< Luka 20 >

1 Ana nan wata rana, Yesu yana kan koyarwa a haikali da wa'azin bishara, sai shugaban firistoci da marubuta suka zo wurinsa da dattawa.
Un de ces jours-là, comme Jésus enseignait le peuple dans le temple, et qu'il annonçait la bonne nouvelle, les Princes des prêtres et les Scribes survinrent avec les Anciens,
2 Suka yi magana, su na ce masa, “Gaya mana da wanne iko ne ka ke yin wadannan abubuwan? Ko wanene ya baka wannan ikon?”
et lui dirent: " Dites-nous par quelle autorité vous faites ces choses, ou qui vous a donné cette autorité? "
3 Ya amsa sai ya ce masu, “Ni ma zan yi maku tambaya. Gaya mani game
Jésus leur répondit: " Moi aussi je vous ferai une question. Répondez-moi.
4 da baptisman Yahaya. Daga sama take ko kuwa daga mutane ne?”
Le baptême de Jean était-il du ciel, ou des hommes? "
5 Sai suka yi mahawara da junansu, suna cewa, “In mun ce, 'Daga sama,' zai ce, 'To don me ba ku ba da gaskiya gareshi ba?'
Mais ils faisaient entre eux cette réflexion: " Si nous répondons: Du ciel, il nous dira: Pourquoi n'avez-vous pas cru en lui?
6 Amma in mun ce, 'Daga mutane ne,' dukan mutane za su jejjefe mu da duwatsu, domin sun tabbata a ransu Yahaya annabi ne.”
Et si nous répondons: Des hommes, tout le peuple nous lapidera, car il est persuadé que Jean était un prophète. "
7 Sai suka amsa cewa ba su san ko daga ina ne take ba.
Ils lui répondirent donc qu'ils ne savaient d'où il était.
8 Yesu yace masu, “To haka ni ma ba zan gaya maku ko da wanne iko nake yin wadannan abubuwan ba.”
" Et Moi, leur dit Jésus, je ne vous dis pas non plus par quelle autorité je fais ces choses. "
9 Ya gaya wa mutane wannan misali, “Wani mutum ya dasa gonar inabi, ya ba wadansu manoma jinginarta, sai ya tafi wata kasa har ya dade.
Alors il se mit à dire au peuple cette parabole: " Un homme planta une vigne, et la loua à des vignerons; puis il s'en alla pour un temps assez long en pays étranger.
10 Da lokacin girbi ya yi sai ya aiki wani bawansa zuwa wurin manoman, saboda su bashi daga cikin anfanin gonar. Amma manoman suka doke shi, sai suka kore shi hannu wofi.
La saison étant venue, il envoya un serviteur aux vignerons, afin qu'ils lui donnassent du produit de la vigne. Mais eux, l'ayant battu, le renvoyèrent les mains vides.
11 Ya aike wani bawa kuma sai suka daddoke shi, suka kunyatar da shi, suka kore shi hannu wofi.
Il envoya encore un autre serviteur; mais, l'ayant aussi battu et traité indignement, ils le renvoyèrent les mains vides.
12 Ya kuma sake aike na uku suka yi masa rauni, suka jefar da shi a waje.
Il en envoya un troisième; mais, lui aussi, les vignerons le blessèrent et le jetèrent dehors.
13 Sai mai gonar inabin ya ce, 'Me zan yi? Zan aiki kaunattacen dana. Watakila zasu ba shi daraja.'
Alors le maître de la vigne se dit: Que ferai-je? J'enverrai mon fils bien-aimé; peut-être qu'en le voyant ils auront pour lui du respect.
14 Amma sa'adda manoman suka gan shi, suka yi shawara a tsakaninsu, cewa, 'Wannan ne magajin. Bari mu kashe shi, saboda gadon ya zama namu.'
Mais lorsque les vignerons le virent, ils se dirent entre eux: Celui-ci est l'héritier, tuons-le, afin que l'héritage soit à nous.
15 Suka jefar da shi waje daga gonar, suka kashe shi. Menene ubangijin gonar inabin zai yi da su?
Et l'ayant jeté hors de la vigne, ils le tuèrent. Que leur fera donc le maître de la vigne?
16 Zai zo ya halakar da wadannan manoma, sai ya ba wadansu gonar.” Da suka ji wannan, suka ce, “Allah ya sawake!”
Il viendra et exterminera ces vignerons, et donnera sa vigne à d'autres. " Ce qu'ayant entendu, ils dirent: " A Dieu ne plaise! "
17 Amma Yesu ya kalle su, sai yace, “Menene ma'anar wannan nassi? 'Dutsen da magina suka ki, an mayar da shi kan kusurwa'?
Mais, fixant le regard sur eux, Jésus dit: " Qu'est-ce donc que cette parole de l'Ecriture: La pierre qu'ont rejetée ceux qui bâtissaient est devenue la pierre angulaire?
18 Duk wanda ya fadi kan dutsen zai farfashe. Amma duk wanda dutsen ya fadi a kansa, zai rugurguza shi.”
Quiconque tombera sur cette pierre sera brisé; et celui sur qui elle tombera, sera écrasé. "
19 Sai marubutan da manyan firistocin suka so su kama shi a wannan sa'a, domin sun sani ya yi wannan misali a kansu ne. Amma sun ji tsoron mutane.
Les Princes des prêtres et les Scribes cherchèrent à se saisir de lui à l'heure même; mais la crainte du peuple les retint, car ils comprenaient bien que c'était pour eux que Jésus avait dit cette parabole.
20 Suna fakonsa, suka aiki magewaya, wadanda suke kamar masu adalci, saboda su sami kuskure cikin maganarsa, don su mika shi ga hukumci da kuma ikon gwamna.
Ils ne le perdirent donc pas de vue, et lui envoyèrent des gens apostés qui feignaient d'être justes, pour le surprendre dans ses paroles, afin de le livrer à l'autorité et au pouvoir du gouverneur.
21 Suka tambaye shi, cewa, “Malam, mun sani da cewa kana fada da koyar da abin ke daidai, kuma ba wanda yake cusa maka ra'ayi, amma kana koyar da gaskiya game da hanyar Allah.
Ces gens l'interrogèrent en ces termes: " Maître, nous savons que vous parlez et enseignez avec droiture, et sans faire acception de personne, mais que vous enseignez la voie de Dieu dans la vérité.
22 Wai shin doka ne mu biya haraji ga Kaisar, ko babu?”
Nous est-il permis, ou non, de payer le tribut à César? "
23 Amma Yesu ya gane makircinsu, sai ya ce masu,
Jésus, connaissant leur fourberie, leur dit: " Pourquoi me tentez-vous?
24 “Nuna mani dinari. Sifar wanene da kuma rubutun wanene akan sa?” Suka ce, “Na Kaisar ne.”
Montrez-moi un denier. De qui porte-t-il l'effigie et le nom? " Ils lui répondirent: " De César. "
25 Sai ya ce masu, “To sai ku ba Kaisar abin da ke na Kaisar, ku kuma ba Allah, abin da ke na Allah.”
Et il leur dit: " Rendez donc à César ce qui est à César, et à Dieu ce qui est à Dieu. "
26 Marubutan da manyan firistocin ba su sami abin zargi cikin maganarsa, a gaban mutane ba. Suka yi mamakin amsar sa, ba su kuma ce komai ba.
Ainsi ils ne purent le prendre en défaut sur aucune parole devant le peuple; et admirant sa réponse, ils gardèrent le silence.
27 Sa'adda wadansu Sadukiyawa suka zo wurinsa, wadan da suka ce babu tashin mattatu,
Quelques-uns des Sadducéens, qui nient la résurrection, s'approchèrent alors et l'interrogèrent:
28 suka tambaye shi, cewa, “Malam, Musa ya rubuta mana cewa idan dan'uwan mutum ya mutu, mai mace kuma ba shi da yaro, sai dan'uwansa ya auri matar, ya samar wa dan'uwansa yaro.
" Maître, lui dirent-ils, Moïse nous a donné cette loi: Si un homme, ayant une femme, meurt sans laisser d'enfants, que son frère prenne sa femme, et suscite des enfants à son frère.
29 Akwai 'yan'uwa guda bakwai kuma na farin ya yi aure, sai ya mutu babu da,
Or, il y avait sept frères; le premier prit une femme et mourut sans enfants.
30 haka ma na biyun.
Le second prit sa femme, et mourut aussi sans enfants.
31 Na ukun ya aure ta, haka nan na bakwai ma bai bar yaya ba, har suka mutu.
Le troisième la prit ensuite, et de même tous les sept, et ils moururent sans laisser d'enfants.
32 Daga baya sai matar ma ta mutu.
Après eux tous, la femme mourut aussi.
33 To a ranar tashin mattatu, matar wa za ta zama? Domin duka bakwai din sun aure ta.”
Duquel donc, au temps de la résurrection, sera-t-elle la femme, car elle l'a été de tous les sept? "
34 Yesu ya ce masu, “'Ya'yan duniyan nan suna aure, ana kuma ba da su ga aure. (aiōn g165)
Jésus leur dit: " Les enfants de ce siècle se marient et sont donnés en mariage; (aiōn g165)
35 Amma wadanda aka ga cancantarsu a waccan tsara, sun isa su sami tashin mattatu, ba za suyi aure ko a aurar da su ba. (aiōn g165)
mais ceux qui ont été trouvés dignes d'avoir part au siècle à venir et à la résurrection des morts, ne prennent point de femme et n'ont point de mari; (aiōn g165)
36 Gama ba za su mutu kuma ba, domin suna daidai da mala'iku kuma su 'ya'yan Allah ne, da shike su 'ya'yan tashin matattu ne.
aussi bien ne peuvent-ils plus mourir, puisqu'ils sont en comme les anges, et qu'ils sont fils de Dieu, étant fils de la résurrection.
37 Amma batun tashi matattu, ko Musa ma ya nuna wannan, a cikin jeji, inda ya kira Ubangiji, Allah na Ibrahim da kuma Allah na Ishaku da Allah na Yakubu.
Mais que les morts ressuscitent, c'est ce que Moïse lui-même a fait connaître dans le passage du Buisson, lorsqu'il nomme le Seigneur: Le Dieu d'Abraham, le Dieu d'Isaac et le Dieu de Jacob.
38 Yanzu shi ba Allahn matattu ba ne, amma na masu rai, saboda duka suna raye a wurinsa.”
Or il n'est pas Dieu des morts, mais des vivants; car tous sont vivants devant lui. "
39 Wadansu marubuta suka amsa, “Malam, ka amsa da kyau.”
Quelques-uns des Scribes, prenant la parole, lui dirent: " Maître, vous avez bien parlé. "
40 Gama ba su sake yi masa wadansu tambayoyi ba.
Et ils n'osaient plus lui poser aucune question.
41 Yesu ya ce masu, “Yaya suke cewa Almasihu dan Dauda ne?
Jésus leur dit: " Comment dit-on que le Christ est fils de David?
42 Gama Dauda da kansa ya ce a cikin littafin Zabura, Ubangiji ya ce wa Ubangiji na, 'Zauna a hannun dama na,
David lui-même dit dans le livre des Psaumes: Le Seigneur a dit à mon Seigneur: Asseyez-vous à ma droite,
43 sai na maida makiyanka a karkashin tafin sawunka.'
jusqu'à ce que je fasse de vos ennemis l'escabeau de vos pieds. —
44 Dauda ya kira Kristi 'Ubangiji', to ta yaya ya zama dan Dauda?”
David l'appelle donc Seigneur; comment peut-il être son fils? "
45 Dukan mutane suna ji ya ce wa almajiransa,
Tandis que tout le peuple l'écoutait, il dit à ses disciples:
46 “Ku yi hankali da marubuta, wadanda suna son tafiya da manyan riguna, suna kuma son a gaishe su a cikin kasuwanni, da mayan wuraren zama a cikin majami'u, da kuma manyan wurare a wurin bukukkuwa.
" Gardez-vous des Scribes, qui se plaisent à se promener en longues robes; qui aiment à être salués dans les places publiques, à occuper les premiers sièges dans les synagogues et les premières places dans les festins:
47 Suna kuma kwace wa gwamraye gidaje, suna kuma badda kama ta wurin yin doguwar addu'a. Wadannan za su sha hukumci mai girma.”
ces gens qui dévorent les maisons des veuves, et font pour l'apparence de longues prières, subiront une condamnation plus sévère. "

< Luka 20 >