< Luka 18 >

1 Ya kuma ba su wani misali cewa ya kamata kullum su yi addu'a kada kuma su karaya,
And he also spoke a parable to them about it being necessary to always pray, and not to give up,
2 yace, “A wani gari an yi wani alkali mara tsoron Allah, kuma baya ganin darajan mutane.
saying, In a certain city there was a judge who did not fear God, and did not regard man.
3 Akwai wata mace gwauruwa a wannan garin, wadda ta rika zuwa wurinsa, tana ce masa, 'Ka taimake ni yanda zan sami adalci a kan abokin gaba na.'
And a widow was in that city, and she came to him, saying, Avenge me of my opponent.
4 An dade bai so ya taimaka mata, amma daga baya sai ya ce a ransa, 'ko da yake ba na tsoron Allah, ba na kuma darajanta mutane,
And for a time he would not, but after these things he said within himself, Although I fear not God, and regard not man,
5 duk da haka saboda gwauruwar nan ta dame ni, zan taimake ta domin ta sami adalci, yadda ba za ta gajiyar da ni da zuwanta wurina ba.'”
yet because this widow causes me a beating, I will avenge her, lest by no end of coming she give me a black eye.
6 Sai Ubangiji ya ce, “Ku ji fa abin da alkalin nan marar gaskiya ya fada.
And the Lord said, Hear ye what the unrighteous judge says.
7 A yanzu Allah ba zai biya wa zababbunsa da suke yi masa kuka dare da rana hakkinsu ba? Zai yi jinkiri a wajen taimakonsu ne?
And God, will he, no, not do the vengeance of his chosen who cry out to him day and night, and yet being patient toward them?
8 Ina gaya maku, zai biya masu hakkin su da wuri. Amma sa'adda Dan Mutum ya zo, zai tarar da bangaskiya a duniya?”
I say to you, that he will do their vengeance speedily. Nevertheless, when the Son of man comes, will he then find faith on the earth?
9 Ya sake ba da misalin nan ga wadansu masu amincewa da kansu, wai su masu adalci ne, har suna raina sauran mutane,
And he also spoke this parable to some of those who were persuaded in themselves that they were righteous, and disdained other men.
10 “Wadansu mutane biyu suka shiga haikali domin yin addu'a - daya Bafarise, dayan kuma mai karbar haraji ne.
Two men went up into the temple to pray, the one a Pharisee, and the other a tax collector.
11 Sai Bafarisen ya mike, ya yi addu'a a kan wadannan abubuwa game da kansa, 'Allah, na gode maka, da cewa ni ba kamar sauran mutane dake mazambata ba, ko marasa adalci, ko mazinata, ko kamar wannan mai karbar harajin.
Having stood by himself, the Pharisee prayed these things: God, I thank thee that I am not as the rest of men, predatory, unjust, adulterers, or even as this tax collector.
12 Duk mako ina azumi sau biyu. Nakan bayar da zakkar dukan abin da na samu.'
I fast twice of the week. I tithe all things, as many as I acquire.
13 Amma mai karbar harajin kuwa yana tsaye daga can nesa, bai yarda ya daga kai sama ba, sai dai yana bugun kirjin sa, yana cewa, 'Allah, ka yi mini jinkai, ni mai zunubi.'
But the tax collector, having stood from afar, would not even lift his eyes to the sky, but beat upon his breast, saying, God, be thou merciful to me a sinful man.
14 Ina gaya maku, wannan mutum ya koma gidansa baratacce, ba kamar dayan ba, domin dukan wanda ya daukaka kansa, za a kaskantar da shi, amma duk wanda kaskantar da kansa kuwa daukaka shi za a yi.”
I say to you, this man went down to his house justified rather than that man. Because every man who lifts himself up will be made lower, and he who makes himself lower will be lifted up.
15 Sai mutanen suka kawo masa jariransu, domin ya taba su, da almajiransa suka ga haka, sai suka kwabe su.
And they were also bringing the infants to him, so that he would touch them, but when the disciples saw it, they rebuked them.
16 Amma Yesu ya kira su wurinsa, ya ce, “Ku bar yara kanana su zo wurina, kada ku hana su. Ai mulkin Allah na irin su ne.
But having summoned them, Jesus said, Allow the children to come to me, and do not forbid them, for of such is the kingdom of God.
17 Gaskiya ina gaya maku, duk wanda bai karbi mulkin Allah kamar karamin yaro ba, lallai ba zai shige shi ba.”
Truly I say to you, whoever will not receive the kingdom of God as a child, will, no, not enter into it.
18 Wani shugaban jama'a ya tambaye shi ya ce “Malam managarci, me zan yi in gaji rai Madawwami?” (aiōnios g166)
And a certain ruler questioned him, saying, Good teacher, having done what, will I inherit eternal life? (aiōnios g166)
19 Yesu ya ce masa, “Don me ka kira ni managarci? Babu wani managarci sai Allah kadai.
And Jesus said to him, Why do thou call me good? None is good except one, God.
20 Ka dai san dokokin - kada ka yi zina, kada ka yi kisankai, kada ka yi sata, kada ka yi shaidar karya, ka girmama mahaifinka da mahaifiyarka.”
Thou know the commandments. Thou shall not commit adultery. Thou shall not murder. Thou shall not steal. Thou shall not give false testimony. Honor thy father and thy mother.
21 Sai shugaban ya ce, “Dukan wadannan abubuwa na kiyaye su tun a kuruciya ta.”
And he said, All these things I have kept from my youth.
22 Da Yesu ya ji haka, ya ce masa, “Abu daya ne kadai ya rage maka. Dole ne ka sayar da dukan mallakarka, ka rarraba wa gajiyayyu, za ka kuma sami wadata a sama - sa'annan ka zo ka biyoni.”
And when he heard these things, Jesus said to him, Yet one thing is lacking from thee. Sell all things, as many as thou have, and distribute to the poor, and thou will have treasure in heaven. And come, follow me.
23 Amma da mai arzikin ya ji wadannan abubuwa, sai yayi bakin ciki kwarai, don shi mai arziki ne sosai.
But when he heard these things, he became very sorrowful, for he was very rich.
24 Yesu kuwa, da ya ga ransa ya baci, sai ya ce, “Yana da wuya masu dukiya su shiga mulkin Allah!
And having seen him become very sorrowful, Jesus said, How difficultly those who have riches will enter into the kingdom of God.
25 Zai zama da sauki rakumi ya shiga kafar allura, da mai arziki ya shiga mulkin Allah.”
For it is easier for a camel to enter in through the hole of a needle, than for a rich man to enter into the kingdom of God.
26 Wadanda suka ji wannan magana suka ce, “Idan hakane wa zai sami ceto kenan?”
And those who heard it said, And who can be saved?
27 Yesu ya amsa, “Abin da ya fi karfin mutum, mai yiwuwa ne a gun Allah.”
And he said, The things impossible with men are possible with God.
28 Sai Bitrus ya ce, “To, ga shi mun bar mallakarmu, mun bi ka.”
And Peter said, Lo, we have left all and followed thee.
29 Yesu ya ce masu, “Hakika, ina gaya maku, ba wanda zai bar gida, ko matarsa, ko 'yan'uwansa, ko iyayensa, ko kuma 'ya'yansa, saboda mulkin Allah,
And he said to them, Truly I say to you, that there is no man who has left house, or parents, or brothers, or wife, or children for the sake of the kingdom of God,
30 sa'annan ya kasa samun ninkin ba ninkin a duniyan nan, da rai na har abada a duniya mai zuwa.” (aiōn g165, aiōnios g166)
who will, no, not receive back manifold more in this time, and in the coming age eternal life. (aiōn g165, aiōnios g166)
31 Bayan da ya tara su goma sha biyun nan, ya ce masu, “Ga shi, muna tafiya zuwa Urushalima, duk abubuwan da aka rubuta game da Dan Mutum ta hannun annabawa zasu tabbata.
And having taken along the twelve, he said to them, Behold, we are going up to Jerusalem, and all the things that are written through the prophets about the Son of man will be completed.
32 Gama za a bashe shi ga al'ummai, a yi masa ba'a, a wulakanta shi, a kuma tofa masa miyau.
For he will be delivered up to the Gentiles, and he will be mocked and insulted and spit upon.
33 Za su yi masa bulala, su kashe shi, a rana ta uku kuma zai tashi.”
And after scourging, they will kill him, and the third day he will rise up.
34 Amma ba su fahimci ko daya daga cikin wadannan abubuwa ba, domin zancen nan a boye yake daga garesu, ba su ma gane abin da aka fada ba.
And they understood none of these things, and this saying was hidden from them, and they did not understand the things that were said.
35 Da ya kusato Yariko, ga wani makaho zaune a gefen hanya, yana bara,
And it came to pass as he approached Jericho, a certain blind man sat beside the road begging.
36 da ya ji taro na wucewa, sai ya tambaya ko menene.
And having heard a multitude going by, he inquired what this may be.
37 Suka ce masa Yesu Banazarat ne yake wucewa.
And they informed him that Jesus the Nazarene passes by.
38 Sai makahon ya ta da murya mai karfi, ya ce, “Yesu, Dan Dauda, ka yi mani jinkai.”
And he cried out, saying, Jesus, thou son of David, be merciful to me.
39 Sai wadanda suke gaba suka kwabe shi, suna gaya masa ya yi shiru. Amma ya kara daga murya kwarai da gaske, yana cewa, “Dan Dauda, ka yi mani jinkai.”
And those who went ahead rebuked him, so that he would be quiet, but he cried out much more, Thou son of David, be merciful to me.
40 Sai Yesu ya tsaya, ya umarta a kawo shi wurinsa. Da makahon ya zo kusa, sai Yesu ya tambaye shi,
And having stood still, Jesus commanded him to be brought to him. And when he came near, he questioned him,
41 “Me kake so in yi maka?” Ya ce, “Ubangiji, ina so in samu gani.”
saying, What do thou that I would do to thee? And he said, Lord, that I may receive sight.
42 Yesu ya ce masa, “Karbi ganin gari, bangaskiyarka ta warkar da kai.”
And Jesus said to him, Receive sight. Thy faith has healed thee.
43 Nan take ya samu gani, ya bi Yesu, yana daukaka Allah. Ganin haka, sai duk jama'a suka yabi Allah.
And immediately he received sight, and followed him glorifying God. And all the people when they saw it gave praise to God.

< Luka 18 >