< Luka 20 >

1 Ana nan wata rana, Yesu yana kan koyarwa a haikali da wa'azin bishara, sai shugaban firistoci da marubuta suka zo wurinsa da dattawa.
В один из тех дней, когда Он учил народ в храме и благовествовал, приступили первосвященники и книжники со старейшинами,
2 Suka yi magana, su na ce masa, “Gaya mana da wanne iko ne ka ke yin wadannan abubuwan? Ko wanene ya baka wannan ikon?”
и сказали Ему: скажи нам, какою властью Ты это делаешь, или кто дал Тебе власть сию?
3 Ya amsa sai ya ce masu, “Ni ma zan yi maku tambaya. Gaya mani game
Он сказал им в ответ: спрошу и Я вас об одном, и скажите Мне:
4 da baptisman Yahaya. Daga sama take ko kuwa daga mutane ne?”
крещение Иоанново с небес было, или от человеков?
5 Sai suka yi mahawara da junansu, suna cewa, “In mun ce, 'Daga sama,' zai ce, 'To don me ba ku ba da gaskiya gareshi ba?'
Они же, рассуждая между собою, говорили: если скажем: с небес, то скажет: почему же вы не поверили ему?
6 Amma in mun ce, 'Daga mutane ne,' dukan mutane za su jejjefe mu da duwatsu, domin sun tabbata a ransu Yahaya annabi ne.”
а если скажем: от человеков, то весь народ побьет нас камнями, ибо он уверен, что Иоанн есть пророк.
7 Sai suka amsa cewa ba su san ko daga ina ne take ba.
И отвечали: не знаем откуда.
8 Yesu yace masu, “To haka ni ma ba zan gaya maku ko da wanne iko nake yin wadannan abubuwan ba.”
Иисус сказал им: и Я не скажу вам, какою властью это делаю.
9 Ya gaya wa mutane wannan misali, “Wani mutum ya dasa gonar inabi, ya ba wadansu manoma jinginarta, sai ya tafi wata kasa har ya dade.
И начал Он говорить к народу притчу сию: один человек насадил виноградник и отдал его виноградарям, и отлучился на долгое время;
10 Da lokacin girbi ya yi sai ya aiki wani bawansa zuwa wurin manoman, saboda su bashi daga cikin anfanin gonar. Amma manoman suka doke shi, sai suka kore shi hannu wofi.
и в свое время послал к виноградарям раба, чтобы они дали ему плодов из виноградника; но виноградари, прибив его, отослали ни с чем.
11 Ya aike wani bawa kuma sai suka daddoke shi, suka kunyatar da shi, suka kore shi hannu wofi.
Еще послал другого раба; но они и этого, прибив и обругав, отослали ни с чем.
12 Ya kuma sake aike na uku suka yi masa rauni, suka jefar da shi a waje.
И еще послал третьего; но они и того, изранив, выгнали.
13 Sai mai gonar inabin ya ce, 'Me zan yi? Zan aiki kaunattacen dana. Watakila zasu ba shi daraja.'
Тогда сказал господин виноградника: что мне делать? Пошлю сына моего возлюбленного; может быть, увидев его, постыдятся.
14 Amma sa'adda manoman suka gan shi, suka yi shawara a tsakaninsu, cewa, 'Wannan ne magajin. Bari mu kashe shi, saboda gadon ya zama namu.'
Но виноградари, увидев его, рассуждали между собою, говоря: это наследник; пойдем, убьем его, и наследство его будет наше.
15 Suka jefar da shi waje daga gonar, suka kashe shi. Menene ubangijin gonar inabin zai yi da su?
И, выведя его вон из виноградника, убили. Что же сделает с ними господин виноградника?
16 Zai zo ya halakar da wadannan manoma, sai ya ba wadansu gonar.” Da suka ji wannan, suka ce, “Allah ya sawake!”
Придет и погубит виноградарей тех, и отдаст виноградник другим. Слышавшие же это сказали: да не будет!
17 Amma Yesu ya kalle su, sai yace, “Menene ma'anar wannan nassi? 'Dutsen da magina suka ki, an mayar da shi kan kusurwa'?
Но Он, взглянув на них, сказал: что значит сие написанное: камень, который отвергли строители, тот самый сделался главою угла?
18 Duk wanda ya fadi kan dutsen zai farfashe. Amma duk wanda dutsen ya fadi a kansa, zai rugurguza shi.”
Всякий, кто упадет на тот камень, разобьется, а на кого он упадет, того раздавит.
19 Sai marubutan da manyan firistocin suka so su kama shi a wannan sa'a, domin sun sani ya yi wannan misali a kansu ne. Amma sun ji tsoron mutane.
И искали в это время первосвященники и книжники, чтобы наложить на Него руки, но побоялись народа, ибо поняли, что о них сказал Он эту притчу.
20 Suna fakonsa, suka aiki magewaya, wadanda suke kamar masu adalci, saboda su sami kuskure cikin maganarsa, don su mika shi ga hukumci da kuma ikon gwamna.
И, наблюдая за Ним, подослали лукавых людей, которые, притворившись благочестивыми, уловили бы Его в каком-либо слове, чтобы предать Его начальству и власти правителя.
21 Suka tambaye shi, cewa, “Malam, mun sani da cewa kana fada da koyar da abin ke daidai, kuma ba wanda yake cusa maka ra'ayi, amma kana koyar da gaskiya game da hanyar Allah.
И они спросили Его: Учитель! мы знаем, что Ты правдиво говоришь и учишь и не смотришь на лице, но истинно пути Божию учишь;
22 Wai shin doka ne mu biya haraji ga Kaisar, ko babu?”
позволительно ли нам давать подать кесарю, или нет?
23 Amma Yesu ya gane makircinsu, sai ya ce masu,
Он же, уразумев лукавство их, сказал им: что вы Меня искушаете?
24 “Nuna mani dinari. Sifar wanene da kuma rubutun wanene akan sa?” Suka ce, “Na Kaisar ne.”
Покажите Мне динарий: чье на нем изображение и надпись? Они отвечали: кесаревы.
25 Sai ya ce masu, “To sai ku ba Kaisar abin da ke na Kaisar, ku kuma ba Allah, abin da ke na Allah.”
Он сказал им: итак, отдавайте кесарево кесарю, а Божие Богу.
26 Marubutan da manyan firistocin ba su sami abin zargi cikin maganarsa, a gaban mutane ba. Suka yi mamakin amsar sa, ba su kuma ce komai ba.
И не могли уловить Его в слове перед народом, и, удивившись ответу Его, замолчали.
27 Sa'adda wadansu Sadukiyawa suka zo wurinsa, wadan da suka ce babu tashin mattatu,
Тогда пришли некоторые из саддукеев, отвергающих воскресение, и спросили Его:
28 suka tambaye shi, cewa, “Malam, Musa ya rubuta mana cewa idan dan'uwan mutum ya mutu, mai mace kuma ba shi da yaro, sai dan'uwansa ya auri matar, ya samar wa dan'uwansa yaro.
Учитель! Моисей написал нам, что если у кого умрет брат, имевший жену, и умрет бездетным, то брат его должен взять его жену и восставить семя брату своему.
29 Akwai 'yan'uwa guda bakwai kuma na farin ya yi aure, sai ya mutu babu da,
Было семь братьев, первый, взяв жену, умер бездетным;
30 haka ma na biyun.
взял ту жену второй, и тот умер бездетным;
31 Na ukun ya aure ta, haka nan na bakwai ma bai bar yaya ba, har suka mutu.
взял ее третий; также и все семеро, и умерли, не оставив детей;
32 Daga baya sai matar ma ta mutu.
после всех умерла и жена;
33 To a ranar tashin mattatu, matar wa za ta zama? Domin duka bakwai din sun aure ta.”
итак, в воскресение которого из них будет она женою, ибо семеро имели ее женою?
34 Yesu ya ce masu, “'Ya'yan duniyan nan suna aure, ana kuma ba da su ga aure. (aiōn g165)
Иисус сказал им в ответ: чада века сего женятся и выходят замуж; (aiōn g165)
35 Amma wadanda aka ga cancantarsu a waccan tsara, sun isa su sami tashin mattatu, ba za suyi aure ko a aurar da su ba. (aiōn g165)
а сподобившиеся достигнуть того века и воскресения из мертвых ни женятся, ни замуж не выходят, (aiōn g165)
36 Gama ba za su mutu kuma ba, domin suna daidai da mala'iku kuma su 'ya'yan Allah ne, da shike su 'ya'yan tashin matattu ne.
и умереть уже не могут, ибо они равны Ангелам и суть сыны Божии, будучи сынами воскресения.
37 Amma batun tashi matattu, ko Musa ma ya nuna wannan, a cikin jeji, inda ya kira Ubangiji, Allah na Ibrahim da kuma Allah na Ishaku da Allah na Yakubu.
А что мертвые воскреснут, и Моисей показал при купине, когда назвал Господа Богом Авраама и Богом Исаака и Богом Иакова.
38 Yanzu shi ba Allahn matattu ba ne, amma na masu rai, saboda duka suna raye a wurinsa.”
Бог же не есть Бог мертвых, но живых, ибо у Него все живы.
39 Wadansu marubuta suka amsa, “Malam, ka amsa da kyau.”
На это некоторые из книжников сказали: Учитель! Ты хорошо сказал.
40 Gama ba su sake yi masa wadansu tambayoyi ba.
И уже не смели спрашивать Его ни о чем. Он же сказал им:
41 Yesu ya ce masu, “Yaya suke cewa Almasihu dan Dauda ne?
как говорят, что Христос есть Сын Давидов,
42 Gama Dauda da kansa ya ce a cikin littafin Zabura, Ubangiji ya ce wa Ubangiji na, 'Zauna a hannun dama na,
а сам Давид говорит в книге псалмов: сказал Господь Господу моему: седи одесную Меня,
43 sai na maida makiyanka a karkashin tafin sawunka.'
доколе положу врагов Твоих в подножие ног Твоих?
44 Dauda ya kira Kristi 'Ubangiji', to ta yaya ya zama dan Dauda?”
Итак, Давид Господом называет Его; как же Он Сын ему?
45 Dukan mutane suna ji ya ce wa almajiransa,
И когда слушал весь народ, Он сказал ученикам Своим:
46 “Ku yi hankali da marubuta, wadanda suna son tafiya da manyan riguna, suna kuma son a gaishe su a cikin kasuwanni, da mayan wuraren zama a cikin majami'u, da kuma manyan wurare a wurin bukukkuwa.
остерегайтесь книжников, которые любят ходить в длинных одеждах и любят приветствия в народных собраниях, председания в синагогах и предвозлежания на пиршествах,
47 Suna kuma kwace wa gwamraye gidaje, suna kuma badda kama ta wurin yin doguwar addu'a. Wadannan za su sha hukumci mai girma.”
которые поедают домы вдов и лицемерно долго молятся; они примут тем большее осуждение.

< Luka 20 >