< Luka 19 >

1 Yesu ya shiga Yariko ya na wucewa cikinta.
et ingressus perambulabat Hiericho
2 Sai ga wani mutum a wurin mai suna Zakka. Shugaba ne na masu karban haraji, kuma mai arziki ne.
et ecce vir nomine Zaccheus et hic erat princeps publicanorum et ipse dives
3 Yana kokarin ya ga ko wanene Yesu, amma bai iya gani ba sabo da yawan jama'a, domin shi gajere ne.
et quaerebat videre Iesum quis esset et non poterat prae turba quia statura pusillus erat
4 Sai ya ruga gaba ya hau itacen baure domin ya gan shi, saboda Yesu zai wuce ta wannan hanya.
et praecurrens ascendit in arborem sycomorum ut videret illum quia inde erat transiturus
5 Sa'adda Yesu ya zo wurin, ya kalli sama sai ya ce masa, “Zakka, ka sauko da sauri, domin yau dole in sauka a gidanka.”
et cum venisset ad locum suspiciens Iesus vidit illum et dixit ad eum Zacchee festinans descende quia hodie in domo tua oportet me manere
6 Sai ya sauko da sauri, ya karbe shi da farin ciki.
et festinans descendit et excepit illum gaudens
7 Sa'adda dukansu suka ga wannan, sai suka yi gunaguni, cewa, “Ya ziyarci mutum mai zunubi.”
et cum viderent omnes murmurabant dicentes quod ad hominem peccatorem devertisset
8 Zakka ya tsaya ya ce wa Ubangiji, “Duba, Ubangiji, zan ba matalauta rabin arzikina, idan kuma na cuci wani a kome, zan mai da adadinsa sau hudu.”
stans autem Zaccheus dixit ad Dominum ecce dimidium bonorum meorum Domine do pauperibus et si quid aliquem defraudavi reddo quadruplum
9 Yesu ya ce masa, “Yau ceto ya shigo wannan gida, domin shi ma dan Ibrahim ne.
ait Iesus ad eum quia hodie salus domui huic facta est eo quod et ipse filius sit Abrahae
10 Gama Dan Mutum ya zo ne domin ya nemi, ya kuma ceci batattun mutane.”
venit enim Filius hominis quaerere et salvum facere quod perierat
11 Da suka ji wadannan abubuwan, ya cigaba da magana, sannan ya fada masu wani misali, domin yana kusa da Urushalima, sai suka yi tsamani mulkin Allah za ya bayyana nan da nan.
haec illis audientibus adiciens dixit parabolam eo quod esset prope Hierusalem et quia existimarent quod confestim regnum Dei manifestaretur
12 Sai ya ce, “Akwai wani mutum mai sarauta wanda ya tafi wata kasa mai nisa domin ya karba wa kansa mulki sa'annan ya dawo.
dixit ergo homo quidam nobilis abiit in regionem longinquam accipere sibi regnum et reverti
13 Sai ya kira bayinsa guda goma, ya ba su fam goma, sai ya ce masu, 'Ku yi kasuwanci da wannan har sai na dawo.'
vocatis autem decem servis suis dedit illis decem mnas et ait ad illos negotiamini dum venio
14 Amma mutanensa suka ki shi sai suka aiki jakadu bayansa, cewa, 'Ba za mu yarda wannan mutum ya yi mulki a kanmu ba.'
cives autem eius oderant illum et miserunt legationem post illum dicentes nolumus hunc regnare super nos
15 Anan nan sa'adda ya koma kuma, bayan da ya sami mulkin, sai ya ba da umarni a kira masa bayin da ya basu kudi, domin ya san ribar da suka samu wajen kasuwancin da suka yi.
et factum est ut rediret accepto regno et iussit vocari servos quibus dedit pecuniam ut sciret quantum quisque negotiatus esset
16 Na farkon ya zo wurinsa, cewa, 'Ubangiji, fam nan na ka ya yi riban fam goma.'
venit autem primus dicens domine mna tua decem mnas adquisivit
17 Masaraucin ya ce masa, 'Madalla, bawan kirki. Domin ka yi aminci a karamin abu, za a baka iko kan birane goma.'
et ait illi euge bone serve quia in modico fidelis fuisti eris potestatem habens supra decem civitates
18 Na biyun ya zo, yana cewa, 'Fam na ka, Ubangiji, ya yi ribar fam biyar.'
et alter venit dicens domine mna tua fecit quinque mnas
19 Sai masarauncin yace masa, 'Ka dauki mulkin birane biyar.'
et huic ait et tu esto supra quinque civitates
20 Wani kuma ya zo, yana cewa, 'Ubangiji, ga fam naka da na ajjiye shi da kyau cikin kaya,
et alter venit dicens domine ecce mna tua quam habui repositam in sudario
21 gama na ji tsoronka, domin kai mutum mai tsanani ne. Kana daukar abu da baka ajiye ba, kana kuma girbin abin da ba ka shuka ba.'
timui enim te quia homo austeris es tollis quod non posuisti et metis quod non seminasti
22 Masarauncin ya ce masa, 'Da kalmominka zan shari'antaka, kai mugun bawa. Ka sani cewa ni mutum mai tsanani ne, ina daukan abinda ban ajiye ba, ina kuma girbin abinda ban shuka ba.
dicit ei de ore tuo te iudico serve nequam sciebas quod ego austeris homo sum tollens quod non posui et metens quod non seminavi
23 To don me ba ka kai kudi na wurin masu banki ba, saboda bayan da na dawo zan karbe shi da riba?'
et quare non dedisti pecuniam meam ad mensam et ego veniens cum usuris utique exegissem illud
24 Masaraucin ya ce wa wadanda suke a tsaye a wurin, 'Ku karba fam da ke a wurinsa, ku ba mai fam goman nan.'
et adstantibus dixit auferte ab illo mnam et date illi qui decem mnas habet
25 Suka ce masa, 'Ubangiji, yana da fam goma.'
et dixerunt ei domine habet decem mnas
26 'Ina ce maku, duk wanda yake da abu za a kara masa, amma wadda bai da shi, za a karba sauran da ke wurinsa.
dico autem vobis quia omni habenti dabitur ab eo autem qui non habet et quod habet auferetur ab eo
27 Amma wadannan abokan gabana, wadanda ba sa so in yi mulki bisansu, a kawo su nan a kashe su a gaba na.'
verumtamen inimicos meos illos qui noluerunt me regnare super se adducite huc et interficite ante me
28 Da ya fadi wadannan abubuwan, sai ya yi gaba, yana tafiya zuwa Urushalima.
et his dictis praecedebat ascendens in Hierosolyma
29 Ananan sa'adda ya zo kusa da Baitfaji da Baitanya, a kan tudu da a ke kira Zaitun, sai ya aiki almajiransa guda biyu, cewa,
et factum est cum adpropinquasset ad Bethfage et Bethania ad montem qui vocatur Oliveti misit duos discipulos suos
30 cewa, “Ku tafi cikin kauye da ke gabanku. Sa'adda ku ka shiga, za ku same dan aholaki da ba a taba hawansa ba. Ku kwance sai ku kawo mani shi.
dicens ite in castellum quod contra est in quod introeuntes invenietis pullum asinae alligatum cui nemo umquam hominum sedit solvite illum et adducite
31 Idan wani ya tambaye ku, 'Don me ku ke kwance shi?' Ku ce, 'Ubangiji ne ke bukatarsa.”
et si quis vos interrogaverit quare solvitis sic dicetis ei quia Dominus operam eius desiderat
32 Wadanda aka aike su suka je sun sami aholakin kamar yadda Yesu ya gaya masu.
abierunt autem qui missi erant et invenerunt sicut dixit illis stantem pullum
33 Sa'adda suna kwance aholakin, sai masu shi suka ce masu, “Don me ku ke kwance aholakin?”
solventibus autem illis pullum dixerunt domini eius ad illos quid solvitis pullum
34 Suka ce, “Ubangiji yana bukatar sa.”
at illi dixerunt quia Dominus eum necessarium habet
35 Suka kawo wa Yesu, suka shimfida tufafinsu akan aholakin sai suka dora Yesu akansa.
et duxerunt illum ad Iesum et iactantes vestimenta sua supra pullum inposuerunt Iesum
36 Da yana cikin tafiya, suka shimfida tufafinsu akan hanya.
eunte autem illo substernebant vestimenta sua in via
37 Da ya yi kusa da gangaren tudun Zaitun, sai dukan taron almajiransa suka fara yin murna suna kuma yabon Allah da murya mai karfi domin dukan ayukan al'ajibi da suka gani,
et cum adpropinquaret iam ad descensum montis Oliveti coeperunt omnes turbae discentium gaudentes laudare Deum voce magna super omnibus quas viderant virtutibus
38 cewa, “Albarka ta tabbata ga sarki da ke zuwa cikin sunan Uba! Salama a sama da daraja mafi daukaka kuma!”
dicentes benedictus qui venit rex in nomine Domini pax in caelo et gloria in excelsis
39 Wadansu Farisawa daga cikin taron jama'a suka ce masa, “Malam, ka tsauta wa almajiranka.”
et quidam Pharisaeorum de turbis dixerunt ad illum magister increpa discipulos tuos
40 Yesu ya amsa ya ce, “Ina gaya maku gaskiya, in wadannan sun yi shiru, duwatsu za su yi shewa.”
quibus ipse ait dico vobis quia si hii tacuerint lapides clamabunt
41 Sa'adda Yesu yana kusatowa, sai ya yi kuka akan birnin,
et ut adpropinquavit videns civitatem flevit super illam dicens
42 cewa, “Da kun san wannan rana, ko ku ma, abubuwan da ke kawo maku salama! Amma yanzu an boye su daga idanunku.
quia si cognovisses et tu et quidem in hac die tua quae ad pacem tibi nunc autem abscondita sunt ab oculis tuis
43 Gama rana zata ta zo a gareki, da makiyan ki zasu gina ganuwa a kewaye da ke, su kuma fada maki daga kowace gefe.
quia venient dies in te et circumdabunt te inimici tui vallo et circumdabunt te et coangustabunt te undique
44 Za su sare ki kasa tare da 'ya'yanki. Ba za su bar wani dutse akan dan'uwansa ba, domin ba ki lura da lokacin da Allah ya na kokarin ceton ki ba.”
ad terram prosternent te et filios qui in te sunt et non relinquent in te lapidem super lapidem eo quod non cognoveris tempus visitationis tuae
45 Yesu ya shiga Haikalin sai ya fara korar masu sayarwa,
et ingressus in templum coepit eicere vendentes in illo et ementes
46 ya na ce masu, “A rubuce yake, 'Gida na zai zama wurin addu'a,' amma kun mayar da shi kogon mafasa.”
dicens illis scriptum est quia domus mea domus orationis est vos autem fecistis illam speluncam latronum
47 Yesu yana nan yana koyarwa kowace rana a cikin haikali. Amma manyan firistoci da marubuta da shugabanin jama'a suna so su kashe shi,
et erat docens cotidie in templo principes autem sacerdotum et scribae et principes plebis quaerebant illum perdere
48 amma ba su sami hanyar yin wannan ba, domin mutane suna sauraron sa sosai.
et non inveniebant quid facerent illi omnis enim populus suspensus erat audiens illum

< Luka 19 >