< Luka 18 >

1 Ya kuma ba su wani misali cewa ya kamata kullum su yi addu'a kada kuma su karaya,
Sade han ock en liknelse till dem derom, att man skall alltid bedja, och icke förtröttas;
2 yace, “A wani gari an yi wani alkali mara tsoron Allah, kuma baya ganin darajan mutane.
Sägandes: En domare var uti en stad, den icke fruktade Gud, och ej heller hade försyn för några mennisko;
3 Akwai wata mace gwauruwa a wannan garin, wadda ta rika zuwa wurinsa, tana ce masa, 'Ka taimake ni yanda zan sami adalci a kan abokin gaba na.'
Så var i samma stad en enka; hon kom till honom, och sade: Hjelp mig ifrå min trätobroder.
4 An dade bai so ya taimaka mata, amma daga baya sai ya ce a ransa, 'ko da yake ba na tsoron Allah, ba na kuma darajanta mutane,
Och han ville icke till någon tid. Sedan sade han vid sig: Ändock jag icke fruktar Gud, ej heller hafver försyn för någon mennisko;
5 duk da haka saboda gwauruwar nan ta dame ni, zan taimake ta domin ta sami adalci, yadda ba za ta gajiyar da ni da zuwanta wurina ba.'”
Dock, fördenskull att denna enkan öfverfaller mig så svåra, måste jag fly henne rätt, att hon icke skall komma på det sista, och ropa på mig.
6 Sai Ubangiji ya ce, “Ku ji fa abin da alkalin nan marar gaskiya ya fada.
Och sade Herren: Hörer här, hvad den orätta domaren säger.
7 A yanzu Allah ba zai biya wa zababbunsa da suke yi masa kuka dare da rana hakkinsu ba? Zai yi jinkiri a wajen taimakonsu ne?
Skulle ock icke Gud hämnas sina utkorade, som ropa till honom dag och natt; skulle han hafva tålamod dermed?
8 Ina gaya maku, zai biya masu hakkin su da wuri. Amma sa'adda Dan Mutum ya zo, zai tarar da bangaskiya a duniya?”
Jag säger eder, att han skall hämnas dem snarliga. Dock likväl, då menniskones Son kommer, månn han skall finna tro på jordene?
9 Ya sake ba da misalin nan ga wadansu masu amincewa da kansu, wai su masu adalci ne, har suna raina sauran mutane,
Sade han ock till somliga, som tröste på sig sjelfva, att de voro rättfärdige, och försmådde andra, denna liknelsen:
10 “Wadansu mutane biyu suka shiga haikali domin yin addu'a - daya Bafarise, dayan kuma mai karbar haraji ne.
Två män gingo upp i templet till att bedja; den ene en Pharisee, och den andre en Publican.
11 Sai Bafarisen ya mike, ya yi addu'a a kan wadannan abubuwa game da kansa, 'Allah, na gode maka, da cewa ni ba kamar sauran mutane dake mazambata ba, ko marasa adalci, ko mazinata, ko kamar wannan mai karbar harajin.
Phariseen stod och bad så vid sig sjelf: Jag tackar dig Gud, att jag är icke såsom andra menniskor, röfvare, orättfärdige, horkarlar, eller ock såsom denne Publicanen.
12 Duk mako ina azumi sau biyu. Nakan bayar da zakkar dukan abin da na samu.'
Jag fastar två resor i veckone, och gifver tiond af allt det jag äger.
13 Amma mai karbar harajin kuwa yana tsaye daga can nesa, bai yarda ya daga kai sama ba, sai dai yana bugun kirjin sa, yana cewa, 'Allah, ka yi mini jinkai, ni mai zunubi.'
Och Publicanen stod långt ifrån, och ville icke lyfta sin ögon upp till himmelen; utan slog sig för sitt bröst, och sade: Gud, miskunda dig öfver mig syndare.
14 Ina gaya maku, wannan mutum ya koma gidansa baratacce, ba kamar dayan ba, domin dukan wanda ya daukaka kansa, za a kaskantar da shi, amma duk wanda kaskantar da kansa kuwa daukaka shi za a yi.”
Jag säger eder: Denne gick dädan hem igen rättfärdigad, mer än den andre; ty den sig upphöjer, han varder förnedrad; och den sig förnedrar, han varder upphöjd.
15 Sai mutanen suka kawo masa jariransu, domin ya taba su, da almajiransa suka ga haka, sai suka kwabe su.
Så båro de ock barn till honom, att han skulle taga på dem; då hans Lärjungar det sågo, näpste de dem.
16 Amma Yesu ya kira su wurinsa, ya ce, “Ku bar yara kanana su zo wurina, kada ku hana su. Ai mulkin Allah na irin su ne.
Men Jesus kallade dem till sig, och sade: Låter barnen komma till mig, och förmener dem icke; ty sådana hörer Guds rike till.
17 Gaskiya ina gaya maku, duk wanda bai karbi mulkin Allah kamar karamin yaro ba, lallai ba zai shige shi ba.”
Sannerliga säger jag eder: Hvilken som icke tager Guds rike som ett barn, han skall icke komma derin.
18 Wani shugaban jama'a ya tambaye shi ya ce “Malam managarci, me zan yi in gaji rai Madawwami?” (aiōnios g166)
Och frågade honom en öfverste, sägandes: Gode Mästar, hvad skall jag göra, att jag må få evinnerligit lif? (aiōnios g166)
19 Yesu ya ce masa, “Don me ka kira ni managarci? Babu wani managarci sai Allah kadai.
Sade Jesus till honom: Hvi kallar du mig godan? Ingen är god, utan allena Gud.
20 Ka dai san dokokin - kada ka yi zina, kada ka yi kisankai, kada ka yi sata, kada ka yi shaidar karya, ka girmama mahaifinka da mahaifiyarka.”
Budorden vetst du: Du skall icke bedrifva hor; du skall icke dräpa; du skall icke stjäla; du skall icke säga falskt vittnesbörd; du skall ära din fader och dina moder.
21 Sai shugaban ya ce, “Dukan wadannan abubuwa na kiyaye su tun a kuruciya ta.”
Då sade han: Allt detta hafver jag hållit af min ungdom.
22 Da Yesu ya ji haka, ya ce masa, “Abu daya ne kadai ya rage maka. Dole ne ka sayar da dukan mallakarka, ka rarraba wa gajiyayyu, za ka kuma sami wadata a sama - sa'annan ka zo ka biyoni.”
Då Jesus det hörde, sade han till honom: Än fattas dig ett; sälj bort allt det du hafver, och skift emellan de fattiga, och du skall få en skatt i himmelen; och kom, och följ mig.
23 Amma da mai arzikin ya ji wadannan abubuwa, sai yayi bakin ciki kwarai, don shi mai arziki ne sosai.
Då han det hörde, vardt han storliga bedröfvad; ty han var ganska rik.
24 Yesu kuwa, da ya ga ransa ya baci, sai ya ce, “Yana da wuya masu dukiya su shiga mulkin Allah!
Då Jesus såg honom vara mägta bedröfvad, sade han: O! med huru stor plats komma de i Guds rike, som penningar hafva;
25 Zai zama da sauki rakumi ya shiga kafar allura, da mai arziki ya shiga mulkin Allah.”
Ty snarare kan en camel gå igenom ett nålsöga, än en riker komma in i Guds rike.
26 Wadanda suka ji wannan magana suka ce, “Idan hakane wa zai sami ceto kenan?”
Då sade de som det hörde: Ho kan då varda salig?
27 Yesu ya amsa, “Abin da ya fi karfin mutum, mai yiwuwa ne a gun Allah.”
Men han sade: Det omöjeligit är för menniskom, det är möjeligit för Gud.
28 Sai Bitrus ya ce, “To, ga shi mun bar mallakarmu, mun bi ka.”
Då sade Petrus: Si, vi hafve all ting öfvergifvit, och följt dig.
29 Yesu ya ce masu, “Hakika, ina gaya maku, ba wanda zai bar gida, ko matarsa, ko 'yan'uwansa, ko iyayensa, ko kuma 'ya'yansa, saboda mulkin Allah,
Sade han till dem: Sannerliga säger jag eder; ingen är den som hafver öfvergifvit hus, eller föräldrar, eller bröder, eller hustru, eller barn, för Guds rikes skull;
30 sa'annan ya kasa samun ninkin ba ninkin a duniyan nan, da rai na har abada a duniya mai zuwa.” (aiōn g165, aiōnios g166)
Den icke skall igenfå mycket mer i denna tiden, och i tillkommande verld evinnerligit lif. (aiōn g165, aiōnios g166)
31 Bayan da ya tara su goma sha biyun nan, ya ce masu, “Ga shi, muna tafiya zuwa Urushalima, duk abubuwan da aka rubuta game da Dan Mutum ta hannun annabawa zasu tabbata.
Då tog Jesus till sig de tolf, och sade till dem: Si, vi gåm upp till Jerusalem, och all ting skola fullbordad varda, som skrifven äro af Propheterna om menniskones Son.
32 Gama za a bashe shi ga al'ummai, a yi masa ba'a, a wulakanta shi, a kuma tofa masa miyau.
Ty han skall öfverantvardas Hedningom, och begabbas, och försmädas, och bespottas.
33 Za su yi masa bulala, su kashe shi, a rana ta uku kuma zai tashi.”
Och sedan de hafva hudflängt honom, skola de döda honom; och tredje dagen skall han uppstå igen.
34 Amma ba su fahimci ko daya daga cikin wadannan abubuwa ba, domin zancen nan a boye yake daga garesu, ba su ma gane abin da aka fada ba.
Men de förstodo der intet af, och talet var dem så fördoldt, att de icke förstodo hvad som sades.
35 Da ya kusato Yariko, ga wani makaho zaune a gefen hanya, yana bara,
Så hände sig, att när han kom in mot Jericho, satt en blinder vid vägen, och tiggde.
36 da ya ji taro na wucewa, sai ya tambaya ko menene.
Och när han hörde folket framgå, frågade han hvad det var?
37 Suka ce masa Yesu Banazarat ne yake wucewa.
Då sade de till honom, att Jesus af Nazareth gick der fram.
38 Sai makahon ya ta da murya mai karfi, ya ce, “Yesu, Dan Dauda, ka yi mani jinkai.”
Då ropade han, och sade: Jesu, Davids Son, varkunna dig öfver mig.
39 Sai wadanda suke gaba suka kwabe shi, suna gaya masa ya yi shiru. Amma ya kara daga murya kwarai da gaske, yana cewa, “Dan Dauda, ka yi mani jinkai.”
Men de, som föregingo, näpste honom, att han skulle tiga; men han ropade dessmer: Davids Son, varkunna dig öfver mig.
40 Sai Yesu ya tsaya, ya umarta a kawo shi wurinsa. Da makahon ya zo kusa, sai Yesu ya tambaye shi,
Då stadnade Jesus, och böd leda honom till sig. Då han kom fram, frågade han honom,
41 “Me kake so in yi maka?” Ya ce, “Ubangiji, ina so in samu gani.”
Sägandes: Hvad vill du, att jag skall göra dig? Då sade han: Herre, att jag måtte få min syn.
42 Yesu ya ce masa, “Karbi ganin gari, bangaskiyarka ta warkar da kai.”
Och Jesus sade till honom: Haf din syn; din tro hafver frälst dig.
43 Nan take ya samu gani, ya bi Yesu, yana daukaka Allah. Ganin haka, sai duk jama'a suka yabi Allah.
Och straxt fick han sin syn igen, och följde honom, prisandes Gud. Och allt folket, som detta sågo, lofvade Gud.

< Luka 18 >