< Luka 20 >

1 Ana nan wata rana, Yesu yana kan koyarwa a haikali da wa'azin bishara, sai shugaban firistoci da marubuta suka zo wurinsa da dattawa.
On one of those days, as he was teaching the people in the temple and preaching the Good News, the priests and scribes came to him with the elders.
2 Suka yi magana, su na ce masa, “Gaya mana da wanne iko ne ka ke yin wadannan abubuwan? Ko wanene ya baka wannan ikon?”
They asked him, “Tell us: by what authority do you do these things? Or who is giving you this authority?”
3 Ya amsa sai ya ce masu, “Ni ma zan yi maku tambaya. Gaya mani game
He answered them, “I also will ask you one question. Tell me:
4 da baptisman Yahaya. Daga sama take ko kuwa daga mutane ne?”
the baptism of John, was it from heaven, or from men?”
5 Sai suka yi mahawara da junansu, suna cewa, “In mun ce, 'Daga sama,' zai ce, 'To don me ba ku ba da gaskiya gareshi ba?'
They reasoned with themselves, saying, “If we say, ‘From heaven,’ he will say, ‘Why didn’t you believe him?’
6 Amma in mun ce, 'Daga mutane ne,' dukan mutane za su jejjefe mu da duwatsu, domin sun tabbata a ransu Yahaya annabi ne.”
But if we say, ‘From men,’ all the people will stone us, for they are persuaded that John was a prophet.”
7 Sai suka amsa cewa ba su san ko daga ina ne take ba.
They answered that they didn’t know where it was from.
8 Yesu yace masu, “To haka ni ma ba zan gaya maku ko da wanne iko nake yin wadannan abubuwan ba.”
Jesus said to them, “Neither will I tell you by what authority I do these things.”
9 Ya gaya wa mutane wannan misali, “Wani mutum ya dasa gonar inabi, ya ba wadansu manoma jinginarta, sai ya tafi wata kasa har ya dade.
He began to tell the people this parable: “A man planted a vineyard and rented it out to some farmers, and went into another country for a long time.
10 Da lokacin girbi ya yi sai ya aiki wani bawansa zuwa wurin manoman, saboda su bashi daga cikin anfanin gonar. Amma manoman suka doke shi, sai suka kore shi hannu wofi.
At the proper season, he sent a servant to the farmers to collect his share of the fruit of the vineyard. But the farmers beat him and sent him away empty.
11 Ya aike wani bawa kuma sai suka daddoke shi, suka kunyatar da shi, suka kore shi hannu wofi.
He sent yet another servant, and they also beat him and treated him shamefully, and sent him away empty.
12 Ya kuma sake aike na uku suka yi masa rauni, suka jefar da shi a waje.
He sent yet a third, and they also wounded him and threw him out.
13 Sai mai gonar inabin ya ce, 'Me zan yi? Zan aiki kaunattacen dana. Watakila zasu ba shi daraja.'
The lord of the vineyard said, ‘What shall I do? I will send my beloved son. It may be that seeing him, they will respect him.’
14 Amma sa'adda manoman suka gan shi, suka yi shawara a tsakaninsu, cewa, 'Wannan ne magajin. Bari mu kashe shi, saboda gadon ya zama namu.'
“But when the farmers saw him, they reasoned among themselves, saying, ‘This is the heir. Come, let’s kill him, that the inheritance may be ours.’
15 Suka jefar da shi waje daga gonar, suka kashe shi. Menene ubangijin gonar inabin zai yi da su?
Then they threw him out of the vineyard and killed him. What therefore will the lord of the vineyard do to them?
16 Zai zo ya halakar da wadannan manoma, sai ya ba wadansu gonar.” Da suka ji wannan, suka ce, “Allah ya sawake!”
He will come and destroy these farmers, and will give the vineyard to others.” When they heard that, they said, “May that never be!”
17 Amma Yesu ya kalle su, sai yace, “Menene ma'anar wannan nassi? 'Dutsen da magina suka ki, an mayar da shi kan kusurwa'?
But he looked at them and said, “Then what is this that is written, ‘The stone which the builders rejected was made the chief cornerstone’?
18 Duk wanda ya fadi kan dutsen zai farfashe. Amma duk wanda dutsen ya fadi a kansa, zai rugurguza shi.”
Everyone who falls on that stone will be broken to pieces, but it will crush whomever it falls on to dust.”
19 Sai marubutan da manyan firistocin suka so su kama shi a wannan sa'a, domin sun sani ya yi wannan misali a kansu ne. Amma sun ji tsoron mutane.
The chief priests and the scribes sought to lay hands on him that very hour, but they feared the people—for they knew he had spoken this parable against them.
20 Suna fakonsa, suka aiki magewaya, wadanda suke kamar masu adalci, saboda su sami kuskure cikin maganarsa, don su mika shi ga hukumci da kuma ikon gwamna.
They watched him and sent out spies, who pretended to be righteous, that they might trap him in something he said, so as to deliver him up to the power and authority of the governor.
21 Suka tambaye shi, cewa, “Malam, mun sani da cewa kana fada da koyar da abin ke daidai, kuma ba wanda yake cusa maka ra'ayi, amma kana koyar da gaskiya game da hanyar Allah.
They asked him, “Teacher, we know that you say and teach what is right, and aren’t partial to anyone, but truly teach the way of God.
22 Wai shin doka ne mu biya haraji ga Kaisar, ko babu?”
Is it lawful for us to pay taxes to Caesar, or not?”
23 Amma Yesu ya gane makircinsu, sai ya ce masu,
But he perceived their craftiness, and said to them, “Why do you test me?
24 “Nuna mani dinari. Sifar wanene da kuma rubutun wanene akan sa?” Suka ce, “Na Kaisar ne.”
Show me a denarius. Whose image and inscription are on it?” They answered, “Caesar’s.”
25 Sai ya ce masu, “To sai ku ba Kaisar abin da ke na Kaisar, ku kuma ba Allah, abin da ke na Allah.”
He said to them, “Then give to Caesar the things that are Caesar’s, and to God the things that are God’s.”
26 Marubutan da manyan firistocin ba su sami abin zargi cikin maganarsa, a gaban mutane ba. Suka yi mamakin amsar sa, ba su kuma ce komai ba.
They weren’t able to trap him in his words before the people. They marveled at his answer and were silent.
27 Sa'adda wadansu Sadukiyawa suka zo wurinsa, wadan da suka ce babu tashin mattatu,
Some of the Sadducees came to him, those who deny that there is a resurrection.
28 suka tambaye shi, cewa, “Malam, Musa ya rubuta mana cewa idan dan'uwan mutum ya mutu, mai mace kuma ba shi da yaro, sai dan'uwansa ya auri matar, ya samar wa dan'uwansa yaro.
They asked him, “Teacher, Moses wrote to us that if a man’s brother dies having a wife, and he is childless, his brother should take the wife and raise up children for his brother.
29 Akwai 'yan'uwa guda bakwai kuma na farin ya yi aure, sai ya mutu babu da,
There were therefore seven brothers. The first took a wife, and died childless.
30 haka ma na biyun.
The second took her as wife, and he died childless.
31 Na ukun ya aure ta, haka nan na bakwai ma bai bar yaya ba, har suka mutu.
The third took her, and likewise the seven all left no children, and died.
32 Daga baya sai matar ma ta mutu.
Afterward the woman also died.
33 To a ranar tashin mattatu, matar wa za ta zama? Domin duka bakwai din sun aure ta.”
Therefore in the resurrection whose wife of them will she be? For the seven had her as a wife.”
34 Yesu ya ce masu, “'Ya'yan duniyan nan suna aure, ana kuma ba da su ga aure. (aiōn g165)
Jesus said to them, “The children of this age marry and are given in marriage. (aiōn g165)
35 Amma wadanda aka ga cancantarsu a waccan tsara, sun isa su sami tashin mattatu, ba za suyi aure ko a aurar da su ba. (aiōn g165)
But those who are considered worthy to attain to that age and the resurrection from the dead neither marry nor are given in marriage. (aiōn g165)
36 Gama ba za su mutu kuma ba, domin suna daidai da mala'iku kuma su 'ya'yan Allah ne, da shike su 'ya'yan tashin matattu ne.
For they can’t die any more, for they are like the angels and are children of God, being children of the resurrection.
37 Amma batun tashi matattu, ko Musa ma ya nuna wannan, a cikin jeji, inda ya kira Ubangiji, Allah na Ibrahim da kuma Allah na Ishaku da Allah na Yakubu.
But that the dead are raised, even Moses showed at the bush, when he called the Lord ‘The God of Abraham, the God of Isaac, and the God of Jacob.’
38 Yanzu shi ba Allahn matattu ba ne, amma na masu rai, saboda duka suna raye a wurinsa.”
Now he is not the God of the dead, but of the living, for all are alive to him.”
39 Wadansu marubuta suka amsa, “Malam, ka amsa da kyau.”
Some of the scribes answered, “Teacher, you speak well.”
40 Gama ba su sake yi masa wadansu tambayoyi ba.
They didn’t dare to ask him any more questions.
41 Yesu ya ce masu, “Yaya suke cewa Almasihu dan Dauda ne?
He said to them, “Why do they say that the Christ is David’s son?
42 Gama Dauda da kansa ya ce a cikin littafin Zabura, Ubangiji ya ce wa Ubangiji na, 'Zauna a hannun dama na,
David himself says in the book of Psalms, ‘The Lord said to my Lord, “Sit at my right hand,
43 sai na maida makiyanka a karkashin tafin sawunka.'
until I make your enemies the footstool of your feet.”’
44 Dauda ya kira Kristi 'Ubangiji', to ta yaya ya zama dan Dauda?”
“David therefore calls him Lord, so how is he his son?”
45 Dukan mutane suna ji ya ce wa almajiransa,
In the hearing of all the people, he said to his disciples,
46 “Ku yi hankali da marubuta, wadanda suna son tafiya da manyan riguna, suna kuma son a gaishe su a cikin kasuwanni, da mayan wuraren zama a cikin majami'u, da kuma manyan wurare a wurin bukukkuwa.
“Beware of those scribes who like to walk in long robes, and love greetings in the marketplaces, the best seats in the synagogues, and the best places at feasts;
47 Suna kuma kwace wa gwamraye gidaje, suna kuma badda kama ta wurin yin doguwar addu'a. Wadannan za su sha hukumci mai girma.”
who devour widows’ houses, and for a pretense make long prayers. These will receive greater condemnation.”

< Luka 20 >