< Luka 19 >

1 Yesu ya shiga Yariko ya na wucewa cikinta.
And [Jesus] entered and passed through Jericho.
2 Sai ga wani mutum a wurin mai suna Zakka. Shugaba ne na masu karban haraji, kuma mai arziki ne.
And, behold, [there was] a man named Zacchæus, which was the chief among the publicans, and he was rich.
3 Yana kokarin ya ga ko wanene Yesu, amma bai iya gani ba sabo da yawan jama'a, domin shi gajere ne.
And he sought to see Jesus who he was; and could not for the press, because he was little of stature.
4 Sai ya ruga gaba ya hau itacen baure domin ya gan shi, saboda Yesu zai wuce ta wannan hanya.
And he ran before, and climbed up into a sycomore tree to see him: for he was to pass that [way].
5 Sa'adda Yesu ya zo wurin, ya kalli sama sai ya ce masa, “Zakka, ka sauko da sauri, domin yau dole in sauka a gidanka.”
And when Jesus came to the place, he looked up, and saw him, and said unto him, Zacchæus, make haste, and come down; for to day I must abide at thy house.
6 Sai ya sauko da sauri, ya karbe shi da farin ciki.
And he made haste, and came down, and received him joyfully.
7 Sa'adda dukansu suka ga wannan, sai suka yi gunaguni, cewa, “Ya ziyarci mutum mai zunubi.”
And when they saw [it], they all murmured, saying, That he was gone to be guest with a man that is a sinner.
8 Zakka ya tsaya ya ce wa Ubangiji, “Duba, Ubangiji, zan ba matalauta rabin arzikina, idan kuma na cuci wani a kome, zan mai da adadinsa sau hudu.”
And Zacchæus stood, and said unto the Lord; Behold, Lord, the half of my goods I give to the poor; and if I have taken any thing from any man by false accusation, I restore [him] fourfold.
9 Yesu ya ce masa, “Yau ceto ya shigo wannan gida, domin shi ma dan Ibrahim ne.
And Jesus said unto him, This day is salvation come to this house, forsomuch as he also is a son of Abraham.
10 Gama Dan Mutum ya zo ne domin ya nemi, ya kuma ceci batattun mutane.”
For the Son of man is come to seek and to save that which was lost.
11 Da suka ji wadannan abubuwan, ya cigaba da magana, sannan ya fada masu wani misali, domin yana kusa da Urushalima, sai suka yi tsamani mulkin Allah za ya bayyana nan da nan.
And as they heard these things, he added and spake a parable, because he was nigh to Jerusalem, and because they thought that the kingdom of God should immediately appear.
12 Sai ya ce, “Akwai wani mutum mai sarauta wanda ya tafi wata kasa mai nisa domin ya karba wa kansa mulki sa'annan ya dawo.
He said therefore, A certain nobleman went into a far country to receive for himself a kingdom, and to return.
13 Sai ya kira bayinsa guda goma, ya ba su fam goma, sai ya ce masu, 'Ku yi kasuwanci da wannan har sai na dawo.'
And he called his ten servants, and delivered them ten pounds, and said unto them, Occupy till I come.
14 Amma mutanensa suka ki shi sai suka aiki jakadu bayansa, cewa, 'Ba za mu yarda wannan mutum ya yi mulki a kanmu ba.'
But his citizens hated him, and sent a message after him, saying, We will not have this [man] to reign over us.
15 Anan nan sa'adda ya koma kuma, bayan da ya sami mulkin, sai ya ba da umarni a kira masa bayin da ya basu kudi, domin ya san ribar da suka samu wajen kasuwancin da suka yi.
And it came to pass, that when he was returned, having received the kingdom, then he commanded these servants to be called unto him, to whom he had given the money, that he might know how much every man had gained by trading.
16 Na farkon ya zo wurinsa, cewa, 'Ubangiji, fam nan na ka ya yi riban fam goma.'
Then came the first, saying, Lord, thy pound hath gained ten pounds.
17 Masaraucin ya ce masa, 'Madalla, bawan kirki. Domin ka yi aminci a karamin abu, za a baka iko kan birane goma.'
And he said unto him, Well, thou good servant: because thou hast been faithful in a very little, have thou authority over ten cities.
18 Na biyun ya zo, yana cewa, 'Fam na ka, Ubangiji, ya yi ribar fam biyar.'
And the second came, saying, Lord, thy pound hath gained five pounds.
19 Sai masarauncin yace masa, 'Ka dauki mulkin birane biyar.'
And he said likewise to him, Be thou also over five cities.
20 Wani kuma ya zo, yana cewa, 'Ubangiji, ga fam naka da na ajjiye shi da kyau cikin kaya,
And another came, saying, Lord, behold, [here is] thy pound, which I have kept laid up in a napkin:
21 gama na ji tsoronka, domin kai mutum mai tsanani ne. Kana daukar abu da baka ajiye ba, kana kuma girbin abin da ba ka shuka ba.'
For I feared thee, because thou art an austere man: thou takest up that thou layedst not down, and reapest that thou didst not sow.
22 Masarauncin ya ce masa, 'Da kalmominka zan shari'antaka, kai mugun bawa. Ka sani cewa ni mutum mai tsanani ne, ina daukan abinda ban ajiye ba, ina kuma girbin abinda ban shuka ba.
And he saith unto him, Out of thine own mouth will I judge thee, [thou] wicked servant. Thou knewest that I was an austere man, taking up that I laid not down, and reaping that I did not sow:
23 To don me ba ka kai kudi na wurin masu banki ba, saboda bayan da na dawo zan karbe shi da riba?'
Wherefore then gavest not thou my money into the bank, that at my coming I might have required mine own with usury?
24 Masaraucin ya ce wa wadanda suke a tsaye a wurin, 'Ku karba fam da ke a wurinsa, ku ba mai fam goman nan.'
And he said unto them that stood by, Take from him the pound, and give [it] to him that hath ten pounds.
25 Suka ce masa, 'Ubangiji, yana da fam goma.'
(And they said unto him, Lord, he hath ten pounds.)
26 'Ina ce maku, duk wanda yake da abu za a kara masa, amma wadda bai da shi, za a karba sauran da ke wurinsa.
For I say unto you, That unto every one which hath shall be given; and from him that hath not, even that he hath shall be taken away from him.
27 Amma wadannan abokan gabana, wadanda ba sa so in yi mulki bisansu, a kawo su nan a kashe su a gaba na.'
But those mine enemies, which would not that I should reign over them, bring hither, and slay [them] before me.
28 Da ya fadi wadannan abubuwan, sai ya yi gaba, yana tafiya zuwa Urushalima.
And when he had thus spoken, he went before, ascending up to Jerusalem.
29 Ananan sa'adda ya zo kusa da Baitfaji da Baitanya, a kan tudu da a ke kira Zaitun, sai ya aiki almajiransa guda biyu, cewa,
And it came to pass, when he was come nigh to Bethphage and Bethany, at the mount called [the mount] of Olives, he sent two of his disciples,
30 cewa, “Ku tafi cikin kauye da ke gabanku. Sa'adda ku ka shiga, za ku same dan aholaki da ba a taba hawansa ba. Ku kwance sai ku kawo mani shi.
Saying, Go ye into the village over against [you]; in the which at your entering ye shall find a colt tied, whereon yet never man sat: loose him, and bring [him hither].
31 Idan wani ya tambaye ku, 'Don me ku ke kwance shi?' Ku ce, 'Ubangiji ne ke bukatarsa.”
And if any man ask you, Why do ye loose [him]? thus shall ye say unto him, Because the Lord hath need of him.
32 Wadanda aka aike su suka je sun sami aholakin kamar yadda Yesu ya gaya masu.
And they that were sent went their way, and found even as he had said unto them.
33 Sa'adda suna kwance aholakin, sai masu shi suka ce masu, “Don me ku ke kwance aholakin?”
And as they were loosing the colt, the owners thereof said unto them, Why loose ye the colt?
34 Suka ce, “Ubangiji yana bukatar sa.”
And they said, The Lord hath need of him.
35 Suka kawo wa Yesu, suka shimfida tufafinsu akan aholakin sai suka dora Yesu akansa.
And they brought him to Jesus: and they cast their garments upon the colt, and they set Jesus thereon.
36 Da yana cikin tafiya, suka shimfida tufafinsu akan hanya.
And as he went, they spread their clothes in the way.
37 Da ya yi kusa da gangaren tudun Zaitun, sai dukan taron almajiransa suka fara yin murna suna kuma yabon Allah da murya mai karfi domin dukan ayukan al'ajibi da suka gani,
And when he was come nigh, even now at the descent of the mount of Olives, the whole multitude of the disciples began to rejoice and praise God with a loud voice for all the mighty works that they had seen;
38 cewa, “Albarka ta tabbata ga sarki da ke zuwa cikin sunan Uba! Salama a sama da daraja mafi daukaka kuma!”
Saying, Blessed [be] the King that cometh in the name of the Lord: peace in heaven, and glory in the highest.
39 Wadansu Farisawa daga cikin taron jama'a suka ce masa, “Malam, ka tsauta wa almajiranka.”
And some of the Pharisees from among the multitude said unto him, Master, rebuke thy disciples.
40 Yesu ya amsa ya ce, “Ina gaya maku gaskiya, in wadannan sun yi shiru, duwatsu za su yi shewa.”
And he answered and said unto them, I tell you that, if these should hold their peace, the stones would immediately cry out.
41 Sa'adda Yesu yana kusatowa, sai ya yi kuka akan birnin,
And when he was come near, he beheld the city, and wept over it,
42 cewa, “Da kun san wannan rana, ko ku ma, abubuwan da ke kawo maku salama! Amma yanzu an boye su daga idanunku.
Saying, If thou hadst known, even thou, at least in this thy day, the things [which belong] unto thy peace! but now they are hid from thine eyes.
43 Gama rana zata ta zo a gareki, da makiyan ki zasu gina ganuwa a kewaye da ke, su kuma fada maki daga kowace gefe.
For the days shall come upon thee, that thine enemies shall cast a trench about thee, and compass thee round, and keep thee in on every side,
44 Za su sare ki kasa tare da 'ya'yanki. Ba za su bar wani dutse akan dan'uwansa ba, domin ba ki lura da lokacin da Allah ya na kokarin ceton ki ba.”
And shall lay thee even with the ground, and thy children within thee; and they shall not leave in thee one stone upon another; because thou knewest not the time of thy visitation.
45 Yesu ya shiga Haikalin sai ya fara korar masu sayarwa,
And he went into the temple, and began to cast out them that sold therein, and them that bought;
46 ya na ce masu, “A rubuce yake, 'Gida na zai zama wurin addu'a,' amma kun mayar da shi kogon mafasa.”
Saying unto them, It is written, My house is the house of prayer: but ye have made it a den of thieves.
47 Yesu yana nan yana koyarwa kowace rana a cikin haikali. Amma manyan firistoci da marubuta da shugabanin jama'a suna so su kashe shi,
And he taught daily in the temple. But the chief priests and the scribes and the chief of the people sought to destroy him,
48 amma ba su sami hanyar yin wannan ba, domin mutane suna sauraron sa sosai.
And could not find what they might do: for all the people were very attentive to hear him.

< Luka 19 >