< Luka 16 >

1 Yesu ya kuma ce wa almajiransa, “Akwai wani mai arziki da yake da wakili, sai aka yi karan sa da cewa wannan wakili yana fallasar masa da dukiya.
Il disait aussi aux disciples: «Un homme riche avait un économe; cet économe lui fut dénoncé comme dissipant ses biens.
2 Sai mai arziki ya kira shi ya ce masa, 'Labarin me nake ji game da kai? Kawo lissafin wakilcin ka, don ba za ka sake zama wakili na ba.'
Il l'appela et lui dit: «Qu'est-ce que j'entends dire de toi? Rends compte de ton administration; car il n'est plus possible que tu administres désormais.» —
3 Sai wakilin ya ce a ransa, 'Kaka zan yi, da yake maigida na zai karbe wakilci daga hannuna? Gashi, ba ni da karfin noma ina kuwa jin kunya in yi roko.
«Que ferai-je?» se dit en lui-même l'économe, «puisque mon maître me retire la gestion de ses biens. Travailler la terre, je n'en ai pas la force; mendier, j'en aurais honte.
4 Na san abin da zan yi domin idan an fitar da ni daga wakilcin, mutane su karbe ni a gidajensu.
Je vois ce que je ferai pour que, destitué de mes fonctions, il se trouve des gens qui me reçoivent dans leurs maisons.»
5 Sai wakilin ya kira kowanne daya da maigidansa ke bi bashi, yace wa na farkon, 'Nawa maigida na yake bin ka?'
Il convoqua l'un après l'autre chacun des débiteurs de son maître.»«Au premier il dit: «Combien dois-tu à mon maître?»
6 Ya ce, 'Garwan mai dari.' Sai ya ce masa, 'Ga takardarka, maza ka zauna, ka rubuta hamsin.'
«Cent mesures d'huile», — «Voici ton billet, reprit l'économe, assieds-toi vite et écris: «cinquante».
7 Ya kuma ce wa wani, 'Nawa ake binka?' Ya ce, 'Buhu dari na alkama.' Ya ce masa, 'Ga tarkardarka, ka rubuta tamanin.'
Ensuite il dit à un autre: «Et toi, combien dois-tu?» Celui-là répondit: «Cent mesures de froment.» «Voici ton billet, reprit encore l'économe, et écris: «quatre-vingts».
8 Sai maigida ya yaba wa wakilin nan marar gaskiya saboda wayonsa. Gama 'ya'yan zamanin nan a ma'ammalar su da mutanen zamaninsu sun fi 'ya'yan haske wayo. (aiōn g165)
«Le maître loua l'économe infidèle de ce qu'il avait agi avec, habileté; parce que les enfants de ce siècle sont, dans leur monde, plus avisés que les enfants de la lumière. (aiōn g165)
9 Ina gaya maku ku yi abuta ta dukiya ta rashin gaskiya, saboda idan ya kare, su karbe ku a gidaje masu dauwama. (aiōnios g166)
Et moi, je vous dis: Du Mamôn de l'iniquité faites-vous des amis qui, lorsqu'il viendra à manquer, vous reçoivent dans les éternels tabernacles. (aiōnios g166)
10 Wanda yake da aminci a karamin abu, mai aminci ne a babban abu, wanda yake marar gaskiya a karamin abu, marar gaskiya ne a babban abu.
Qui est fidèle dans une très petite chose, l'est également dans une grande; qui est injuste dans une très petite chose, l'est également dans une grande.
11 Idan fa ba ku yi aminci da dukiya mara adalci ba, wa zai amince maku da dukiya ta gaskiya?
Si donc vous n'avez pas été fidèles dans le Mamôn injuste, qui vous confiera le véritable?
12 Idan kuma ba ku yi aminci da kudin wani ba, wa zai ba ku kudin da ke naku?
Et si vous n'avez pas été fidèles dans le bien d'un autre, qui vous donnera ce qui est à vous?»
13 Ba bawan da zai iya bauta wa iyayengiji biyu, ko dai ya ki daya, ya so daya ko kuwa ya amince wa dayan, ya raina dayan. Ba za ku iya bauta wa Allah ku kuma bauta wa dukiya ba.”
«Aucun domestique ne peut servir deux maîtres; ou bien, en effet, il haïra l'un et aimera l'autre; ou bien il s'attachera au premier et méprisera le second. Vous ne pouvez servir Dieu et Mamôn.»
14 Da Farisawa da ke da kaunar kudi suka ji dukan wadannan abubuwa, suka yi masa ba'a.
Les Pharisiens qui aiment l'argent entendaient tout cela et tournaient Jésus en dérision.
15 Sai ya ce masu, “Ku ne masu baratar da kanku a gaban mutane, amma Allah ya san zuciyarku. Abin da mutane suke girmamawa kwarai abin kyama ne a gun Allah.
«Vous, leur dit-il, vous voulez vous faire passer pour justes devant les hommes, mais Dieu connaît vos coeurs. Ce qui, d'après les hommes, est élevé, est, devant Dieu, une abomination.»
16 Attaura da litattafan annabawa suna nan har zuwan Yahaya. Tun daga lokacin nan ake yin bisharar mulkin Allah, kowa kuma yana kokarin kutsawa zuwa cikinta.
«Jusques à Jean, la Loi et les Prophètes; depuis, l'Évangile du Royaume de Dieu est annoncé et tous s'efforcent de s'en emparer.»
17 Duk da haka, zai fi sauki sama da kasa su shude, da ko digo daya na attaura ya shude.
«Plus facilement passeront le ciel et la terre que ne tombera un seul petit trait de la Loi.»
18 Duk wanda ya saki matansa ya auri wata ya aikata zina, kuma wanda ma ya auri sakakkiya ya aikata zina.
«Quiconque répudie sa femme et en épouse une autre commet un adultère; et celui qui épouse une femme répudiée par son mari commet un adultère.»
19 Akwai wani mai arziki, mai sa tufafi na alfarma masu tsada yana shagalin sa kowace rana.
«Il y avait un riche qui était vêtu de pourpre et de lin, et qui menait tous les jours joyeuse et splendide vie.
20 Aka ajiye wani gajiyayye a kofarsa, mai suna liazaru wanda duk jikinsa miki ne,
Un pauvre nommé Lazare gisait à sa porte, couvert d'ulcères.
21 Shi kuwa yana marmarin ya koshi da barbashin da ke fadowa daga teburin mai arzikin nan har ma karnuka sukan zo suna lasar mikinsa.
Il aurait bien voulu se rassasier de ce qui tombait de la table du riche; mais les chiens eux-mêmes venaient lécher ses ulcères.
22 Ana nan sai gajiyayyen nan ya mutu, malaiku kuma suka dauke shi suka kai shi wurin Ibrahim. Mai arzikin ma ya mutu, aka kuma binne shi,
Or il arriva que le pauvre mourut, et qu'il fut transporté par les anges dans le sein d'Abraham. Le riche mourut aussi, et fut enseveli.
23 yana cikin hades yana shan azaba, sai ya daga kai ya hangi Ibrahim daga nesa, da Li'azaru a kirjinsa. (Hadēs g86)
Étant dans la Demeure-des-morts, et en proie aux tourments, il leva les yeux; il vit de loin Abraham et, dans son sein, Lazare. (Hadēs g86)
24 Sai ya yi kira ya ce, 'Baba Ibrahim, ka ji tausayi na, ka aiko Li'azaru ya tsoma dan yatsansa a ruwa ya sanyaya harshena, don azaba nake sha a cikin wannan wuta.'
Alors il éleva la voix; il dit: «Père Abraham, aie pitié de moi; et envoie Lazare tremper dans l'eau le bout de son doigt pour rafraîchir ma langue, car je suis torturé dans ces flammes.»
25 Amma Ibrahim ya ce, 'Yaro, ka tuna fa a zamanka na duniya ka sha duniyarka, ka kuma karba abubuwa masu kyau, amma Li'azaru kuma sai wahala. Amma yanzu dadi ake bashi a nan, kai kuwa kana shan azaba.
«Mon enfant, lui répondit Abraham, souviens-toi que, en ta vie, tu as reçu tes biens; Lazare, dans la sienne, a eu des maux. Ici maintenant il est consolé, et toi tu es torturé.
26 Banda haka ma, akwai rami mai zurfi, domin wadanda suke son ketarewa zuwa wurinku kada su iya, kada kuma kowa ya ketaro zuwa wurinmu daga can.'
En outre, un abîme immense est établi entre nous et vous, de sorte qu'il serait impossible à qui le voudrait soit d'aller vers vous de là où nous sommes, soit de venir vers nous de là où vous êtes.»
27 Sai mai arziki ya ce, 'To ina rokonka, Baba Ibrahim, ka aike shi zuwa gidan mahaifina -
«Il reprit: «Père, envoie donc, je t'en supplie, Lazare dans la maison de mon père;
28 domin ina da 'yan'uwa maza biyar, ya je ya yi masu gargadi kada su ma su zo wurin azaban nan.'
car j'ai cinq frères; il leur attestera ces choses afin qu'ils ne viennent pas, eux aussi, dans ce lieu de tourments.»
29 Amma Ibrahim ya ce, 'Suna da Musa da annabawa; bari su saurare su.'
Mais Abraham lui répondit: «Ils ont «Moïse et les Prophètes»; qu'ils les écoutent!» —
30 Sai mai arziki ya amsa, 'A'a, Baba Ibrahim, idan wani daga cikin matattu ya je wurinsu, zasu tuba.'
«Non, père Abraham, continua l'autre, mais si, de chez les morts, quelqu'un va vers eux, ils se repentiront.»
31 Amma Ibrahim ya ce masa, 'In dai har basu saurari Musa da na annabawa ba, ko da wani ya tashi daga matattu ma, ba za su rinjayu ba.'”
Abraham lui dit alors: «S'ils n'écoutent ni «Moïse, » ni «les Prophètes, » quand même quelqu'un ressusciterait d'entre les morts, ils ne seraient pas persuadés.»

< Luka 16 >