< Luka 15 >

1 To sai duk masu karbar haraji da masu zunubi suna ta zuwa wurin Yesu suna sauraronsa.
And pupplicans and synful men weren neiyynge to him, to here hym.
2 Dukan Farisawa da Marubuta suna ta gunaguni da junansu, cewa, “Wannan mutum yana karbar masu zunubi, har ma tare suke cin abinci.”
And the Farisees and scribis grutchiden, seiynge, For this resseyueth synful men, and etith with hem.
3 Yesu ya fadi wannan misali, ya ce,
And he spak to hem this parable,
4 “Idan waninku yana da tumaki dari, sai dayarsu ta bace, wato ba zai bar tasa'in da taran nan a makiyaya, ya bi sawun wadda ta bata gudan nan har sai ya same shi ba?
and seide, What man of you that hath an hundrith scheep, and if he hath lost oon of hem, whethir he leeueth not nynti and nyne in desert, and goith to it that perischide, til he fynde it?
5 Idan kuwa ya same ta, sai ya dauke ta a kafadarsa yana farin ciki.
And whanne he hath foundun it, he ioieth, and leyith it on hise schuldris; and he cometh hoom,
6 In ya dawo gida, sai ya kira abokansa da makwabta, yace masu, 'Ku taya ni murna don na samo tunkiyata da ta bata.'
and clepith togidir hise freendis and neiyboris, and seith to hem, Be ye glad with me, for Y haue founde my scheep, that hadde perischid.
7 Ina gaya maku, haka kuma za a yi farin ciki a sama, a kan mai zunubi guda da ya tuba, fiye da kan masu adalci tassa'in da tara wadanda ba su bukatar tuba.
And Y seie to you, so ioye schal be in heuene on o synful man doynge penaunce, more than on nynti and nyne iuste, that han no nede to penaunce.
8 Ko kuwa wacce mace ce, in tana da kudi azurfa guda goma, in ta batar da daya, ba za ta kunna fitila ta share gidan, ta yi ta neman shi har sai ta same shi ba?
Or what womman hauynge ten besauntis, and if sche hath lost oo besaunt, whether sche teendith not a lanterne, and turneth vpsodoun the hows, and sekith diligentli, til that sche fynde it?
9 In kuwa ta same shi sai ta tara kawayenta da makwabtanta, ta ce, 'Ku taya ni farin ciki don na sami kudin nan nawa da ya bace.'
And whanne sche hath foundun, sche clepith togidir freendis and neiyboris, and seith, Be ye glad with me, for Y haue founde the besaunt, that Y hadde lost.
10 Haka nake gaya maku, abin farin ciki ne ga mala'ikun Allah idan mai zunubi guda ya tuba.”
So Y seie to you, ioye schal be bifor aungels of God on o synful man doynge penaunce.
11 Sai Yesu ya ce, “Akwai wani mutum mai 'ya'ya biyu maza,
And he seide, A man hadde twei sones;
12 sai karamin ya ce wa mahaifinsa, 'Baba, bani rabona daga cikin dukiyarka.' Sai mahaifinsa ya raba masu dukiyarsa tsakaninsu.
and the yonger of hem seide to the fadir, Fadir, yyue me the porcioun of catel, that fallith to me. And he departide to hem the catel.
13 Bayan 'yan kwanaki kadan, sai karamin dan ya tattara duk mallakarsa, ya kama hanya zuwa wata kasa mai nisa. A can ya batas da kudinsa, yana sayan abubuwan da ba ya bukata, ya kuma batas da kudinsa a wajen masha'a.
And not aftir many daies, whanne alle thingis weren gederid togider, the yonger sone wente forth in pilgrymage in to a fer cuntre; and there he wastide hise goodis in lyuynge lecherously.
14 Bayan da ya batas da duk abin da ya ke da shi, sai aka yi babbar yunwa a kasar, sai ya shiga fatara.
And aftir that he hadde endid alle thingis, a strong hungre was maad in that cuntre, and he bigan to haue nede.
15 Ya je ya mika kansa domin aiki ga wani dan kasar, sai ya aike shi cikin gonakinsa domin ya rika ba aladu abinci.
And he wente, and drouy hym to oon of the citeseyns of that cuntre. And he sente hym in to his toun, to fede swyn.
16 Har yayi marmarin ya ci daga cikin barbashin da aladu suke ci, domin babu wanda yake ba shi wani abu ya ci.
And he coueitide to fille his wombe of the coddis that the hoggis eeten, and no man yaf hym.
17 Amma da hankalinsa ya dawo, ya ce, 'Barorin mahaifina su nawa ne da suke da abinci isasshe, amma ina nan a nan, ina mutuwa sabili da yunwa!
And he turnede ayen to hym silf, and seide, Hou many hirid men in my fadir hous han plente of looues; and Y perische here thorouy hungir.
18 Zan tashi, in tafi gun mahaifina, in ce masa, “Baba, na yi wa sama zunubi, na kuma saba maka.
Y schal rise vp, and go to my fadir, and Y schal seie to hym, Fadir, Y haue synned in to heuene, and bifor thee;
19 Ban cancanci a kara kira na danka ba; ka mai da ni kamar daya daga cikin barorinka.'”
and now Y am not worthi to be clepid thi sone, make me as oon of thin hirid men.
20 Sai ya tashi, ya taho wurin mahaifinsa. Amma tun yana daga nesa, sai mahaifinsa ya hango shi tausayi ya kama shi, ya ruga a guje, ya rungume shi, ya yi ta sumbatar sa.
And he roos vp, and cam to his fadir. And whanne he was yit afer, his fadir saiy hym, and was stirrid bi mercy. And he ran, and fel on his necke, and kisside hym.
21 Dan kuma ya ce masa, 'Baba, na yi wa sama zunubi, na kuma saba maka. Ban isa a kara kira na danka ba.'
And the sone seide to hym, Fadir, Y haue synned in to heuene, and bifor thee; and now Y am not worthi to be clepid thi sone.
22 Amma mahaifinsa ya ce wa bayinsa, 'Ku yi hamzari ku kawo riga mafi kyau, ku yafa masa. Ku sa masa zobe a hanunsa da takalma a kafafunsa.
And the fadir seide to hise seruauntis, Swithe brynge ye forth the firste stoole, and clothe ye hym, and yyue ye a ryng in his hoond,
23 Sa'annan a kawo kiwataccen marakin nan, a yanka. Mu yi buki!
and schoon on hise feet; and brynge ye a fat calf, and sle ye, and ete we, and make we feeste.
24 Gama da na ya mutu a da, amma yanzu yana a raye. Ya bata a da, amma a yanzu an same shi.' Sai suka fara liyafa.
For this my sone was deed, and hath lyued ayen; he perischid, and is foundun. And alle men bigunnen to ete.
25 A wannan lokacin, babban dansa yana gona. Da ya kai kusa da gida, ya ji ana kade-kade da raye-raye.
But his eldere sone was in the feeld; and whanne he cam, and neiyede to the hous, he herde a symfonye and a croude.
26 Sai ya kira wani bawan gidan, ya tambayi manufar wadannan abubuwa.
And he clepide oon of the seruauntis, and axide, what these thingis weren.
27 Bawan ya ce masa, 'Dan'uwanka ne ya dawo gida, mahaifinka kuma ya yanka kiwataccen marakin nan, saboda ya dawo gida lafiya.'
And he seide to hym, Thi brother is comun, and thi fadir slewe a fat calf, for he resseyuede hym saaf.
28 Amma dan'uwan ya yi fushi, ya ki ya shiga ciki, mahaifinsa kuwa ya fito, ya roke shi.
And he was wrooth, and wolde not come in. Therfor his fadir wente out, and bigan to preye hym.
29 Amma babban dan ya amsa wa ubansa ya ce, 'Duba, duk yawan shekarun nan da nake bauta maka, ban taba karya umarnin ka ba, duk da haka ba ka taba bani ko dan taure da zan yi shagali tare da abokaina ba,
And he answerde to his fadir, and seide, Lo! so many yeeris Y serue thee, and Y neuer brak thi comaundement; and thou neuer yaf to me a kidde, that Y with my freendis schulde haue ete.
30 amma da dan nan naka ya zo wanda ya fallasar da dukiyarka a kan karuwai, ka yanka masa kiwataccen marakin nan.
But aftir that this thi sone, that hath deuourid his substaunce with horis, cam, thou hast slayn to hym a fat calf.
31 Sai mahaifin ya ce masa, 'Dana, ai kullum kana tare da ni, duk abin da yake nawa naka ne.
And he seide to hym, Sone, thou art euer more with me, and alle my thingis ben thine.
32 Amma, daidai ne a yi murna da farinciki, don dan'uwan nan naka da ya mutu, amma yanzu yana da rai, da ya bata, amma yanzu an same shi.'”
But it bihofte for to make feeste, and to haue ioye; for this thi brother was deed, and lyuede ayen; he perischide, and is foundun.

< Luka 15 >