< Luka 13 >

1 A lokacin, wadansu mutane suka gaya masa game da galilawa wadanda Bilatus ya gauraye jininsu da hadayunsu.
Just at that time some people had come to tell Jesus about the Galileans, whose blood Pilate had mingled with the blood of their sacrifices.
2 Sai Yesu ya amsa masu yace “Kuna tsammani wadannan Galilawa sun fi duk sauran Galilawan zunubi ne, da suka sha azaba haka?
“Do you suppose,” replied Jesus, “that, because these Galileans have suffered in this way, they were worse sinners than any other Galileans?
3 A'a, ina gaya maku. In ba ku tuba ba, dukanku za ku halaka kamarsu.
No, I tell you; but, unless you repent, you will all perish as they did.
4 Ko kuwa mutane goma sha takwas din nan da suna Siluwam wadanda hasumiya ta fado a kansu ta kashe su, kuna tsamani sun fi duk sauran mutanen Urushalima laifi ne?
Or those eighteen men at Siloam on whom the tower fell, killing them all, do you suppose that they were worse offenders than any other inhabitants of Jerusalem?
5 Ina gaya maku ba haka bane. Amma duk wanda ya ki tuba, dukanku za su hallaka”
No, I tell you; but, unless you repent, you will all perish in the same manner.”
6 Yesu ya fada wannan misali, “Wani mutum yana da baure wanda ya shuka a garkar inabinsa sai ya zo neman 'ya'yan itacen amma bai samu ba.
And Jesus told them this parable – “A man, who had a fig tree growing in his vineyard, came to look for fruit on it, but could not find any.
7 Sai mutumin ya ce wa mai kula da garkar, “ka ga, shekara uku kenan nake zuwa neman 'ya'yan wannan baure, amma ban samu ba. A sare shi. Yaya za a bar shi ya tsare wurin a banza?
So he said to his gardener ‘Three years now I have come to look for fruit on this fig tree, without finding any! Cut it down. Why should it rob the soil?’
8 Sai mai lura da garkar ya amsa yace, 'Ka dan ba shi lokaci kadan in yi masa kaftu in zuba masa taki.
‘Leave it this one year more, Sir,’ the man answered, ‘until I have dug around it and manured it.
9 In yayi 'ya'ya shekara mai zuwa to, amma in bai yi 'ya'ya ba sai a sare shi!”'
Then, if it bears in future, well and good; but if not, you can have it cut down.’”
10 Wata rana Yesu yana koyarwa a wata majami' a ran Asabaci.
Jesus was teaching on a Sabbath in one of the synagogues,
11 Sai, ga wata mace a wurin shekarunta goma sha takwas tana da mugun ruhu, duk ta tankware, ba ta iya mikewa.
and he saw before him a woman who for eighteen years had suffered from weakness owing to her having an evil spirit in her. She was bent double, and was wholly unable to raise herself.
12 Da Yesu ya gan ta, sai ya kira ta ya ce mata, an warkar da ke daga wannan cuta.”
When Jesus saw her, he called her to him, and said, “Woman, you are released from your weakness.”
13 Sai Yesu ya dora hannunsa a kanta, nan da nan sai ta mike a tsaye ta fara daukaka Allah.
He placed his hands on her, and she was instantly made straight, and began to praise God.
14 Amma shugaban majami'a yayi fushi domin Yesu yayi warkarwa a ranar Asabaci. Sai shugaban ya amsa yace wa jama'a, “Akwai ranaku shida da ya kamata a yi aiki. Ku zo domin a warkar da ku amma ba ranar Asabaci ba.”
But the synagogue leader, indignant that Jesus had worked the cure on the Sabbath, intervened and said to the people, “There are six days on which work ought to be done; come to be cured on one of those, and not on the Sabbath.”
15 Amma Ubangiji ya amsa masa ya ce, “Munafukai! Ashe kowannenku ba ya kwance Jakinsa ko Sa daga turkensa ya kai shi banruwa ran Asabaci?
“You hypocrites!” the Master answered him. “Does not everyone of you let your ox or your donkey loose from its manger, and take it out to drink, on the Sabbath?
16 Ashe wannan 'yar gidan Ibrahim, wanda shaidan ya daure ta shekara goma sha takwas, wato ba za a iya kwance ta a ranar Asabaci kenan ba?
But this woman, a daughter of Abraham, who has been kept in bondage by Satan for now eighteen years, ought not she to have been released from her bondage on the Sabbath?”
17 Da ya fada wadannan abubuwa, dukansu da suka yi adawa da shi suka kunyata, duk taron kuwa suka yi ta farin ciki da abubuwa masu daraja da yayi.
As he said this, his opponents all felt ashamed; but all the people rejoiced to see all the wonderful things that he was doing.
18 Sai Yesu ya ce, “Yaya za a misalta mulkin Allah, kuma da me zan kwatanta shi?
So Jesus said, “What is the kingdom of God like? And to what can I liken it?
19 Yananan kamar kwayar mastad, wanda wani mutum ya dauka ya jefa ta a lambunsa, ta kuma yi girma ta zama gagarumin itace, har tsuntsaye suka yi shekarsu a rassanta.”
It is like a mustard seed which a man took and put in his garden. The seed grew and became a tree, and the wild birds roosted in its branches.”
20 Ya sake cewa, “Da me zan kwatanta mulkin Allah?
And again Jesus said, “To what can I liken the kingdom of God?
21 Yana kamar yisti wanda wata mace ta dauka ta cuda da mudu uku na garin alkama don ya kumburar da shi.”
It is like some yeast which a woman took and covered in three pecks of flour, until the whole had risen.”
22 Yesu ya ziyarci kowanne birni da kauye, a hanyar sa ta zuwa Urushalima yana koyar da su.
Jesus went through towns and villages, teaching as he went, and making his way towards Jerusalem.
23 Sai wani ya ce masa, “Ubangiji, wadanda za su sami ceto kadan ne?” Sai ya ce masu,
“Master,” someone asked, “are there but few in the path of salvation?” And Jesus answered,
24 “Ku yi kokari ku shiga ta matsatsiyar kofa, domin na ce maku, mutane dayawa za su nemi shiga amma ba za su iya shiga ba.
“Strive to go in by the narrow door. Many, I tell you, will seek to go in, but they will not be able,
25 In dai maigida ya riga ya tashi ya rufe kofa, sannan za ku tsaya a waje kuna kwankwasa kofar kuna cewa, 'Ubangiji, Ubangiji, bari mu shiga ciki'. Sai ya amsa yace maku, 'Ni ban san ku ba ko daga ina ku ka fito.'
when once the master of the house has got up and shut the door, while you begin to say, as you stand outside and knock, ‘Sir, open the door for us.’ His answer will be – ‘I do not know where you come from.’
26 Sannan za ku ce, 'Mun ci mun sha a gabanka, ka kuma yi koyarwa a kan titunanmu.'
Then you will begin to say ‘We have eaten and drunk in your presence, and you have taught in our streets,’ and his reply will be –
27 Amma zai amsa ya ce, “Ina gaya maku, ban san ko daga ina ku ka fito ba, ku tafi daga wurina, dukanku masu aikata mugunta!'
‘I do not know where you come from. Leave my presence, all you who are living in wickedness.’
28 Za a yi kuka da cizon hakora a lokacin da kun ga Ibrahim, da Ishaku, da Yakubu da dukan annabawa a mulkin Allah amma ku-za a jefar da ku waje.
There, there will be weeping and grinding of teeth, when you see Abraham, Isaac, and Jacob, and all the prophets, in the kingdom of God, while you yourselves are being driven outside.
29 Za su zo daga gabas, yamma, kudu, da arewa, za su ci a teburin abinci a mulkin Allah.
People will come from East and West, and from North and South, and take their places at the banquet in the kingdom of God.
30 Ku san da wannan, na karshe za su zama na farko, na farko kuma za su zama na karshe.”
There are some who are last now who will then be first, and some who are first now who will then be last!”
31 Nan take, wadansu farisiyawa suka zo suka ce masa, “Ka tafi daga nan domin Hirudus yana so ya kashe ka.”
Just then some Pharisees came up to Jesus and said, “Go away and leave this place, for Herod wants to kill you.”
32 Yesu ya ce, “Ku tafi ku gaya wa dilan nan cewa, 'Duba, na fitar da aljanu, ina warkarwa yau da gobe, kuma a rana ta uku kuwa zan gama aiki na.'
But Jesus answered, “Go and say to that fox ‘Look you, I am driving out demons and will be completing cures today and tomorrow, and on the third day I will have done.’
33 Ko da kaka, dole ne in ci gaba da tafiyata yau, da gobe, da kuma jibi, don bai dace a kashe annabi nesa da Urushalima ba.
But today and tomorrow and the day after I must go on my way, because it cannot be that a prophet should meet his end outside Jerusalem.
34 Urushalima, Urushalima masu kisan annabawa, masu jifan wadanda aka aiko gare ku. Sau nawa ne ina so in tattara 'ya'yanki kamar yadda kaza take tattara 'ya'yanta a cikin fukafukanta, amma ba ki so wannan ba.
Jerusalem! Jerusalem! You who slays the prophets and stones the messengers sent to you – Oh, how often have I wished to gather your children around me, as a hen takes her brood under her wings, and you would not come!
35 Duba, an yashe gidanki. Ina kwa gaya maku ba za ku kara ganina ba sai ran da kuka ce, 'Albarka ta tabbata ga mai zuwa da sunan Ubangiji.'”
Verily your house is left to you desolate! And never, I tell you, will you see me, until you say – ‘Blessed is He who comes in the name of the Lord.’”

< Luka 13 >