< Luka 19 >

1 Yesu ya shiga Yariko ya na wucewa cikinta.
И вшед прохождаше Иерихон.
2 Sai ga wani mutum a wurin mai suna Zakka. Shugaba ne na masu karban haraji, kuma mai arziki ne.
И се, муж нарицаемый Закхей, и сей бе старей мытарем, и той бе богат:
3 Yana kokarin ya ga ko wanene Yesu, amma bai iya gani ba sabo da yawan jama'a, domin shi gajere ne.
и искаше видети Иисуса, кто есть, и не можаше от народа, яко возрастом мал бе:
4 Sai ya ruga gaba ya hau itacen baure domin ya gan shi, saboda Yesu zai wuce ta wannan hanya.
и предитек, возлезе на ягодичину, да видит, яко хотяше мимо ея проити.
5 Sa'adda Yesu ya zo wurin, ya kalli sama sai ya ce masa, “Zakka, ka sauko da sauri, domin yau dole in sauka a gidanka.”
И яко прииде на место, воззрев Иисус виде его и рече к нему: Закхее, потщався слези: днесь бо в дому твоем подобает Ми быти.
6 Sai ya sauko da sauri, ya karbe shi da farin ciki.
И потщався слезе и прият Его радуяся.
7 Sa'adda dukansu suka ga wannan, sai suka yi gunaguni, cewa, “Ya ziyarci mutum mai zunubi.”
И видевше вси роптаху, глаголюще, яко ко грешну мужу вниде витати.
8 Zakka ya tsaya ya ce wa Ubangiji, “Duba, Ubangiji, zan ba matalauta rabin arzikina, idan kuma na cuci wani a kome, zan mai da adadinsa sau hudu.”
Став же Закхей рече ко Господу: се, пол имения моего, Господи, дам нищым: и аще кого чим обидех, возвращу четверицею.
9 Yesu ya ce masa, “Yau ceto ya shigo wannan gida, domin shi ma dan Ibrahim ne.
Рече же к нему Иисус, яко днесь спасение дому сему бысть, зане и сей сын Авраамль есть:
10 Gama Dan Mutum ya zo ne domin ya nemi, ya kuma ceci batattun mutane.”
прииде бо Сын Человечь взыскати и спасти погибшаго.
11 Da suka ji wadannan abubuwan, ya cigaba da magana, sannan ya fada masu wani misali, domin yana kusa da Urushalima, sai suka yi tsamani mulkin Allah za ya bayyana nan da nan.
Слышащым же им сия, приложь рече притчу, зане близ Ему быти Иерусалима, и мняху, яко абие Царство Божие хощет явитися.
12 Sai ya ce, “Akwai wani mutum mai sarauta wanda ya tafi wata kasa mai nisa domin ya karba wa kansa mulki sa'annan ya dawo.
Рече убо: человек некий добра рода иде на страну далече прияти себе царство и возвратитися:
13 Sai ya kira bayinsa guda goma, ya ba su fam goma, sai ya ce masu, 'Ku yi kasuwanci da wannan har sai na dawo.'
призвав же десять раб своих, даде им десять мнас и рече к ним: куплю дейте, дондеже прииду.
14 Amma mutanensa suka ki shi sai suka aiki jakadu bayansa, cewa, 'Ba za mu yarda wannan mutum ya yi mulki a kanmu ba.'
И граждане его ненавидяху его и послаша послы вслед его, глаголюще: не хощем сему, да царствует над нами.
15 Anan nan sa'adda ya koma kuma, bayan da ya sami mulkin, sai ya ba da umarni a kira masa bayin da ya basu kudi, domin ya san ribar da suka samu wajen kasuwancin da suka yi.
И бысть егда возвратися приим царство, рече пригласити рабы тыя, имже даде сребро, да увесть, какову куплю суть сотворили.
16 Na farkon ya zo wurinsa, cewa, 'Ubangiji, fam nan na ka ya yi riban fam goma.'
Прииде же первый, глаголя: господи, мнас твоя придела десять мнас.
17 Masaraucin ya ce masa, 'Madalla, bawan kirki. Domin ka yi aminci a karamin abu, za a baka iko kan birane goma.'
И рече ему: благо, рабе добрый: яко о мале верен был еси, буди область имея над десятию градов.
18 Na biyun ya zo, yana cewa, 'Fam na ka, Ubangiji, ya yi ribar fam biyar.'
И прииде вторый, глаголя: господи, мнас твоя сотвори пять мнас.
19 Sai masarauncin yace masa, 'Ka dauki mulkin birane biyar.'
Рече же и тому: и ты буди над пятию градов.
20 Wani kuma ya zo, yana cewa, 'Ubangiji, ga fam naka da na ajjiye shi da kyau cikin kaya,
И другий прииде, глаголя: господи, се, мнас твоя, юже имех положену во убрусе:
21 gama na ji tsoronka, domin kai mutum mai tsanani ne. Kana daukar abu da baka ajiye ba, kana kuma girbin abin da ba ka shuka ba.'
бояхся бо тебе, яко человек яр еси, вземлеши, егоже не положил еси, и жнеши, егоже не сеял еси.
22 Masarauncin ya ce masa, 'Da kalmominka zan shari'antaka, kai mugun bawa. Ka sani cewa ni mutum mai tsanani ne, ina daukan abinda ban ajiye ba, ina kuma girbin abinda ban shuka ba.
Глагола же ему: от уст твоих сужду ти, лукавый рабе: ведел еси, яко аз человек яр есмь, вземлю, егоже не положих, и жну, егоже не сеях:
23 To don me ba ka kai kudi na wurin masu banki ba, saboda bayan da na dawo zan karbe shi da riba?'
и почто не вдал еси моего сребра купцем, и аз пришед с лихвою истязал бых е?
24 Masaraucin ya ce wa wadanda suke a tsaye a wurin, 'Ku karba fam da ke a wurinsa, ku ba mai fam goman nan.'
И предстоящым рече: возмите от него мнас и дадите имущему десять мнас.
25 Suka ce masa, 'Ubangiji, yana da fam goma.'
И реша ему: господи, имать десять мнас.
26 'Ina ce maku, duk wanda yake da abu za a kara masa, amma wadda bai da shi, za a karba sauran da ke wurinsa.
Глаголю бо вам, яко всякому имущему дастся: а от неимущаго, и еже имать, отимется от него:
27 Amma wadannan abokan gabana, wadanda ba sa so in yi mulki bisansu, a kawo su nan a kashe su a gaba na.'
обаче враги моя оны, иже не восхотеша мене, да царь бых был над ними, приведите семо и изсецыте предо мною.
28 Da ya fadi wadannan abubuwan, sai ya yi gaba, yana tafiya zuwa Urushalima.
И сия рек, идяше преди, восходя во Иерусалим.
29 Ananan sa'adda ya zo kusa da Baitfaji da Baitanya, a kan tudu da a ke kira Zaitun, sai ya aiki almajiransa guda biyu, cewa,
И бысть яко приближися в Вифсфагию и Вифанию, к горе нарицаемей Елеон, посла два ученик Своих,
30 cewa, “Ku tafi cikin kauye da ke gabanku. Sa'adda ku ka shiga, za ku same dan aholaki da ba a taba hawansa ba. Ku kwance sai ku kawo mani shi.
глаголя: идита в прямную весь: (и) в нюже входяща обрящета жребя привязано, на неже никтоже николиже от человек вседе: отрешша е приведита:
31 Idan wani ya tambaye ku, 'Don me ku ke kwance shi?' Ku ce, 'Ubangiji ne ke bukatarsa.”
и аще кто вы вопрошает: почто отрешаета? Сице рцыта ему, яко Господь его требует.
32 Wadanda aka aike su suka je sun sami aholakin kamar yadda Yesu ya gaya masu.
Шедша же посланная обретоста, якоже рече има.
33 Sa'adda suna kwance aholakin, sai masu shi suka ce masu, “Don me ku ke kwance aholakin?”
Отрешающема же има жребя, рекоша господие его к нима: что отрешаета жребя?
34 Suka ce, “Ubangiji yana bukatar sa.”
Она же рекоста, яко Господь его требует.
35 Suka kawo wa Yesu, suka shimfida tufafinsu akan aholakin sai suka dora Yesu akansa.
И приведоста е ко Иисусови: и возвергше ризы своя на жребя, всадиша Иисуса.
36 Da yana cikin tafiya, suka shimfida tufafinsu akan hanya.
Идущу же Ему, постилаху ризы своя по пути.
37 Da ya yi kusa da gangaren tudun Zaitun, sai dukan taron almajiransa suka fara yin murna suna kuma yabon Allah da murya mai karfi domin dukan ayukan al'ajibi da suka gani,
Приближающужеся Ему уже (абие) к низхождению горе Елеонстей, начаша все множество ученик радующеся хвалити Бога гласом велиим о всех силах, яже видеша,
38 cewa, “Albarka ta tabbata ga sarki da ke zuwa cikin sunan Uba! Salama a sama da daraja mafi daukaka kuma!”
глаголюще: благословен грядый Царь во имя Господне: мир на небеси и слава в вышних.
39 Wadansu Farisawa daga cikin taron jama'a suka ce masa, “Malam, ka tsauta wa almajiranka.”
И нецыи фарисее от народа реша к Нему: Учителю, запрети учеником Твоим.
40 Yesu ya amsa ya ce, “Ina gaya maku gaskiya, in wadannan sun yi shiru, duwatsu za su yi shewa.”
И отвещав рече им: глаголю вам, яко, аще сии умолчат, камение возопиет.
41 Sa'adda Yesu yana kusatowa, sai ya yi kuka akan birnin,
И яко приближися, видев град, плакася о нем,
42 cewa, “Da kun san wannan rana, ko ku ma, abubuwan da ke kawo maku salama! Amma yanzu an boye su daga idanunku.
глаголя: яко аще бы разумел и ты, в день сей твой, еже к смирению твоему: ныне же скрыся от очию твоею:
43 Gama rana zata ta zo a gareki, da makiyan ki zasu gina ganuwa a kewaye da ke, su kuma fada maki daga kowace gefe.
яко приидут дние на тя, и обложат врази твои острог о тебе, и обыдут тя, и оымут тя отвсюду,
44 Za su sare ki kasa tare da 'ya'yanki. Ba za su bar wani dutse akan dan'uwansa ba, domin ba ki lura da lokacin da Allah ya na kokarin ceton ki ba.”
и разбиют тя и чада твоя в тебе, и не оставят камень на камени в тебе: понеже не разумел еси времене посещения твоего.
45 Yesu ya shiga Haikalin sai ya fara korar masu sayarwa,
И вшед в церковь, начат изгонити продающыя в ней и купующыя,
46 ya na ce masu, “A rubuce yake, 'Gida na zai zama wurin addu'a,' amma kun mayar da shi kogon mafasa.”
глаголя им: писано есть: дом Мой дом молитвы есть: вы же сотвористе его пещеру разбойником.
47 Yesu yana nan yana koyarwa kowace rana a cikin haikali. Amma manyan firistoci da marubuta da shugabanin jama'a suna so su kashe shi,
И бе учя по вся дни в церкви. Архиерее же и книжницы искаху Его погубити, и старейшины людем:
48 amma ba su sami hanyar yin wannan ba, domin mutane suna sauraron sa sosai.
и не обретаху, что бы сотворили Ему: людие бо вси держахуся Его, послушающе Его.

< Luka 19 >