< Luka 18 >

1 Ya kuma ba su wani misali cewa ya kamata kullum su yi addu'a kada kuma su karaya,
And he spake a parable unto them [to this end], that men ought always to pray, and not to faint;
2 yace, “A wani gari an yi wani alkali mara tsoron Allah, kuma baya ganin darajan mutane.
Saying, There was in a city a judge, which feared not God, neither regarded man:
3 Akwai wata mace gwauruwa a wannan garin, wadda ta rika zuwa wurinsa, tana ce masa, 'Ka taimake ni yanda zan sami adalci a kan abokin gaba na.'
And there was a widow in that city; and she came unto him, saying, Avenge me of mine adversary.
4 An dade bai so ya taimaka mata, amma daga baya sai ya ce a ransa, 'ko da yake ba na tsoron Allah, ba na kuma darajanta mutane,
And he would not for a while: but afterward he said within himself, Though I fear not God, nor regard man;
5 duk da haka saboda gwauruwar nan ta dame ni, zan taimake ta domin ta sami adalci, yadda ba za ta gajiyar da ni da zuwanta wurina ba.'”
Yet because this widow troubleth me, I will avenge her, lest by her continual coming she weary me.
6 Sai Ubangiji ya ce, “Ku ji fa abin da alkalin nan marar gaskiya ya fada.
And the Lord said, Hear what the unjust judge saith.
7 A yanzu Allah ba zai biya wa zababbunsa da suke yi masa kuka dare da rana hakkinsu ba? Zai yi jinkiri a wajen taimakonsu ne?
And shall not God avenge his own elect, which cry day and night unto him, though he bear long with them?
8 Ina gaya maku, zai biya masu hakkin su da wuri. Amma sa'adda Dan Mutum ya zo, zai tarar da bangaskiya a duniya?”
I tell you that he will avenge them speedily. Nevertheless when the Son of man cometh, shall he find faith on the earth?
9 Ya sake ba da misalin nan ga wadansu masu amincewa da kansu, wai su masu adalci ne, har suna raina sauran mutane,
And he spake this parable unto certain which trusted in themselves that they were righteous, and despised others:
10 “Wadansu mutane biyu suka shiga haikali domin yin addu'a - daya Bafarise, dayan kuma mai karbar haraji ne.
Two men went up into the temple to pray; the one a Pharisee, and the other a publican.
11 Sai Bafarisen ya mike, ya yi addu'a a kan wadannan abubuwa game da kansa, 'Allah, na gode maka, da cewa ni ba kamar sauran mutane dake mazambata ba, ko marasa adalci, ko mazinata, ko kamar wannan mai karbar harajin.
The Pharisee stood and prayed thus with himself, God, I thank thee, that I am not as other men [are], extortioners, unjust, adulterers, or even as this publican.
12 Duk mako ina azumi sau biyu. Nakan bayar da zakkar dukan abin da na samu.'
I fast twice in the week, I give tithes of all that I possess.
13 Amma mai karbar harajin kuwa yana tsaye daga can nesa, bai yarda ya daga kai sama ba, sai dai yana bugun kirjin sa, yana cewa, 'Allah, ka yi mini jinkai, ni mai zunubi.'
And the publican, standing afar off, would not lift up so much as [his] eyes unto heaven, but smote upon his breast, saying, God be merciful to me a sinner.
14 Ina gaya maku, wannan mutum ya koma gidansa baratacce, ba kamar dayan ba, domin dukan wanda ya daukaka kansa, za a kaskantar da shi, amma duk wanda kaskantar da kansa kuwa daukaka shi za a yi.”
I tell you, this man went down to his house justified [rather] than the other: for every one that exalteth himself shall be abased; and he that humbleth himself shall be exalted.
15 Sai mutanen suka kawo masa jariransu, domin ya taba su, da almajiransa suka ga haka, sai suka kwabe su.
And they brought unto him also infants, that he would touch them: but when [his] disciples saw [it], they rebuked them.
16 Amma Yesu ya kira su wurinsa, ya ce, “Ku bar yara kanana su zo wurina, kada ku hana su. Ai mulkin Allah na irin su ne.
But Jesus called them [unto him], and said, Suffer little children to come unto me, and forbid them not: for of such is the kingdom of God.
17 Gaskiya ina gaya maku, duk wanda bai karbi mulkin Allah kamar karamin yaro ba, lallai ba zai shige shi ba.”
Verily I say unto you, Whosoever shall not receive the kingdom of God as a little child shall in no wise enter therein.
18 Wani shugaban jama'a ya tambaye shi ya ce “Malam managarci, me zan yi in gaji rai Madawwami?” (aiōnios g166)
And a certain ruler asked him, saying, Good Master, what shall I do to inherit eternal life? (aiōnios g166)
19 Yesu ya ce masa, “Don me ka kira ni managarci? Babu wani managarci sai Allah kadai.
And Jesus said unto him, Why callest thou me good? none [is] good, save one, [that is], God.
20 Ka dai san dokokin - kada ka yi zina, kada ka yi kisankai, kada ka yi sata, kada ka yi shaidar karya, ka girmama mahaifinka da mahaifiyarka.”
Thou knowest the commandments, Do not commit adultery, Do not kill, Do not steal, Do not bear false witness, Honour thy father and thy mother.
21 Sai shugaban ya ce, “Dukan wadannan abubuwa na kiyaye su tun a kuruciya ta.”
And he said, All these have I kept from my youth up.
22 Da Yesu ya ji haka, ya ce masa, “Abu daya ne kadai ya rage maka. Dole ne ka sayar da dukan mallakarka, ka rarraba wa gajiyayyu, za ka kuma sami wadata a sama - sa'annan ka zo ka biyoni.”
Now when Jesus heard these things, he said unto him, Yet lackest thou one thing: sell all that thou hast, and distribute unto the poor, and thou shalt have treasure in heaven: and come, follow me.
23 Amma da mai arzikin ya ji wadannan abubuwa, sai yayi bakin ciki kwarai, don shi mai arziki ne sosai.
And when he heard this, he was very sorrowful: for he was very rich.
24 Yesu kuwa, da ya ga ransa ya baci, sai ya ce, “Yana da wuya masu dukiya su shiga mulkin Allah!
And when Jesus saw that he was very sorrowful, he said, How hardly shall they that have riches enter into the kingdom of God!
25 Zai zama da sauki rakumi ya shiga kafar allura, da mai arziki ya shiga mulkin Allah.”
For it is easier for a camel to go through a needle’s eye, than for a rich man to enter into the kingdom of God.
26 Wadanda suka ji wannan magana suka ce, “Idan hakane wa zai sami ceto kenan?”
And they that heard [it] said, Who then can be saved?
27 Yesu ya amsa, “Abin da ya fi karfin mutum, mai yiwuwa ne a gun Allah.”
And he said, The things which are impossible with men are possible with God.
28 Sai Bitrus ya ce, “To, ga shi mun bar mallakarmu, mun bi ka.”
Then Peter said, Lo, we have left all, and followed thee.
29 Yesu ya ce masu, “Hakika, ina gaya maku, ba wanda zai bar gida, ko matarsa, ko 'yan'uwansa, ko iyayensa, ko kuma 'ya'yansa, saboda mulkin Allah,
And he said unto them, Verily I say unto you, There is no man that hath left house, or parents, or brethren, or wife, or children, for the kingdom of God’s sake,
30 sa'annan ya kasa samun ninkin ba ninkin a duniyan nan, da rai na har abada a duniya mai zuwa.” (aiōn g165, aiōnios g166)
Who shall not receive manifold more in this present time, and in the world to come life everlasting. (aiōn g165, aiōnios g166)
31 Bayan da ya tara su goma sha biyun nan, ya ce masu, “Ga shi, muna tafiya zuwa Urushalima, duk abubuwan da aka rubuta game da Dan Mutum ta hannun annabawa zasu tabbata.
Then he took [unto him] the twelve, and said unto them, Behold, we go up to Jerusalem, and all things that are written by the prophets concerning the Son of man shall be accomplished.
32 Gama za a bashe shi ga al'ummai, a yi masa ba'a, a wulakanta shi, a kuma tofa masa miyau.
For he shall be delivered unto the Gentiles, and shall be mocked, and spitefully entreated, and spitted on:
33 Za su yi masa bulala, su kashe shi, a rana ta uku kuma zai tashi.”
And they shall scourge [him], and put him to death: and the third day he shall rise again.
34 Amma ba su fahimci ko daya daga cikin wadannan abubuwa ba, domin zancen nan a boye yake daga garesu, ba su ma gane abin da aka fada ba.
And they understood none of these things: and this saying was hid from them, neither knew they the things which were spoken.
35 Da ya kusato Yariko, ga wani makaho zaune a gefen hanya, yana bara,
And it came to pass, that as he was come nigh unto Jericho, a certain blind man sat by the way side begging:
36 da ya ji taro na wucewa, sai ya tambaya ko menene.
And hearing the multitude pass by, he asked what it meant.
37 Suka ce masa Yesu Banazarat ne yake wucewa.
And they told him, that Jesus of Nazareth passeth by.
38 Sai makahon ya ta da murya mai karfi, ya ce, “Yesu, Dan Dauda, ka yi mani jinkai.”
And he cried, saying, Jesus, [thou] Son of David, have mercy on me.
39 Sai wadanda suke gaba suka kwabe shi, suna gaya masa ya yi shiru. Amma ya kara daga murya kwarai da gaske, yana cewa, “Dan Dauda, ka yi mani jinkai.”
And they which went before rebuked him, that he should hold his peace: but he cried so much the more, [Thou] Son of David, have mercy on me.
40 Sai Yesu ya tsaya, ya umarta a kawo shi wurinsa. Da makahon ya zo kusa, sai Yesu ya tambaye shi,
And Jesus stood, and commanded him to be brought unto him: and when he was come near, he asked him,
41 “Me kake so in yi maka?” Ya ce, “Ubangiji, ina so in samu gani.”
Saying, What wilt thou that I shall do unto thee? And he said, Lord, that I may receive my sight.
42 Yesu ya ce masa, “Karbi ganin gari, bangaskiyarka ta warkar da kai.”
And Jesus said unto him, Receive thy sight: thy faith hath saved thee.
43 Nan take ya samu gani, ya bi Yesu, yana daukaka Allah. Ganin haka, sai duk jama'a suka yabi Allah.
And immediately he received his sight, and followed him, glorifying God: and all the people, when they saw [it], gave praise unto God.

< Luka 18 >