< Luka 19 >

1 Yesu ya shiga Yariko ya na wucewa cikinta.
Now when Iesus entred and passed through Iericho,
2 Sai ga wani mutum a wurin mai suna Zakka. Shugaba ne na masu karban haraji, kuma mai arziki ne.
Beholde, there was a man named Zaccheus, which was the chiefe receiuer of the tribute, and he was riche.
3 Yana kokarin ya ga ko wanene Yesu, amma bai iya gani ba sabo da yawan jama'a, domin shi gajere ne.
And he sought to see Iesus, who hee should be, and coulde not for the preasse, because he was of a lowe stature.
4 Sai ya ruga gaba ya hau itacen baure domin ya gan shi, saboda Yesu zai wuce ta wannan hanya.
Wherefore he ranne before, and climed vp into a wilde figge tree, that he might see him: for he should come that way.
5 Sa'adda Yesu ya zo wurin, ya kalli sama sai ya ce masa, “Zakka, ka sauko da sauri, domin yau dole in sauka a gidanka.”
And when Iesus came to the place, he looked vp, and saw him, and said vnto him, Zaccheus, come downe at once: for to day I must abide at thine house.
6 Sai ya sauko da sauri, ya karbe shi da farin ciki.
Then he came downe hastily, and receiued him ioyfully.
7 Sa'adda dukansu suka ga wannan, sai suka yi gunaguni, cewa, “Ya ziyarci mutum mai zunubi.”
And when all they sawe it, they murmured, saying, that hee was gone in to lodge with a sinfull man.
8 Zakka ya tsaya ya ce wa Ubangiji, “Duba, Ubangiji, zan ba matalauta rabin arzikina, idan kuma na cuci wani a kome, zan mai da adadinsa sau hudu.”
And Zaccheus stood forth, and said vnto the Lord, Beholde, Lord, the halfe of my goods I giue to the poore: and if I haue taken from any man by forged cauillation, I restore him foure folde.
9 Yesu ya ce masa, “Yau ceto ya shigo wannan gida, domin shi ma dan Ibrahim ne.
Then Iesus said to him, This day is saluation come vnto this house, forasmuch as hee is also become the sonne of Abraham.
10 Gama Dan Mutum ya zo ne domin ya nemi, ya kuma ceci batattun mutane.”
For the Sonne of man is come to seeke, and to saue that which was lost.
11 Da suka ji wadannan abubuwan, ya cigaba da magana, sannan ya fada masu wani misali, domin yana kusa da Urushalima, sai suka yi tsamani mulkin Allah za ya bayyana nan da nan.
And whiles they heard these thinges, hee continued and spake a parable, because hee was neere to Hierusalem, and because also they thought that the kingdom of God should shortly appeare.
12 Sai ya ce, “Akwai wani mutum mai sarauta wanda ya tafi wata kasa mai nisa domin ya karba wa kansa mulki sa'annan ya dawo.
He saide therefore, A certaine noble man went into a farre countrey, to receiue for himselfe a kingdome, and so to come againe.
13 Sai ya kira bayinsa guda goma, ya ba su fam goma, sai ya ce masu, 'Ku yi kasuwanci da wannan har sai na dawo.'
And he called his ten seruants, and deliuered them ten pieces of money, and sayd vnto them, Occupie till I come.
14 Amma mutanensa suka ki shi sai suka aiki jakadu bayansa, cewa, 'Ba za mu yarda wannan mutum ya yi mulki a kanmu ba.'
Nowe his citizens hated him, and sent an ambassage after him, saying, We will not haue this man to reigne ouer vs.
15 Anan nan sa'adda ya koma kuma, bayan da ya sami mulkin, sai ya ba da umarni a kira masa bayin da ya basu kudi, domin ya san ribar da suka samu wajen kasuwancin da suka yi.
And it came to passe, when hee was come againe, and had receiued his kingdome, that he commanded the seruants to be called to him, to whome he gaue his money, that he might knowe what euery man had gained.
16 Na farkon ya zo wurinsa, cewa, 'Ubangiji, fam nan na ka ya yi riban fam goma.'
Then came the first, saying, Lord, thy piece hath encreased ten pieces.
17 Masaraucin ya ce masa, 'Madalla, bawan kirki. Domin ka yi aminci a karamin abu, za a baka iko kan birane goma.'
And he sayd vnto him, Well, good seruant: because thou hast bene faithfull in a very litle thing, take thou authoritie ouer ten cities.
18 Na biyun ya zo, yana cewa, 'Fam na ka, Ubangiji, ya yi ribar fam biyar.'
And the second came, saying, Lord, thy piece hath encreased fiue pieces.
19 Sai masarauncin yace masa, 'Ka dauki mulkin birane biyar.'
And to the same he sayd, Be thou also ruler ouer fiue cities.
20 Wani kuma ya zo, yana cewa, 'Ubangiji, ga fam naka da na ajjiye shi da kyau cikin kaya,
So the other came, and sayd, Lord, beholde thy piece, which I haue laide vp in a napkin:
21 gama na ji tsoronka, domin kai mutum mai tsanani ne. Kana daukar abu da baka ajiye ba, kana kuma girbin abin da ba ka shuka ba.'
For I feared thee, because thou art a straight man: thou takest vp, that thou layedst not downe, and reapest that thou diddest not sowe.
22 Masarauncin ya ce masa, 'Da kalmominka zan shari'antaka, kai mugun bawa. Ka sani cewa ni mutum mai tsanani ne, ina daukan abinda ban ajiye ba, ina kuma girbin abinda ban shuka ba.
Then he sayde vnto him, Of thine owne mouth will I iudge thee, O euill seruant. Thou knewest that I am a straight man, taking vp that I layd not downe, and reaping that I did not sowe.
23 To don me ba ka kai kudi na wurin masu banki ba, saboda bayan da na dawo zan karbe shi da riba?'
Wherefore then gauest not thou my money into the banke, that at my coming I might haue required it with vantage?
24 Masaraucin ya ce wa wadanda suke a tsaye a wurin, 'Ku karba fam da ke a wurinsa, ku ba mai fam goman nan.'
And he sayd to them that stoode by, Take from him that piece, and giue it him that hath ten pieces.
25 Suka ce masa, 'Ubangiji, yana da fam goma.'
(And they sayd vnto him, Lord, hee hath ten pieces.)
26 'Ina ce maku, duk wanda yake da abu za a kara masa, amma wadda bai da shi, za a karba sauran da ke wurinsa.
For I say vnto you, that vnto all them that haue, it shalbe giuen: and from him that hath not, euen that he hath, shalbe taken from him.
27 Amma wadannan abokan gabana, wadanda ba sa so in yi mulki bisansu, a kawo su nan a kashe su a gaba na.'
Moreouer, those mine enemies, which would not that I should reigne ouer them, bring hither, and slay them before me.
28 Da ya fadi wadannan abubuwan, sai ya yi gaba, yana tafiya zuwa Urushalima.
And when he had thus spoken, he went forth before, ascending vp to Hierusalem.
29 Ananan sa'adda ya zo kusa da Baitfaji da Baitanya, a kan tudu da a ke kira Zaitun, sai ya aiki almajiransa guda biyu, cewa,
And it came to passe, when hee was come neere to Bethphage, and Bethania, besides the mount which is called the mount of Oliues, he sent two of his disciples,
30 cewa, “Ku tafi cikin kauye da ke gabanku. Sa'adda ku ka shiga, za ku same dan aholaki da ba a taba hawansa ba. Ku kwance sai ku kawo mani shi.
Saying, Goe ye to the towne which is before you, wherein, assoone as ye are come, ye shall finde a colte tied, whereon neuer man sate: loose him, and bring him hither.
31 Idan wani ya tambaye ku, 'Don me ku ke kwance shi?' Ku ce, 'Ubangiji ne ke bukatarsa.”
And if any man aske you, why ye loose him, thus shall ye say vnto him, Because the Lord hath neede of him.
32 Wadanda aka aike su suka je sun sami aholakin kamar yadda Yesu ya gaya masu.
So they that were sent, went their way, and found it as he had sayd vnto them.
33 Sa'adda suna kwance aholakin, sai masu shi suka ce masu, “Don me ku ke kwance aholakin?”
And as they were loosing the colte, the owners thereof sayd vnto them, Why loose ye the colte?
34 Suka ce, “Ubangiji yana bukatar sa.”
And they sayd, The Lord hath neede of him.
35 Suka kawo wa Yesu, suka shimfida tufafinsu akan aholakin sai suka dora Yesu akansa.
So they brought him to Iesus, and they cast their garments on the colte, and set Iesus thereon.
36 Da yana cikin tafiya, suka shimfida tufafinsu akan hanya.
And as he went, they spred their clothes in the way.
37 Da ya yi kusa da gangaren tudun Zaitun, sai dukan taron almajiransa suka fara yin murna suna kuma yabon Allah da murya mai karfi domin dukan ayukan al'ajibi da suka gani,
And when he was nowe come neere to the going downe of the mount of Oliues, the whole multitude of the disciples began to reioyce, and to prayse God with a loude voyce, for all the great workes that they had seene,
38 cewa, “Albarka ta tabbata ga sarki da ke zuwa cikin sunan Uba! Salama a sama da daraja mafi daukaka kuma!”
Saying, Blessed be the King that commeth in the Name of the Lord: peace in heauen, and glory in the highest places.
39 Wadansu Farisawa daga cikin taron jama'a suka ce masa, “Malam, ka tsauta wa almajiranka.”
Then some of the Pharises of the companie sayd vnto him, Master, rebuke thy disciples.
40 Yesu ya amsa ya ce, “Ina gaya maku gaskiya, in wadannan sun yi shiru, duwatsu za su yi shewa.”
But he answered, and sayd vnto them, I tell you, that if these should holde their peace, the stones would crie.
41 Sa'adda Yesu yana kusatowa, sai ya yi kuka akan birnin,
And when he was come neere, he behelde the Citie, and wept for it,
42 cewa, “Da kun san wannan rana, ko ku ma, abubuwan da ke kawo maku salama! Amma yanzu an boye su daga idanunku.
Saying, O if thou haddest euen knowen at the least in this thy day those things, which belong vnto thy peace! but nowe are they hid from thine eyes.
43 Gama rana zata ta zo a gareki, da makiyan ki zasu gina ganuwa a kewaye da ke, su kuma fada maki daga kowace gefe.
For the dayes shall come vpon thee, that thine enemies shall cast a trench about thee, and compasse thee round, and keepe thee in on euery side,
44 Za su sare ki kasa tare da 'ya'yanki. Ba za su bar wani dutse akan dan'uwansa ba, domin ba ki lura da lokacin da Allah ya na kokarin ceton ki ba.”
And shall make thee euen with ye ground, and thy children which are in thee, and they shall not leaue in thee a stone vpon a stone, because thou knewest not that season of thy visitation.
45 Yesu ya shiga Haikalin sai ya fara korar masu sayarwa,
He went also into the Temple, and began to cast out them that solde therein, and them that bought,
46 ya na ce masu, “A rubuce yake, 'Gida na zai zama wurin addu'a,' amma kun mayar da shi kogon mafasa.”
Saying vnto them, It is written, Mine house is the house of prayer, but ye haue made it a denne of theeues.
47 Yesu yana nan yana koyarwa kowace rana a cikin haikali. Amma manyan firistoci da marubuta da shugabanin jama'a suna so su kashe shi,
And he taught dayly in the Temple. And the hie Priests and the Scribes, and the chiefe of the people sought to destroy him.
48 amma ba su sami hanyar yin wannan ba, domin mutane suna sauraron sa sosai.
But they could not finde what they might doe to him: for all the people hanged vpon him when they heard him.

< Luka 19 >