< Luka 21 >

1 Yesu ya tada ido sai ya ga mutane masu arziki wadanda suke saka baikonsu a cikin ma'aji.
And having looked up, he saw the rich casting their gifts into the treasury.
2 Ya ga wata gwauruwa matalauciya tana saka anini biyu a ciki.
And he also saw a certain poor widow there casting in two mites.
3 Sai ya ce, “Gaskiya ina gaya maku, wannan matalauciyar gwauruwa ta saka fiye da dukansu.
And he said, Truly I say to you, that this poor widow cast in more than they all.
4 Duka wadannan sun bayar da baikonsu daga cikin yalwarsu. Amma wannan gwauruwan, daga cikin talaucin ta, ta saka dukan iyakar kudinta na zaman gari da take da shi.”
For all these cast into the offerings of God from their abundance, but this woman from her poverty cast in all the living that she had.
5 Kamar yadda wadansu suke maganan haikali, yadda aka yi masa ado da duwatsu masu daraja da bayebaye, ya ce,
And as some spoke about the temple, that it was adorned with fine stones and gifts, he said,
6 “Game da wadannan abubuwa da ku ke gani, rana tana zuwa da ba dutse ko daya da zai zauna kan dan'uwansa da ba za a rushe kasa ba.”
These things that ye see, the days will come during which there will not be left a stone upon a stone that will not be thrown down.
7 Sai suka yi masa tambaya, cewa, “Malam, yaushe ne wadannan abubuwan zasu faru? Menene kuma zai zama alama sa'adda wadannan abubuwa suna shirin faruwa?”
And they questioned him, saying, Teacher, when therefore will these things be? And what is the sign when these things are going to happen?
8 Yesu ya amsa, “Ku yi hankali kada a rude ku. Gama dayawa zasu zo a cikin sunana, suna cewa, 'Ni ne shi,' kuma, 'Lokaci ya yi kusa.' Kada ku bi su.
And he said, Watch that ye may not be led astray, for many will come in my name, saying, I am, and, The time has come near. Go ye not therefore after them.
9 Sa'adda ku ka ji game da yakoki da hargitsi, kada ku firgita, dole ne wadannan abubuwa su faru tukuna, amma karshe ba zai faru nan da nan ba.”
And when ye may hear of wars and tumults, do not be alarmed, for these things must first happen, but the end is not straightaway.
10 Sa'annan ya ce masu, “Al'umma za ta tasar ma al'umma, mulki kuma za ya tasar wa mulki.
Then he said to them, Nation will rise against nation, and kingdom against kingdom.
11 Za a yi babbar girgizan kasa, a wurare dabam dabam kuma za a yi yunwa da annoba. Za a yi al'amura masu ban tsoro da manyan alamu daga sama.
And great earthquakes will be in various places, and famines and plagues. And there will be fearful sights and great signs from the sky.
12 Amma kafin abubuwan nan duka, za su kama ku, su kuma tsananta maku, suna mika ku ga majami'u da kuma gidajen kurkuku, za su kawo ku gaban sarakuna da gwamnoni saboda sunana.
But before all these things, they will throw their hands on you, and will persecute you, delivering you up to the synagogues and prisons, being brought before kings and rulers for my name's sake.
13 Zai zamar maku zarafin shaida.
But it will go out from you for testimony.
14 Saboda haka ku kudurta a ranku kada ku shirya yadda za ku amsa,
Settle therefore in your hearts not to premeditate to make defense.
15 gama ni zan ba ku kalmomi da hikima, wadda dukan makiyanku ba za su yi tsayayya ko su karyata ku ba.
For I will give you a mouth and wisdom that all those who oppose you will not be able to contradict or to resist.
16 Amma har da mahaifa da 'yan'uwa da dangi da abokai za su bashe ku, su kuma kashe wadansun ku.
And ye will be betrayed even by parents, and kinsmen, and friends, and brothers. And some of you they will condemn to death.
17 Kowa zai ki ku saboda sunana.
And ye will be hated by all men because of my name.
18 Amma ba ko gashin kanku da zai hallaka.
And, no, not a hair of your head will perish.
19 A cikin hankurin ku za ku ribato rayukanku.
In your perseverance ye gain your souls.
20 Sa'adda ku ka ga Urushalima tana kewaye da sojoji, sai ku sani da cewa faduwarta ta yi kusa.
But when ye see Jerusalem surrounded by armies, then know that the desolation of it has come near.
21 Sai wadanda su ke Yahudiya su gudu zuwa kan tuddai, wadanda suke tsakiyar gari kuma su tafi, kada su bar wadanda suke kauyuka su shigo ciki.
Then let those in Judea flee to the mountains, and let those in the midst of it depart out, and let not those in the rural areas enter into it.
22 Gama wadannan ranakun ramako ne, saboda duka abubuwan da aka rubuta su cika.
Because these are days of vengeance to fulfill all things that are written.
23 Kaiton wadanda suke da juna biyu da masu ba da mama a wannan kwanakin! Gama za a sha kunci mai girma a kasan, da fushi kuma zuwa ga mutanen nan.
But woe to those who have in the womb, and to those who suckle in those days. For there will be great distress upon the land, and wrath to this people.
24 Za su fadi ta kaifin takobi kuma za a kai su cikin bauta ga dukan kasashe, al'ummai za su tattake Urushalima, har ya zuwa lokacin al'ummai ya cika.
And they will fall by the jaw of the sword, and will be led away captive into all the nations. And Jerusalem will be trampled down by the Gentiles until the times of the Gentiles are fulfilled.
25 Za a ga alamomi cikin rana da wata da kuma taurari. A duniya kuma, al'ummai za su sha kunci, za su rude saboda rurin teku da rakuman ruwa.
And there will be signs in sun and moon and stars, and upon the earth distress of nations, with perplexity, roaring of sea and of tossing,
26 Mutane za su suma da tsoro da kuma da tunanin abubuwa da za su abko wa duniya. Gama za a girgiza ikokin sammai.
fainting of men from fear, and of anticipation of the things coming upon the world, for the powers of the heavens will be shaken.
27 Sa'annan za su ga Dan Mutum yana zuwa a cikin gajimarai da iko da daukaka mai girma.
And then they will see the Son of man coming in a cloud with power and much glory.
28 Amma sa'adda wadannan abubuwa suka fara faruwa, tashi saye, sai ku daga kanku sama, saboda ceton ku ya kusato.”
And when these things begin to happen, stand upright, and lift up your heads, because your redemption approaches.
29 Yesu ya bada misali, “Duba itacen baure, da duka itatuwa.
And he spoke a parable to them. Behold the fig tree, and all the trees.
30 Sa'adda su ke fitar da ganye, za ku gani da kanku cewa bazara ta yi kusa kuma.
When they are now sprouting, ye know seeing for yourselves that summer is now near.
31 Haka kuma, sa'adda ku ka ga wadannan abubuwa suna faruwa, ku sani cewa mulkin Allah ya yi kusa.
Even so ye, when ye see these things happening, know ye that the kingdom of God is near.
32 Gaskiya, na ke gaya maku, wannan zamani ba za ya shude ba, sai duka abubuwan nan sun faru.
Truly I say to you, that this generation will, no, not pass away until all things happen.
33 Sama da kasa za su shude, amma maganata ba za ta shude ba.
The sky and the earth will pass away, but my words may, no, not pass away.
34 Amma ku lura da kanku, domin kada ku nawaita zuciyarku da tararradin duniya da shayeshaye da damuwa ta rayuwa. Gama ranar za ta zo babu shiri
But take heed to yourselves, lest your hearts be weighed down in debauchery and drunkenness and mundane cares, and that day come upon you sudden.
35 kamar tarko. Gama zai zo akan kowa da ke rayuwa a fuskar dukan duniya.
For it will come like a trap upon all those who sit upon the face of all the earth.
36 Amma ku zama a fadake kowanne lokaci, kuna addu'a domin ku iya samun karfin tserewa dukan wadannan abubuwa da za su faru, da kuma yadda za ku tsaya a gaban Dan Mutum.”
Watch ye therefore, making supplication at all times, so that ye may be considered worthy to escape all these things going to happen, and to stand before the Son of man.
37 Da rana yana koyarwa a cikin haikali, dukan dare kuma yakan tafi dutsen da a ke kira zaitun.
And during the days he was teaching in the temple, and going forth the nights, he lodged on the mount that is called Olives.
38 Dukan mutane suka rika zuwa wurinsa da sassafe domin su ji shi a haikali.
And all the people rose early in the morning to him in the temple to hear him.

< Luka 21 >