of the town go out; and let not those who are in the country come in.
22 Gama wadannan ranakun ramako ne, saboda duka abubuwan da aka rubuta su cika.
For these are the days of punishment, in which all the things in the Writings will be put into effect.
23 Kaiton wadanda suke da juna biyu da masu ba da mama a wannan kwanakin! Gama za a sha kunci mai girma a kasan, da fushi kuma zuwa ga mutanen nan.
It will be hard for women who are with child, and for her with a baby at the breast, in those days. For great trouble will come on the land, and wrath on this people.
24 Za su fadi ta kaifin takobi kuma za a kai su cikin bauta ga dukan kasashe, al'ummai za su tattake Urushalima, har ya zuwa lokacin al'ummai ya cika.
And they will be put to death with the sword, and will be taken as prisoners into all the nations; and Jerusalem will be crushed under the feet of the Gentiles, till the times of the Gentiles are complete.
25 Za a ga alamomi cikin rana da wata da kuma taurari. A duniya kuma, al'ummai za su sha kunci, za su rude saboda rurin teku da rakuman ruwa.
And there will be signs in the sun and moon and stars; and on the earth, fear among the nations and doubt because of the loud noise of the sea and the waves;
26 Mutane za su suma da tsoro da kuma da tunanin abubuwa da za su abko wa duniya. Gama za a girgiza ikokin sammai.
Men's strength will go from them in fear and in waiting for the things which are coming on the earth; for the powers of the heavens will be moved.
27 Sa'annan za su ga Dan Mutum yana zuwa a cikin gajimarai da iko da daukaka mai girma.
And then they will see the Son of man coming in a cloud, with power and great glory.
28 Amma sa'adda wadannan abubuwa suka fara faruwa, tashi saye, sai ku daga kanku sama, saboda ceton ku ya kusato.”
But when these things come about, let your heads be lifted up, because your salvation is near.
29 Yesu ya bada misali, “Duba itacen baure, da duka itatuwa.
And he made a story for them: See the fig-tree, and all the trees;
30 Sa'adda su ke fitar da ganye, za ku gani da kanku cewa bazara ta yi kusa kuma.
When they put out their young leaves, you take note of it, and it is clear to you that summer is coming.
31 Haka kuma, sa'adda ku ka ga wadannan abubuwa suna faruwa, ku sani cewa mulkin Allah ya yi kusa.
In the same way, when you see these things taking place you may be certain that the kingdom of God is near.
32 Gaskiya, na ke gaya maku, wannan zamani ba za ya shude ba, sai duka abubuwan nan sun faru.
Truly I say to you, This generation will not come to an end till all things are complete.
33 Sama da kasa za su shude, amma maganata ba za ta shude ba.
Heaven and earth will come to an end, but my words will not come to an end.
34 Amma ku lura da kanku, domin kada ku nawaita zuciyarku da tararradin duniya da shayeshaye da damuwa ta rayuwa. Gama ranar za ta zo babu shiri
But give attention to yourselves, for fear that your hearts become over-full of the pleasures of food and wine, and the cares of this life, and that day may come on you suddenly, and take you as in a net:
35 kamar tarko. Gama zai zo akan kowa da ke rayuwa a fuskar dukan duniya.
For so it will come on all those who are living on the face of all the earth.
36 Amma ku zama a fadake kowanne lokaci, kuna addu'a domin ku iya samun karfin tserewa dukan wadannan abubuwa da za su faru, da kuma yadda za ku tsaya a gaban Dan Mutum.”
But keep watch at all times with prayer, that you may be strong enough to come through all these things and take your place before the Son of man.
37 Da rana yana koyarwa a cikin haikali, dukan dare kuma yakan tafi dutsen da a ke kira zaitun.
And every day he was teaching in the Temple and every night he went out to the mountain which is named the Mountain of Olives to take his rest.
38 Dukan mutane suka rika zuwa wurinsa da sassafe domin su ji shi a haikali.
And all the people came early in the morning to give ear to his words in the Temple.

< Luka 21 >