< Luka 19 >

1 Yesu ya shiga Yariko ya na wucewa cikinta.
پس وارد اریحا شده، از آنجا می گذشت.۱
2 Sai ga wani mutum a wurin mai suna Zakka. Shugaba ne na masu karban haraji, kuma mai arziki ne.
که ناگاه شخصی زکی نام که رئیس باجگیران و دولتمند بود،۲
3 Yana kokarin ya ga ko wanene Yesu, amma bai iya gani ba sabo da yawan jama'a, domin shi gajere ne.
خواست عیسی را ببیند که کیست و از کثرت خلق نتوانست، زیرا کوتاه قد بود.۳
4 Sai ya ruga gaba ya hau itacen baure domin ya gan shi, saboda Yesu zai wuce ta wannan hanya.
پس پیش دویده بردرخت افراغی برآمد تا او را ببیند. چونکه اومی خواست از آن راه عبور کند.۴
5 Sa'adda Yesu ya zo wurin, ya kalli sama sai ya ce masa, “Zakka, ka sauko da sauri, domin yau dole in sauka a gidanka.”
و چون عیسی به آن مکان رسید، بالا نگریسته او را دید و گفت: «ای زکی بشتاب و به زیر بیا زیرا که باید امروز درخانه تو بمانم.»۵
6 Sai ya sauko da sauri, ya karbe shi da farin ciki.
پس به زودی پایین شده او را به خرمی پذیرفت.۶
7 Sa'adda dukansu suka ga wannan, sai suka yi gunaguni, cewa, “Ya ziyarci mutum mai zunubi.”
و همه چون این را دیدند، همهمه‌کنان می‌گفتند که در خانه شخصی گناهکار به میهمانی رفته است.۷
8 Zakka ya tsaya ya ce wa Ubangiji, “Duba, Ubangiji, zan ba matalauta rabin arzikina, idan kuma na cuci wani a kome, zan mai da adadinsa sau hudu.”
اما زکی برپا شده به خداوند گفت: «الحال‌ای خداوند نصف مایملک خود را به فقرامی دهم و اگر چیزی ناحق از کسی گرفته باشم، چهار برابر بدو رد می‌کنم.»۸
9 Yesu ya ce masa, “Yau ceto ya shigo wannan gida, domin shi ma dan Ibrahim ne.
عیسی به وی گفت: «امروز نجات در این خانه پیدا شد. زیرا که این شخص هم پسر ابراهیم است.۹
10 Gama Dan Mutum ya zo ne domin ya nemi, ya kuma ceci batattun mutane.”
زیرا که پسرانسان آمده است تا گمشده را بجوید و نجات‌بخشد.»۱۰
11 Da suka ji wadannan abubuwan, ya cigaba da magana, sannan ya fada masu wani misali, domin yana kusa da Urushalima, sai suka yi tsamani mulkin Allah za ya bayyana nan da nan.
و چون ایشان این را شنیدند او مثلی زیادکرده آورد چونکه نزدیک به اورشلیم بود و ایشان گمان می‌بردند که ملکوت خدا می‌باید در همان زمان ظهور کند.۱۱
12 Sai ya ce, “Akwai wani mutum mai sarauta wanda ya tafi wata kasa mai nisa domin ya karba wa kansa mulki sa'annan ya dawo.
پس گفت: «شخصی شریف به دیار بعید سفر کرد تا ملکی برای خود گرفته مراجعت کند.۱۲
13 Sai ya kira bayinsa guda goma, ya ba su fam goma, sai ya ce masu, 'Ku yi kasuwanci da wannan har sai na dawo.'
پس ده نفر از غلامان خود راطلبیده ده قنطار به ایشان سپرده فرمود، تجارت کنید تا بیایم.۱۳
14 Amma mutanensa suka ki shi sai suka aiki jakadu bayansa, cewa, 'Ba za mu yarda wannan mutum ya yi mulki a kanmu ba.'
اما اهل ولایت او، چونکه او رادشمن می‌داشتند ایلچیان در عقب او فرستاده گفتند، نمی خواهیم این شخص بر ما سلطنت کند.۱۴
15 Anan nan sa'adda ya koma kuma, bayan da ya sami mulkin, sai ya ba da umarni a kira masa bayin da ya basu kudi, domin ya san ribar da suka samu wajen kasuwancin da suka yi.
و چون ملک را گرفته مراجعت کرده بود، فرمود تا آن غلامانی را که به ایشان نقد سپرده بودحاضر کنند تا بفهمد هر یک چه سود نموده است.۱۵
16 Na farkon ya zo wurinsa, cewa, 'Ubangiji, fam nan na ka ya yi riban fam goma.'
پس اولی آمده گفت، ای آقا قنطار تو ده قنطار دیگر نفع آورده است.۱۶
17 Masaraucin ya ce masa, 'Madalla, bawan kirki. Domin ka yi aminci a karamin abu, za a baka iko kan birane goma.'
بدو گفت آفرین‌ای غلام نیکو. چونکه بر چیز کم امین بودی بر ده شهر حاکم شو.۱۷
18 Na biyun ya zo, yana cewa, 'Fam na ka, Ubangiji, ya yi ribar fam biyar.'
و دیگری آمده گفت، ای آقاقنطار تو پنج قنطار سود کرده است.۱۸
19 Sai masarauncin yace masa, 'Ka dauki mulkin birane biyar.'
او را نیزفرمود بر پنج شهر حکمرانی کن.۱۹
20 Wani kuma ya zo, yana cewa, 'Ubangiji, ga fam naka da na ajjiye shi da kyau cikin kaya,
و سومی آمده گفت، ای آقا اینک قنطار تو موجود است، آن را در پارچه‌ای نگاه داشته‌ام.۲۰
21 gama na ji tsoronka, domin kai mutum mai tsanani ne. Kana daukar abu da baka ajiye ba, kana kuma girbin abin da ba ka shuka ba.'
زیرا که از توترسیدم چونکه مرد تندخویی هستی. آنچه نگذارده‌ای، برمی داری و از آنچه نکاشته‌ای درومی کنی.۲۱
22 Masarauncin ya ce masa, 'Da kalmominka zan shari'antaka, kai mugun bawa. Ka sani cewa ni mutum mai tsanani ne, ina daukan abinda ban ajiye ba, ina kuma girbin abinda ban shuka ba.
به وی گفت، از زبان خودت بر توفتوی می‌دهم، ای غلام شریر. دانسته‌ای که من مرد تندخویی هستم که برمیدارم آنچه رانگذاشته‌ام و درو می‌کنم آنچه را نپاشیده‌ام.۲۲
23 To don me ba ka kai kudi na wurin masu banki ba, saboda bayan da na dawo zan karbe shi da riba?'
پس برای چه نقد مرا نزد صرافان نگذاردی تاچون آیم آن را با سود دریافت کنم؟۲۳
24 Masaraucin ya ce wa wadanda suke a tsaye a wurin, 'Ku karba fam da ke a wurinsa, ku ba mai fam goman nan.'
پس به حاضرین فرمود قنطار را از این شخص بگیرید وبه صاحب ده قنطار بدهید.۲۴
25 Suka ce masa, 'Ubangiji, yana da fam goma.'
به او گفتند‌ای خداوند، وی ده قنطار دارد.۲۵
26 'Ina ce maku, duk wanda yake da abu za a kara masa, amma wadda bai da shi, za a karba sauran da ke wurinsa.
زیرا به شمامی گویم به هر‌که دارد داده شود و هر‌که نداردآنچه دارد نیز از او گرفته خواهد شد.۲۶
27 Amma wadannan abokan gabana, wadanda ba sa so in yi mulki bisansu, a kawo su nan a kashe su a gaba na.'
اما آن دشمنان من که نخواستند من بر ایشان حکمرانی نمایم، در اینجا حاضر ساخته پیش من به قتل رسانید.»۲۷
28 Da ya fadi wadannan abubuwan, sai ya yi gaba, yana tafiya zuwa Urushalima.
و چون این را گفت، پیش رفته متوجه اورشلیم گردید.۲۸
29 Ananan sa'adda ya zo kusa da Baitfaji da Baitanya, a kan tudu da a ke kira Zaitun, sai ya aiki almajiransa guda biyu, cewa,
و چون نزدیک بیت‌فاجی وبیت عنیا بر کوه مسمی به زیتون رسید، دو نفر ازشاگردان خود را فرستاده،۲۹
30 cewa, “Ku tafi cikin kauye da ke gabanku. Sa'adda ku ka shiga, za ku same dan aholaki da ba a taba hawansa ba. Ku kwance sai ku kawo mani shi.
گفت: «به آن قریه‌ای که پیش روی شما است بروید و چون داخل آن شدید، کره الاغی بسته خواهید یافت که هیچ‌کس بر آن هرگز سوار نشده. آن را باز کرده بیاورید.۳۰
31 Idan wani ya tambaye ku, 'Don me ku ke kwance shi?' Ku ce, 'Ubangiji ne ke bukatarsa.”
و اگر کسی به شما گوید، چرا این راباز می‌کنید، به وی گویید خداوند او را لازم دارد.»۳۱
32 Wadanda aka aike su suka je sun sami aholakin kamar yadda Yesu ya gaya masu.
پس فرستادگان رفته آن چنانکه بدیشان گفته بود یافتند.۳۲
33 Sa'adda suna kwance aholakin, sai masu shi suka ce masu, “Don me ku ke kwance aholakin?”
و چون کره را باز می‌کردند، مالکانش به ایشان گفتند چرا کره را باز می‌کنید؟۳۳
34 Suka ce, “Ubangiji yana bukatar sa.”
گفتند خداوند او را لازم دارد.۳۴
35 Suka kawo wa Yesu, suka shimfida tufafinsu akan aholakin sai suka dora Yesu akansa.
پس او را به نزد عیسی آوردند و رخت خود را بر کره افکنده، عیسی را سوار کردند.۳۵
36 Da yana cikin tafiya, suka shimfida tufafinsu akan hanya.
و هنگامی که او می‌رفت جامه های خود را در راه می‌گستردند.۳۶
37 Da ya yi kusa da gangaren tudun Zaitun, sai dukan taron almajiransa suka fara yin murna suna kuma yabon Allah da murya mai karfi domin dukan ayukan al'ajibi da suka gani,
و چون نزدیک به‌سرازیری کوه زیتون رسید، تمامی شاگردانش شادی کرده، به آوازبلند خدا را حمد گفتن شروع کردند، به‌سبب همه قواتی که از او دیده بودند.۳۷
38 cewa, “Albarka ta tabbata ga sarki da ke zuwa cikin sunan Uba! Salama a sama da daraja mafi daukaka kuma!”
و می‌گفتند مبارک باد آن پادشاهی که می‌آید، به نام خداوند سلامتی در آسمان و جلال در اعلی علیین باد.۳۸
39 Wadansu Farisawa daga cikin taron jama'a suka ce masa, “Malam, ka tsauta wa almajiranka.”
آنگاه بعضی از فریسیان از آن میان بدو گفتند: «ای استاد شاگردان خود را نهیب نما.»۳۹
40 Yesu ya amsa ya ce, “Ina gaya maku gaskiya, in wadannan sun yi shiru, duwatsu za su yi shewa.”
او درجواب ایشان گفت: «به شما می‌گویم اگراینها ساکت شوند، هرآینه سنگها به صداآیند.»۴۰
41 Sa'adda Yesu yana kusatowa, sai ya yi kuka akan birnin,
و چون نزدیک شده، شهر را نظاره کرد برآن گریان گشته،۴۱
42 cewa, “Da kun san wannan rana, ko ku ma, abubuwan da ke kawo maku salama! Amma yanzu an boye su daga idanunku.
گفت: «اگر تو نیز می‌دانستی هم در این زمان خود آنچه باعث سلامتی تومیشد، لاکن الحال از چشمان تو پنهان گشته است.۴۲
43 Gama rana zata ta zo a gareki, da makiyan ki zasu gina ganuwa a kewaye da ke, su kuma fada maki daga kowace gefe.
زیرا ایامی بر تو می‌آید که دشمنانت گرد تو سنگرها سازند و تو را احاطه کرده از هرجانب محاصره خواهند نمود.۴۳
44 Za su sare ki kasa tare da 'ya'yanki. Ba za su bar wani dutse akan dan'uwansa ba, domin ba ki lura da lokacin da Allah ya na kokarin ceton ki ba.”
و تو را وفرزندانت را در اندرون تو بر خاک خواهند افکندو در تو سنگی بر سنگی نخواهند گذاشت زیرا که ایام تفقد خود را ندانستی.»۴۴
45 Yesu ya shiga Haikalin sai ya fara korar masu sayarwa,
و چون داخل هیکل شد، کسانی را که درآنجا خرید و فروش می‌کردند، به بیرون نمودن آغاز کرد.۴۵
46 ya na ce masu, “A rubuce yake, 'Gida na zai zama wurin addu'a,' amma kun mayar da shi kogon mafasa.”
و به ایشان گفت: «مکتوب است که خانه من خانه عبادت است لیکن شما آن را مغاره دزدان ساخته‌اید.»۴۶
47 Yesu yana nan yana koyarwa kowace rana a cikin haikali. Amma manyan firistoci da marubuta da shugabanin jama'a suna so su kashe shi,
و هر روز در هیکل تعلیم می‌داد، اما روسای کهنه و کاتبان و اکابر قوم قصدهلاک نمودن او می‌کردند.۴۷
48 amma ba su sami hanyar yin wannan ba, domin mutane suna sauraron sa sosai.
و نیافتند چه کنندزیرا که تمامی مردم بر او آویخته بودند که از اوبشنوند.۴۸

< Luka 19 >