< Luka 2 >

1 Ananan cikin kwanakin, sai Kaisar Augustas ya yi shela ya umarta a kidaya dukan mutane da ke zaune a cikin duniya.
Un notika tanī laikā, ka grāmatas no ķeizara Augusta tapa izsūtītas, ka visa pasaule taptu uzrakstīta.
2 Wannan itace kidaya ta farko da aka yi lokacin da Kiriniyus yake mulkin Suriya.
Un šī pirmā uzrakstīšana notika to brīdi, kad Kirenijus Sīrijā valdīja.
3 Sabili da haka, kowa ya koma garinsa domin a yi masa rijista domin kidayan.
Un visi nogāja, ka liktos pierakstīties, ikviens savā cilts pilsētā.
4 Yusufu kuma ya tashi ya bar birnin Nazarat zuwa garin Baitalami da ke Yahudiya, wanda ake kuma kira birnin Dauda, domin shi daga zuriyar iyalin Dauda ne.
Tad arī Jāzeps no Galilejas, no Nacaretes pilsētas, nogāja uz Jūdu zemi, uz Dāvida pilsētu, vārdā Bētlemi, tāpēc ka tas bija no Dāvida rada un cilts,
5 Ya je can ya yi rijista tare da Maryamu, wadda yake tashi tana kuma da juna biyu.
Ka liktos pierakstīties ar Mariju, savu saderēto sievu, kas bija grūta.
6 Ya zama sa'adda suke can, lokaci ya yi da za ta haifi danta.
Un notikās, tiem turpat esot, tas laiks atnāca, ka tai bija dzemdēt.
7 Ta haifi da, dan farinta kuwa, ta nade shi da kyau da 'yan tsummoki. Ta sa shi cikin wani kwami na dabbobi, gama babu daki dominsu a masaukin.
Un viņai piedzima pirmdzimtais Dēls, un tā To ietina autiņos un To lika silē, jo tiem citur nebija rūmes tai mājas vietā.
8 A cikin wannan yankin, akwai makiyaya wadanda suke zama a sarari suna tsaron garken tumakinsu da dare.
Un gani bija ap to pašu vietu laukā pie laidariem, tie nomodā būdami naktī savus lopus sargāja.
9 Nan da nan, sai mala'ikan Ubangiji ya bayyana gare su, daukakar Ubangiji kuma ta haskaka kewaye da su, sai suka figita kwarai.
Un redzi, Tā Kunga eņģelis pie tiem piestājās, un Tā Kunga spožums tos apspīdēja, un tie bijās ļoti.
10 Sai mala'ikan ya ce masu, “Kada ku ji tsoro, domin na kawo maku labari mai dadi da zai kawo murna da yawa ga dukan mutane.
Un tas eņģelis uz tiem sacīja: “Nebīstaties, jo redzi, es jums pasludinu lielu prieku, kas visiem ļaudīm notiks;
11 Yau an haifi maku mai ceto a cikin birnin Dauda! Shine Almasihu Ubangiji!
Jo jums šodien Tas Pestītājs dzimis, kas ir Kristus, Tas Kungs, Dāvida pilsētā.
12 Wannan itace alama da za a ba ku. Za ku ga dan jariri nade cikin 'yan tsummoki kwance cikin kwamin dabbobi.”
Un to ņematies par zīmi: jūs atradīsiet bērnu autos ietītu un silē gulošu.”
13 Nan take, sai ga babban taro daga sama tare da mala'ikan suna yabon Allah, suna cewa,
Un tūdaļ tur pie tā eņģeļa bija tas debesu draudzības pulks; tie Dievu slavēja un sacīja:
14 “Daukaka ga Allah daga bisa, bari salama ta kasance a duniya tsakanin mutanen da ya ke jin dadinsu.”
“Gods Dievam augstībā un miers virs zemes un cilvēkiem labs prāts.”
15 Ya zama sa'adda mala'iku suka bar su zuwa cikin sama, sai makiyayan su ka ce wa junansu, “Bari mu je Baitalami mu ga wannan abin da ya faru, wanda Ubangiji ya nuna mana.”
Un notikās, kad tie eņģeļi no tiem uz debesīm bija aizgājuši, tad tie gani runāja savā starpā: ejam tad nu uz Bētlemi, raudzīt, kas tur noticis, kā Tas Kungs mums licis ziņu dot.
16 Su ka yi hamzari suka tafi can sun iske Maryamu da Yusufu, suka ga jaririn kuwa kwance a cikin kwamin dabbobin.
Un tie steigdamies nāca un atrada gan Mariju, gan Jāzepu un To bērniņu, silē gulošu.
17 Bayan da sun ga wannan, suka gaya wa mutane abinda aka gaya masu game da wannan yaro.
Bet kad tie to bija redzējuši, tad tie izpauda to vārdu, kas tiem par To bērnu bija sacīts.
18 Dukan wadanda su ka ji, su ka yi mamaki kwarai game da abin da makiyayan su ka gaya masu.
Un visi, kas to dzirdēja, izbrīnījās par to valodu, ko tie gani tiem bija sacījuši.
19 Amma ita Maryamu ta ci gaba da tunani akan wadanan abubuwa da ta ji, tana tunani mai zurfi a cikin zuciyarta.
Bet Marija visus tos vārdus paturēja, tos savā sirdī apdomādama.
20 Makiyayan suka koma suna ta daukaka da yabon Allah domin dukan abubuwan da suka ji, suka kuma gani, dadai da yadda aka gaya masu.
Un tie gani griezās uz mājām, godāja un teica Dievu par visu, ko tie bija dzirdējuši un redzējuši, kā uz tiem bija sacīts.
21 Da ya kai kwana takwas, lokacin da za a yi wa jaririn kaciya, sai aka rada masa suna Yesu, sunan da mala'ikan ya bashi kamin a yi cikinsa.
Un kad astoņas dienas bija pagājušas, ka tas bērns taptu apgraizīts, tad Viņa vārdu nosauca Jēzu, kā no tā eņģeļa bija sacīts, pirms Viņš bija ieņemts mātes miesās.
22 Da kwanakin tsarkakewar su ya wuce bisa ga shari'ar Musa, Yusufu da Maryamu suka kawo shi cikin haikali a Urushalima dominsu mika shi ga Ubangiji.
Un kad viņu šķīstīšanas dienas nāca pēc Mozus bauslības, tad tie Viņu nesa uz Jeruzālemi, ka To stādītu Tā Kunga priekšā.
23 Kamar yadda aka rubuta a dokokin Ubangiji, “Za a kira duk da na fari kebabbe ga Ubangiji.”
(Kā Tā Kunga bauslībā stāv rakstīts: ikviena pirmdzimtība no vīriešu kārtas lai top nosaukta Tam Kungam svēta);
24 Suka kuma zo su mika hadaya bisa ga yadda aka fada a shari'ar Ubangiji, “Kurciyoyi biyu ko 'yan tantabaru biyu.”
Ka tie arī to upuri dotu, kā Tā Kunga bauslībā ir sacīts: vienu pāri ūbeļu baložu vai divus jaunus baložus.
25 Ga shi akwai wani mutum a Ushalima mai suna Siman. Wannan mutum adali ne kuma mai ibada. Yana jiran mai ta'aziyar Isra'ila, kuma Ruhu Mai-sarki na bisansa.
Un redzi, viens cilvēks bija Jeruzālemē, vārdā Sīmeans; šis cilvēks bija taisns un dievbijīgs, gaidīdams uz Israēla iepriecināšanu, un Tas Svētais Gars bija iekš viņa.
26 An kuma bayyana masa ta wurin Ruhu Mai-tsarki cewa ba zai mutu ba sai ya ga Kristi na Ubangiji.
Tam no Svētā Gara bija pasludināts, ka nāvi neredzēšot, iekams Tā Kunga Svaidīto nebūšot redzējis.
27 Wata rana Siman ya zo cikin haikali ta wurin jagorar Ruhu Mai-tsarki. Da iyayen suka kawo yaron ciki, wato Yesu, domin su cika sharudan da shari'ar ke bukata,
Tas nāca Dieva namā no Svētā Gara skubināts; un kad tie vecāki To Jēzus bērnu ienesa, ka ar To darītu pēc bauslības ieraduma,
28 sai Siman ya karbe shi cikin hanuwansa, ya yabi Allah ya ce,
Tad To uz savām rokām ņēmis, viņš Dievu teica un sacīja:
29 “Yanzu bari bawanka ya tafi da salama, Ubangiji, bisa ga kalmarka.
“Kungs, lai nu Tavs kalps aiziet mierā, kā Tu esi sacījis;
30 Domin idanuna sun ga cetonka,
Jo manas acis Tavu pestīšanu redzējušas,
31 wanda ka shirya a gaban dukan mutane:
Ko Tu esi sataisījis priekš visiem ļaudīm,
32 Haske ne na wahayi ga al'ummai, kuma daukakar mutanenka Isra'ila.”
Gaismu, apgaismot pagānus, un par slavu Taviem Israēla ļaudīm.”
33 Mahaifin yaron da Mahaifiyarsa, sun yi mamaki kwarai domin abubuwan da aka fada akansa.
Un Jāzeps un viņa māte brīnījās par to, ko viņš runāja.
34 Sai Siman ya albarkace su ya ce wa uwatasa Maryamu, “Ki ji da kyau, wannan yaro zai zama sanadiyar faduwa da tashin mutane dayawa a Isra'ila, kuma alama wadda ake kushen ta.
Un Sīmeans tos svētīja un sacīja uz Mariju, Viņa māti: “Redzi, Šis ir likts par krišanu un augšāmcelšanos daudz ļaudīm iekš Israēla, un par zīmi, kam top pretī runāts,
35 Kuma takobi zai tsaga zuciyar ki yadda tunanin mutane za ya bayyana.”
Un tev pašai caur dvēseli zobens spiedīsies, ka daudz siržu domas taps zināmas.”
36 Wata annabiya mai suna Annatu ta na nan wurin. Ita diyar Fanuyila ce daga kabilar Ashiru. Ta riga ta manyanta a shekaru sosai. Ta kasance da maigidanta shekaru bakwai bayan auren ta,
Un tur bija viena praviete, Anna, Fānuēļa meita, no Ašera cilts, tā bija ļoti veca, un pēc savas jumpravības bija dzīvojusi septiņus gadus ar savu vīru.
37 sannan ta yi zama gwambranci na shekaru tamanin da hudu. Ba ta taba barin haikali ba, tana ci gaba da yi wa Ubangiji sujada, dare da rana.
Un tā bija atraitne pie astoņdesmit četriem gadiem; tā neatstājās no Dieva nama, ar gavēšanu un lūgšanu Dievam kalpodama dienās, naktīs.
38 A dadai lokacin nan, ta hau zuwa wurinsu ta fara yi wa Allah godiya. Ta gaya wa dukan wadanda ke jiran fansar Urushalima.
Tā arīdzan tai pašā stundā piegāja un teica To Kungu, par To runādama uz visiem, kas uz pestīšanu Jeruzālemē gaidīja.
39 Da su ka gama komai da aka bukace su suyi bisa ga tafarkin shari'ar Ubangiji, sai suka koma Galili, zuwa birninsu, Nazarat.
Un visu pabeiguši pēc Tā Kunga bauslības, tie atkal griezās uz Galileju, uz savu pilsētu Nacareti.
40 Yaron kuma ya yi girma ya zama da karfi, yana karuwa da hikima, alherin Ubangiji kuma yana kansa.
Bet Tas Bērns auga un palika stiprs garā, pilns gudrības, un Dieva žēlastība bija pie Viņa.
41 Iyayensa sukan tafi Urushalima kowacce shekara domin idin ketarewa.
Un Viņa vecāki gāja ik gadus uz Jeruzālemi Lieldienas svētkos.
42 Da yana shekara goma sha biyu, suka sake haurawa daidai lokacin idin a al'adance.
Un kad Viņš bija divpadsmit gadus vecs, tad tie pēc svētku ieraduma gāja uz Jeruzālemi.
43 Bayan da sun cika dukan kwanakin idin, sun fara dawowa gida. Amma dan yaron Yesu ya jinkirta ya zauna a Urushalima, kuma iyayensa basu sani ba.
Un kad tās svētās dienas bija pagalam, tad tiem atkal uz mājām ejot Tas Bērns Jēzus palika Jeruzālemē, un Jāzeps un Viņa māte to nezināja.
44 Suna tsammani yana tare da sauran mutane da suke tafiya tare, sai suka yi tafiya na kwana daya. Suka fara neman sa a cikin danginsu da abokansu.
Bet tie domāja, ka Tas esot pie tiem ceļa biedriem; un vienas dienas gājumu nākuši, tie To meklēja pie radiem un pazīstamiem.
45 Da ba su gan shi ba, sai suka koma Urushalima suna cigiyar sa a can.
Un kad tie To neatrada, tad tie gāja atpakaļ uz Jeruzālemi, To meklēdami.
46 Ya zama bayan kwanaki uku, su ka same shi a cikin haikali, yana zama a tsakiyar malamai, yana sauraron su yana kuma yi masu tambayoyi.
Un notikās, pēc trim dienām tie Viņu atrada baznīcā sēžam starp tiem mācītājiem, tos dzirdot un tos jautājot.
47 Dukan wadanda suka ji shi suna ta mamakin fahimtar sa da amsoshin sa.
Un visi, kas Viņu dzirdēja, iztrūkušies brīnījās par Viņa saprašanu un Viņa atbildēšanu.
48 Da suka gan shi, suka yi mamaki kwarai. Mahaifiyarsa ta ce masa, “Da na, don me ka yi mana haka? Ka ji, mahaifinka da ni muna ta neman ka rai a bace.”
Un Viņu ieraudzījuši, tie pārbijās; un Viņa māte uz To sacīja: mans dēls, kāpēc Tu mums tā esi darījis? Redzi, Tavs tēvs un es, mēs Tevi ar sāpēm esam meklējuši.
49 Ya ce masu, “Don me kuke nema na? Ba ku sani cewa dole in kasance a gidan Ubana ba?”
Un Viņš uz tiem sacīja: “Kam jūs Mani esat meklējuši? Vai nezinājāt, ka Man iekš Mana Tēva lietām jādarbojas?”
50 Amma ba su gane abin da yake nufi da kalmomin nan ba.
Bet tie to vārdu neizprata, ko Viņš uz tiem sacīja.
51 Sa'annan ya koma gida tare da su zuwa Nazarat yana kuma masu biyayya. Mahaifiayarsa kuma ta ajiye dukan wadannan abubuwa a zuciyarta tana yin tunani akansu.
Un Viņš nogāja tiem līdz un nāca uz Nacareti un bija tiem paklausīgs. Bet Viņa māte visus šos vārdus paturēja savā sirdī.
52 Amma Yesu ya ci gaba da hikima da girma, ya kuma karu da tagomashi wurin Allah da mutane.
Un Jēzus pieņēmās gudrībā, augumā un piemīlībā pie Dieva un cilvēkiem.

< Luka 2 >