< Luka 14 >

1 Wata ranar Asabaci, ya shiga gidan wani daya daga cikin shugabanin Farisawa domin cin abinci, mutane kuwa suna sa masa idanu.
One (Jewish day of rest/Sabbath day), Jesus went to eat [SYN] at the house of an important Pharisee. Some [men who studied the Jewish] laws and other Pharisees who were there were watching him carefully [to see if he would do something for which they could accuse him].
2 Sai ga wani a gabansa mai ciwon fara.
Unexpectedly, there was a man in front of Jesus whose arms and legs were swollen.
3 Yesu ya tambaye masanan attaura da Farisawa, “Ya halata a wakar a ranan Asabaci, ko a'a?”
Jesus said to them, “Is it permitted in [our(inc)] Jewish laws to heal [someone] (on our Jewish rest day/on the Sabbath), or not?”
4 Amma suka yi shiru. Yesu kuwa ya kama shi, ya warkar da shi, ya kuma sallame shi.
[They knew that their laws permitted it, but they thought that healing was work, which they thought was wrong to do] (on the Sabbath/on the Jewish rest day) (OR, [they knew that their laws permitted it, but they did not want to admit it]). So they did not reply. Then Jesus put his hands on the man and healed him. Then he told him to go [home].
5 Sai yace masu, “Wanene a cikinku in yana da jaki ko takarkari ya fadi a rijiya ran Asabaci, ba zai fitar da shi nan da nan ba?”
Then he said to the rest of them, “If you had a son or an ox that fell into a well on a (Sabbath/our day of rest), would you immediately [work to] pull him out, [or would you(sg) let him stay there until the next day]?”
6 Sai suka kasa ba da amsar wadannan abubuwa.
[They knew that they would immediately work to pull him out, even on their day of rest, so they could not justly say that Jesus did wrong by healing the man on that day. So] they said nothing in reply to Jesus.
7 Sa'adda Yesu ya lura da yadda wadanda aka gayyato sun zabi mazaunan alfarma, sai ya ba su misali yana ce masu,
Jesus noticed that those people who had been {whom [the Pharisee] had} invited [to the meal] chose [to sit in] the places where important [people usually sit]. Then he gave [this advice] to them:
8 “Sa'adda wani ya gayyace ka zuwa bikin aure, kada ka zauna a wuri mai daraja, domin yana yiwuwa an gayyaci wani wanda ya fi ka daraja.
“When one of you [(sg)] is invited by someone {someone invites one of you [(sg)]} to a wedding feast, do not sit in a place where important people sit. Perhaps the man [giving the feast] has invited a man more important than you [(sg)].
9 Sa'adda wanda ya gayyace ku duka biyu ya zo, zai ce maka, 'Ka ba mutumin nan wurinka,' sa'annan a kunyace za ka koma mazauni mafi kaskanci.
[When that man comes], the man who invited both of you will come to you [(sg)] and say to you, ‘Let this man take your seat!’ Then you [(sg)] will have to take the most undesirable seat, and you will be ashamed.
10 Amma idan an gayyace ka biki, sai ka je ka zauna a wuri mafi kaskanci, domin idan wanda ya gayyace ka ya zo, yana iya ce maka, 'Aboki, hawo nan mana'. Sannan za ka sami girma kenan a gaban dukan wadanda kuke zaune tare a kan teburi.
Instead, when you are invited {[someone] invites one of you} [to a feast], go and sit in the most undesirable seat. Then when the man who invited everyone comes, he will say to you [(sg)], ‘Friend, sit in a better seat!’ Then all the people who are eating with you [(sg)] will see that he is honoring you.
11 Duk wanda ya daukaka kansa, za a kaskantar da shi, wanda ya kaskantar da kansa, kuma daukaka shi za a yi”.
Also, [remember this]: [God] will humble those who exalt themselves. And [he] will exalt those who humble themselves.”
12 Yesu ya ce wa mutumin da ya gayyace shi, “Idan za ka gayyaci mutum cin abinci ko biki, kada ka gayyaci abokanka, ko 'yan'uwanka, ko danginka, ko makwabtanka masu arziki, kamar yadda suna iya gayyatar ka, sai ya zama an maida maka.
[Jesus] also said to [the Pharisee] who had invited him to the meal, “When you [(sg)] invite people to a midday or evening meal, do not invite your friends or your family or your other relatives or your rich neighbors. They can later invite you [(sg) for a meal]. In that way they will repay you.
13 Amma idan za ka kira biki sai ka gayyace matalauta, da nakasassu, da guragu, da makafi,
Instead, when you [(sg)] give a feast, invite poor [people], crippled [people], lame [people], or blind [people].
14 za ka kuwa sami albarka da yake ba su da hanyar saka maka. Gama za a saka maka a ranar tashin masu adalci.”
They will be unable to repay you. [But God will bless you! He] will repay you [at the time] when [he causes] righteous people to become alive again.”
15 Da daya daga cikin wadanda ke zama akan teburi da Yesu ya ji wadannan abubuwa, sai ya ce masa, “Albarka ta tabbata ga wanda zai ci abinci a mulkin Allah!”
One of those who were eating with Jesus heard him say that. He said to Jesus, “God [has truly] blessed [us Jews] who will eat [with the Messiah] when he starts to rule!”
16 Amma Yesu ya ce masa, “Wani mutum ne ya shirya babban biki ya gayyaci mutane da yawa.
But [to show that many Jews whom God had invited would not accept God’s invitation] [MET], Jesus replied to him, “One time a man [decided] to prepare a large feast. He invited many people to come.
17 Da lokacin biki ya yi, sai ya aiki bawansa ya ce wa wadanda aka gayyata, “Ku zo, duk an shirya kome.”
When it was the day for the feast, he sent his servant to tell those who had been {whom he had} invited, ‘Come [now] because everything is ready!’
18 Sai dukansu, suka fara kawo dalilai. Na farko ya ce masa, 'Na sayi gona, lalle ne in je in gan ta. Ina rokonka ka dauke mani.'
But [when the servant did that], all of the people [whom he had invited] began to say why they did not want to come. The first [man the servant went to] said, ‘I have just bought a field, and I must go and see it. Please [ask your master to] forgive me for not coming!’
19 Sai wani ya ce, 'Na sayi shanu garma biyar, ina so in gwada su. Ina ronkan ka, ka dauke mani.'
Another person said, ‘I have just bought five pair of oxen, and I must go to examine them. Please [ask your master to] forgive me for not coming!’
20 Wani mutum kuma ya ce, 'Na yi aure, don haka ba zan iya zuwa ba.'
Another person said, ‘I have just been married. So I cannot come.’
21 Da bawan ya zo ya fadi wa maigidansa wadannan abubuwa, sai maigidan yayi fushi, ya ce wa bawansa, jeka da sauri ka bi cikin titunan birni da kwararo-kwararo, ka kawo gajiyayyu, da nakasassu, da makafi, da guragu.'
So the servant returned to his master and reported what [everyone had said]. The owner of the house was angry [when he heard the reasons they gave for not] coming. He said to his servant, ‘Go out quickly to the streets and alleys of the city [and find] poor and crippled and blind and lame [people, and bring] them here into [my house]!’
22 Sai bawan ya ce, 'Maigida, abin da ka umarta an gama, amma har yanzu da sauran wuri.”
[After the servant went and did that], he [came back and] said, ‘Sir, I have done what you [(sg)] told me to do, but there is still room [for more people].’
23 Sai maigidan ya ce wa bawan, 'Jeka, ka bi kwararo-kwararo da hanyoyin karkara, ka rinjayi mutane su shigo, don a cika gidana.
[So] his master said to him, ‘Then go [outside the city]. Search for people along the highways. Search also along the narrow roads with hedges beside them [where homeless people may be staying]. Strongly urge the people in those places to come to [my house]. I want it to be full of [people]!’”
24 Gama ina gaya maku, babu ko daya daga cikin mutanen da na gayyata da farko da zai dandana bikina.”
[Then Jesus said], “I tell you [(pl)] this: Very few of you [Jewish] people will enjoy my feast, even though [I] invited you [first to eat it with me when I become king].”
25 Ana nan, taron suna tafiya tare da shi, sai ya juya ya ce masu,
Large groups of people were traveling with [Jesus]. He turned and said to them,
26 “Duk mai zuwa wurina amma bai ki mahaifinsa da mahaifiyarsa, da matarsa, da 'ya'yansa, da 'yan'uwansa maza da mata ba - I, har da ransa ma, ba zai iya zama almajirina ba.
“If anyone comes to me who loves his father and mother and wife and children and brothers and sisters [more than] [HYP] [he loves me], he cannot be my disciple. He must even love me more than he loves his own life!
27 Duk wanda bai dauki gijiyensa ya biyo ni ba, ba zai iya zama almajirina ba.
[People who are ready to execute a prisoner make] him carry his cross [MET] [to the place where others will nail him] on it. Only those who are willing [to allow others to hurt them and disgrace them] like that because of being my disciples, and who are willing to obey what I teach, can be my disciples.
28 Wanene a cikinku wanda yake niyyar gina bene, da ba zai zauna ya yi lissafin abin da zai kashe ba tun da farko, ko yana da ishashen kudi da zai iya kare aikin?
[I will illustrate] [MET]. If one of you desired to build a (tower/big house), (you would surely first sit down and determine how much it would cost!/would you not first sit down and determine how much it would cost?) [RHQ] Then you would determine whether you had enough money to complete it.
29 Kada ya zama bayan da ya sa harsashin ginin, ya kasa gamawa, har duk wadanda suka gani su fara yi masa ba'a,
[If you did not do that], if you laid the foundation and were not able to finish [the rest of the tower], everyone who saw it would make fun of you.
30 su rika cewa, ga mutumin nan ya fara gini amma ya kasa gamawa.'
They would say, ‘This man started to build [a tower], but he was not able to finish it!’
31 Ko kuwa wanne sarki ne, in za shi je yaki da wani sarki, da ba zai zauna da farko ya yi shawara ya ga ko shi mai jarumawa dubu goma zai iya karawa da dayan sarkin mai jarumawa dubu ashirin ba?
Or, if a king decided to [send his army to] war against another king, (he would surely first sit down [with those who] advised [him]./would he not first sit down [with those who] advised [him]?) [RHQ] They would determine whether [his army], which had only 10,000 soldiers, could defeat the [other army], which had 20,000 soldiers, and was about to attack his [army].
32 In kuwa ba zai iya ba, to tun wancan yana nesa, sai ya aiki wakili ya kuma tambayo sharudan salama.
If he [decided] that his army could not [defeat that army], he would send messengers to [the other king] while the other army was still far away. He would tell the messengers to say to that king, ‘What things must I do to have peace with your country?’
33 Haka ma, ba wani a cikinku wanda bai rabu da duk abin da ya mallaka ba, da zai iya zama almajirina.”
So, similarly, if any one of you does not first decide that you [(sg)] are [willing to] give up all that you have, you cannot be my disciple.”
34 “Gishiri abu ne mai kyau, amma idan gishiri ya sane, da me za a dadada shi?
[Jesus also said, “You are like] [MET] salt, which is useful [to put on food]. But (salt certainly cannot be made {[you] certainly cannot make salt} to taste salty again if it stops tasting salty!/can salt be made {can [you] make salt} to taste salty again if it quits tasting salty?) [RHQ]
35 Ba shi da wani anfani a kasa, ko ya zama taki. Sai dai a zubar kawai. Duk mai kunnen ji, ya ji.”
[If salt does not taste salty any more], it is not good for the soil or even for the manure heap. [People] throw it away. [The same thing will happen to you if you become useless to God]. If you want to understand what I just said [IDM], you must consider [carefully] what you have heard!”

< Luka 14 >