< Luka 21 >

1 Yesu ya tada ido sai ya ga mutane masu arziki wadanda suke saka baikonsu a cikin ma'aji.
Men idet han saa op, fik han Øje paa de rige, som lagde deres Gaver i Tempelblokken.
2 Ya ga wata gwauruwa matalauciya tana saka anini biyu a ciki.
Men han saa en fattig Enke, som lagde to Skærve deri.
3 Sai ya ce, “Gaskiya ina gaya maku, wannan matalauciyar gwauruwa ta saka fiye da dukansu.
Og han sagde: „Sandelig, siger jeg eder, at denne fattige Enke lagde mere i end de alle.
4 Duka wadannan sun bayar da baikonsu daga cikin yalwarsu. Amma wannan gwauruwan, daga cikin talaucin ta, ta saka dukan iyakar kudinta na zaman gari da take da shi.”
Thi alle disse lagde af deres Overflod hen til Gaverne; men hun lagde af sin Fattigdom al sin Ejendom, som hun havde.‟
5 Kamar yadda wadansu suke maganan haikali, yadda aka yi masa ado da duwatsu masu daraja da bayebaye, ya ce,
Og da nogle sagde om Helligdommen, at den var prydet med smukke Stene og Tempelgaver, sagde han:
6 “Game da wadannan abubuwa da ku ke gani, rana tana zuwa da ba dutse ko daya da zai zauna kan dan'uwansa da ba za a rushe kasa ba.”
„Disse Ting, som I se — der skal komme Dage, da der ikke lades Sten paa Sten, som jo skal nedbrydes.‟
7 Sai suka yi masa tambaya, cewa, “Malam, yaushe ne wadannan abubuwan zasu faru? Menene kuma zai zama alama sa'adda wadannan abubuwa suna shirin faruwa?”
Men de spurgte ham og sagde: „Mester! naar skal dette da ske? og hvad er Tegnet paa, naar dette skal ske?‟
8 Yesu ya amsa, “Ku yi hankali kada a rude ku. Gama dayawa zasu zo a cikin sunana, suna cewa, 'Ni ne shi,' kuma, 'Lokaci ya yi kusa.' Kada ku bi su.
Men han sagde: „Ser til, at I ikke blive forførte; thi mange skulle paa mit Navn komme og sige: Det er mig, og: Tiden er kommen nær. Gaar ikke efter dem!
9 Sa'adda ku ka ji game da yakoki da hargitsi, kada ku firgita, dole ne wadannan abubuwa su faru tukuna, amma karshe ba zai faru nan da nan ba.”
Men naar I høre om Krige og Oprør, da forskrækkes ikke; thi dette maa først ske, men Enden er der ikke straks.‟
10 Sa'annan ya ce masu, “Al'umma za ta tasar ma al'umma, mulki kuma za ya tasar wa mulki.
Da sagde han til dem: „Folk skal rejse sig imod Folk, og Rige imod Rige.
11 Za a yi babbar girgizan kasa, a wurare dabam dabam kuma za a yi yunwa da annoba. Za a yi al'amura masu ban tsoro da manyan alamu daga sama.
Og store Jordskælv skal der være her og der og Hungersnød og Pest, og der skal ske frygtelige Ting og store Tegn fra Himmelen.
12 Amma kafin abubuwan nan duka, za su kama ku, su kuma tsananta maku, suna mika ku ga majami'u da kuma gidajen kurkuku, za su kawo ku gaban sarakuna da gwamnoni saboda sunana.
Men forud for alt dette skulle de lægge Haand paa eder og forfølge eder og overgive eder til Synagoger og Fængsler, og I skulle føres frem for Konger og Landshøvdinger for mit Navns Skyld.
13 Zai zamar maku zarafin shaida.
Det skal falde ud for eder til Vidnesbyrd.
14 Saboda haka ku kudurta a ranku kada ku shirya yadda za ku amsa,
Lægger det da paa Hjerte, at I ikke forud skulle overtænke, hvorledes I skulle forsvare eder.
15 gama ni zan ba ku kalmomi da hikima, wadda dukan makiyanku ba za su yi tsayayya ko su karyata ku ba.
Thi jeg vil give eder Mund og Visdom, som alle eders Modstandere ikke skulle kunne modstaa eller modsige.
16 Amma har da mahaifa da 'yan'uwa da dangi da abokai za su bashe ku, su kuma kashe wadansun ku.
Men I skulle endog forraades af Forældre og Brødre og Frænder og Venner, og de skulle slaa nogle af eder ihjel.
17 Kowa zai ki ku saboda sunana.
Og I skulle hades af alle for mit Navns Skyld.
18 Amma ba ko gashin kanku da zai hallaka.
Og ikke et Haar paa eders Hoved skal gaa tabt.
19 A cikin hankurin ku za ku ribato rayukanku.
Ved eders Udholdenhed skulle I vinde eders Sjæle.
20 Sa'adda ku ka ga Urushalima tana kewaye da sojoji, sai ku sani da cewa faduwarta ta yi kusa.
Men naar I se Jerusalem omringet af Krigshære, da forstaar, at dens Ødelæggelse er kommen nær.
21 Sai wadanda su ke Yahudiya su gudu zuwa kan tuddai, wadanda suke tsakiyar gari kuma su tafi, kada su bar wadanda suke kauyuka su shigo ciki.
Da skulle de, som ere i Judæa, fly til Bjergene; og de, som ere midt i Staden, skulle vige bort derfra; og de, som ere paa Landet, skulle ikke gaa ind i den.
22 Gama wadannan ranakun ramako ne, saboda duka abubuwan da aka rubuta su cika.
Thi disse ere Hævnens Dage, da alt, hvad skrevet er, skal opfyldes.
23 Kaiton wadanda suke da juna biyu da masu ba da mama a wannan kwanakin! Gama za a sha kunci mai girma a kasan, da fushi kuma zuwa ga mutanen nan.
Men ve de frugtsommelige og dem, som give Die, i de Dage; thi der skal være stor Nød paa Jorden og Vrede over dette Folk.
24 Za su fadi ta kaifin takobi kuma za a kai su cikin bauta ga dukan kasashe, al'ummai za su tattake Urushalima, har ya zuwa lokacin al'ummai ya cika.
Og de skulle falde for Sværdets Od og føres fangne til alle Hedningerne; og Jerusalem skal nedtrædes af Hedningerne, indtil Hedningernes Tider fuldkommes.
25 Za a ga alamomi cikin rana da wata da kuma taurari. A duniya kuma, al'ummai za su sha kunci, za su rude saboda rurin teku da rakuman ruwa.
Og der skal ske Tegn i Sol og Maane og Stjerner, og paa Jorden skulle Folkene ængstes i Fortvivlelse over Havets og Bølgernes Brusen,
26 Mutane za su suma da tsoro da kuma da tunanin abubuwa da za su abko wa duniya. Gama za a girgiza ikokin sammai.
medens Mennesker forsmægte af Frygt og Forventning om de Ting, som komme over Jorderige; thi Himmelens Kræfter skulle rystes.
27 Sa'annan za su ga Dan Mutum yana zuwa a cikin gajimarai da iko da daukaka mai girma.
Og da skulle de se Menneskesønnen komme i Sky med Kraft og megen Herlighed.
28 Amma sa'adda wadannan abubuwa suka fara faruwa, tashi saye, sai ku daga kanku sama, saboda ceton ku ya kusato.”
Men naar disse Ting begynde at ske, da ser op og opløfter eders Hoveder, efterdi eders Forløsning stunder til.‟
29 Yesu ya bada misali, “Duba itacen baure, da duka itatuwa.
Og han sagde dem en Lignelse: „Ser Figentræet og alle Træerne;
30 Sa'adda su ke fitar da ganye, za ku gani da kanku cewa bazara ta yi kusa kuma.
naar de alt springe ud, da se I og skønne af eder selv, at Sommeren nu er nær.
31 Haka kuma, sa'adda ku ka ga wadannan abubuwa suna faruwa, ku sani cewa mulkin Allah ya yi kusa.
Saaledes skulle ogsaa I, naar I se disse Ting ske, skønne, at Guds Rige er nær.
32 Gaskiya, na ke gaya maku, wannan zamani ba za ya shude ba, sai duka abubuwan nan sun faru.
Sandelig, siger jeg eder, at denne Slægt skal ingenlunde forgaa, førend det er sket alt sammen.
33 Sama da kasa za su shude, amma maganata ba za ta shude ba.
Himmelen og Jorden skulle forgaa; men mine Ord skulle ingenlunde forgaa.
34 Amma ku lura da kanku, domin kada ku nawaita zuciyarku da tararradin duniya da shayeshaye da damuwa ta rayuwa. Gama ranar za ta zo babu shiri
Men vogter eder, at eders Hjerter ikke nogen Tid besværes af Svir og Drukkenskab og timelige Bekymringer, saa hin Dag kommer pludseligt over eder som en Snare.
35 kamar tarko. Gama zai zo akan kowa da ke rayuwa a fuskar dukan duniya.
Thi komme skal den over alle dem, der bo paa hele Jordens Flade.
36 Amma ku zama a fadake kowanne lokaci, kuna addu'a domin ku iya samun karfin tserewa dukan wadannan abubuwa da za su faru, da kuma yadda za ku tsaya a gaban Dan Mutum.”
Og vaager og beder til enhver Tid, for at I maa blive i Stand til at undfly alle disse Ting, som skulle ske, og bestaa for Menneskesønnen.‟
37 Da rana yana koyarwa a cikin haikali, dukan dare kuma yakan tafi dutsen da a ke kira zaitun.
Men han lærte om Dagene i Helligdommen, men om Nætterne gik han ud og overnattede paa det Bjerg, som kaldes Oliebjerget.
38 Dukan mutane suka rika zuwa wurinsa da sassafe domin su ji shi a haikali.
Og hele Folket kom aarle til ham i Helligdommen for at høre ham.

< Luka 21 >