< Luka 1 >

1 Mutane da dayawa sun yi kokarin rubutu akan abubuwan da suka cika a tsakaninmu,
Kad nu daudzi uzņēmušies sarakstīt stāstus par tām lietām, kas mūsu starpā tik tiešām notikušas,
2 kamar yanda suka danka mana su, wadanda tun daga farko suka zama shaidu da idanunsu kuma manzanni ne na sakon.
Tā kā tie mums ziņu devuši, kas no iesākuma paši tās redzējuši un Dieva vārda kalpi bijuši:
3 Sabili da haka, ni ma, bayan da na yi bincike da kyau akan yanayin wadannan abubuwa tun da farko na ga ya yi kyau in rubuta wadannan abubuwa bi da bi ya mafi girmaTiyofilas.
Tad arī man likās labi esam, ka es visas šīs lietas no pirmā gala it smalki izmeklējis, pēc kārtas tev sarakstu, mans mīļais Teofil,
4 Ya zama haka domin ka san gaskiyar abin da aka koya maka ne.
Ka tu vari atzīt to īsteno mācības patiesību, kas tev mācīta.
5 A cikin zamanin Hirudus, Sarkin Yahudiya, akwai wani firist mai suna Zakariya, daga yankin Abija. Matarsa daga cikin yaya mata na zuriyar Haruna ce, kuma sunan ta Alisabatu ne.
Hērodus, Jūdejas ķēniņa, laikā bija viens priesteris, vārdā Zaharija, no Abijas kārtas, un viņa sieva no Ārona meitām, un viņai vārds bija Elizabete.
6 Dukan su biyu masu adalci ne a gaban Allah; marasa zargi a tafiyarsu cikin dukan dokoki da farilan Ubangiji.
Un tie abi bija taisni Dieva priekšā, nenoziedzīgi staigādami iekš visiem Tā Kunga baušļiem un likumiem.
7 Amma ba su da da, domin Alisabatu ba ta haihuwa, kuma a wannan lokacin dukansu sun tsufa kwarai.
Un tiem nebija neviena bērna; jo Elizabete bija neauglīga, un tie abi jau bija piedzīvojuši labu vecumu.
8 Ya zama kuma a lokacin da Zakariya yana gaban Allah, yana yin hidimar sa ta firist bisa ga tsari da ka'idar aikinsa.
Bet notikās, viņam svēto priestera darbu Dieva priekšā darot savā pienākamā kārtā,
9 Bisa ga al'adar zaben firist da zai yi hidima, an zabe shi ta wurin kuri'a ya shiga cikin haikalin Ubangiji domin ya kona turare.
Tad pēc priesteru ieraduma viņam pienācās ieiet Tā Kunga namā un kvēpināt.
10 Dukan taron Jama'a suna addu'a a waje a sa'adda ake kona turaren.
Un viss ļaužu pulks ārā lūdza Dievu tai kvēpināšanas stundā.
11 A lokacin, mala'ikan Ubangiji ya bayana a gare shi yana tsaye a gefen daman bagadi na turaren.
Bet viņam Tā Kunga eņģelis parādījās, stāvēdams pie kvēpināšanas altāra labās puses.
12 Zakariya ya firgita sa'adda ya gan shi; tsoro ya kama shi.
Un Zaharija to redzēdams izbijās, un bailes tam uznāca.
13 Amma mala'ikan ya ce masa, “Kada ka ji tsoro, Zakariya, domin an ji addu'ar ka. Matar ka Alisabatu za ta haifa maka da. Za ka kira sunansa Yahaya.
Bet tas eņģelis uz to sacīja: “Nebīsties, Zaharija, jo tava lūgšana ir paklausīta, un tava sieva Elizabete dzemdēs dēlu, un tu viņa vārdu sauksi: Jānis.
14 Za ka yi murna da farin ciki, kuma da yawa za su yi murna da haifuwarsa.
Un tev būs prieks un līksmība, un daudzi par viņa piedzimšanu priecāsies.
15 Domin zai zama mai girma a gaban Ubangiji. Ba zai sha ruwan inabi ba ko wani abu mai sa maye, kuma zai cika da Ruhu Mai Tsarki tun daga cikin cikin mahaifiyarsa.
Jo viņš būs liels Tā Kunga priekšā, vīnu un stipru dzērienu viņš nedzers un vēl savas mātes miesās viņš taps piepildīts ar Svētu Garu.
16 Kuma mutanen Isra'ila da yawa za su juya zuwa ga Ubangiji Allahnsu.
Un viņš daudz no Israēla bērniem atgriezīs pie Tā Kunga, sava Dieva.
17 Zai yi tafiya a gaban Unbangiji a cikin ruhu da ikon Iliya. Zai yi haka domin ya juya zuciyar Ubanni zuwa ga 'ya'yansu, domin marasa biyayya su yi tafiya a cikin tafarkin adalai. Don ya shirya wa Ubangiji mutanen da aka shirya dominsa.”
Un viņš ies Viņa priekšā Elijas garā un spēkā, atgriezdams tēvu sirdis pie bērniem un neklausīgos pie taisno gudrības, Tam Kungam sataisīt gatavus ļaudis.”
18 Zakariya ya ce wa mala'ikan, “Ta yaya zan san wannan? Ga shi na tsufa kuma matata tana da shekaru da yawa.”
Un Zaharija sacīja uz to eņģeli: “Kā es to zināšu? Jo es esmu vecs, un mana sieva jau ir vecīga.”
19 Mala'ikan ya amsa ya ce masa, “Nine Jibra'ilu, wanda ke tsaye a gaban Allah. An aiko ni in gaya maka wannan labari mai dadi.
Un tas eņģelis atbildēja un uz to sacīja: “Es esmu Gabriēls, kas stāv Dieva priekšā, un esmu sūtīts ar tevi runāt un tev pasludināt šo prieka vēsti.
20 Kuma duba, za ka zama bebe, ba za ka iya magana ba, sai ran da wadannan abubuwa suka cika. Ya zama haka domin ba ka gaskanta da kalmomina ba, wadanda za su cika a daidai lokacin.”
Un redzi, tu tapsi mēms un nevarēsi runāt līdz tai dienai, kad šās lietas notiks, tāpēc ka tu neesi ticējis maniem vārdiem, kas notiks savā laikā.”
21 Sa'adda mutane suke jiran Zakariya. Sun yi mamaki yadda ya dauki lokaci sosai a cikin haikali.
Un tie ļaudis gaidīja uz Zahariju un brīnījās par viņa kavēšanos Dieva namā.
22 Amma da ya fita, bai iya yin magana da su ba. Sun gane da cewa ya ga wahayi lokacin da yake cikin haikali. Ya ci gaba da yi masu alamu, ba ya magana.
Un ārā iznācis tas nevarēja uz tiem runāt, un tie nomanīja, ka viņš Dieva namā bija redzējis kādu parādīšanu, un viņš tiem meta ar roku un palika mēms.
23 Ya zama bayan da kwanakin hidimarsa suka kare, ya tafi gidansa.
Un notikās, kad viņa kalpošanas dienas bija pabeigtas, tad viņš nogāja uz savām mājām.
24 Bayan kwanakin nan, matarsa Alisabatu ta samu juna biyu. Ta boye kanta har na watani biyar. Ta ce,
Un pēc šīm dienām Elizabete, viņa sieva, tapa grūta un paslēpās piecus mēnešus sacīdama:
25 “Wannan shi ne abin da Allah ya yi mani da ya dube ni domin ya dauke kunyata a gaban jama'a.”
“Tā Tas Kungs man ir darījis tanīs dienās, kad Viņš mani uzlūkojis, no manis atņemt manu kaunu starp cilvēkiem.”
26 A cikin watan ta na shidda, an aiki Mala'ika Jibra'ilu daga wurin Allah zuwa wani birni a Galili mai suna Nazarat,
Un sestā mēnesī eņģelis Gabriēls no Dieva tapa sūtīts uz Galilejas pilsētu ar vārdu Nacarete
27 zuwa ga wata budurwa wanda aka ba da ita ga wani mutum mai suna Yusufu. Shi dan zuriyar Dauda ne, kuma ana kiran budurwar Maryamu.
Pie jumpravas, kas bija saderēta vīram, kam vārds Jāzeps, no Dāvida cilts, un tās jumpravas vārds bija Marija.
28 Ya zo wurin ta ya ce, “A gaishe ki, ke da ki ke da tagomashi sosai! Ubangiji yana tare da ke.
Un pie tās ienācis tas eņģelis sacīja: “Esi sveicināta, tu apžēlotā, Tas Kungs ar tevi, tu augsti teicama starp sievām.”
29 Amma ta damu kwarai da wadannan kalmomi sai ta yi tunani ko wacce irin gaisuwa ce wannan.
Bet viņa to redzēdama iztrūkās par viņa valodu un domāja pie sevis, kas tā par sveicināšanu?
30 Mala'ikan ya ce mata, “Kada ki ji tsoro, Maryamu, domin kin samu tagomashi a wurin Allah.
Un tas eņģelis uz to sacīja: “Nebīsties, Marija, jo tu žēlastību esi atradusi pie Dieva.
31 Duba, za ki sami juna biyu, za ki haifi da. Za ki kira sunansa 'Yesu'.
Un redzi, tu tapsi grūta savās miesās un dzemdēsi Dēlu un sauksi Viņa vārdu: Jēzus.
32 Zai zama mai girma, kuma za a ce da shi Dan Allah Madaukaki. Ubangiji Allah zai ba shi kursiyin ubansa Dauda.
Tas būs liels un taps nosaukts Tā Visuaugstākā Dēls, un Dievs Tas Kungs Tam dos Viņa tēva Dāvida krēslu.
33 Zai yi mulkin dukkan gidan Yakubu har abada, kuma mulkinsa ba shi da iyaka.” (aiōn g165)
Un Viņš valdīs pār Jēkaba namu mūžīgi, un Viņa valstībai nebūs gals.” (aiōn g165)
34 Maryamu ta ce wa mala'ikan, “Yaya wannan zai faru, tun da shike ni ban san namiji ba?”
Bet Marija sacīja uz to eņģeli: “Kā lai tas notiek? Jo es no vīra nezinos.”
35 Mala'ikan ya amsa ya ce mata, “Ruhu Mai-tsarki zai sauko a kan ki, kuma ikon Madaukaki zai lullube ki. Sabili da haka, za a kira mai tsarkin da za ki haifa Dan Allah.
Un tas eņģelis atbildēja un uz to sacīja: “Tas Svētais Gars nāks pār tevi un Tā Visuaugstākā spēks tevi apēnos, tāpēc arī Tas Svētais, kas no tevis dzims, taps nosaukts Dieva Dēls.
36 Ki kuma duba, ga 'yar'uwarki Alisabatu ta samu juna biyu a tsufanta. Watannin ta shida kenan, ita wadda aka kira ta bakarariya.
Un redzi, Elizabete, tava radiniece, savā vecumā arīdzan ir grūta ar dēlu un iet tagad sestā mēnesī, kurai tāda slava, ka esot neauglīga.
37 Gama babu abin da ba shi yiwuwa a wurin Allah.”
Jo Dievam nekāda lieta nav neiespējama.”
38 Maryamu ta ce, “To, ni baiwar Ubangiji ce. Bari ya faru da ni bisa ga sakonka.” Sai mala'ikan ya bar ta.
Bet Marija sacīja: “Redzi, es esmu Tā Kunga kalpone, lai man notiek pēc tava vārda.” Un tas eņģelis no tās aizgāja.
39 Sai Maryamu ta tashi da sauri a cikin kwanakin nan, zuwa kasa mai duwatsu, zuwa wani birni a Yahudiya.
Un Marija cēlās tanīs dienās un steidzās iet pār tiem kalniem uz vienu pilsētu iekš Jūda,
40 Ta shiga gidan Zakariya ta kuma gai da Alisabatu.
Un iegāja Zaharijas namā un sveicināja Elizabeti.
41 Ya zama sa'adda Alisabatu ta ji gaisuwar Maryamu, sai dan da ke cikinta ya yi tsalle, an cika Alisabatu kuma da Ruhu Mai Tsarki.
Un notikās, kad Elizabete Marijas sveicināšanu dzirdēja, tad tas bērniņš uzlēca viņas miesās, un Elizabete tapa Svēta Gara pilna.
42 Ta daga murya, ta ce, “Mai albarka kike a cikin mata, kuma mai albarka ne dan cikinki.
Un viņa stiprā balsī sauca un sacīja: “Tu esi augsti teicama starp sievām un augsti teicams ir tavas miesas auglis.
43 Kuma don me ya faru da ni da uwar Ubangijina ta ziyarce ni?
Un kā tas man notiek, ka mana Kunga māte nāk pie manis?
44 Kuma duba, da na ji karar gaisuwan ki sai dan ciki na ya yi tsalle domin murna.
Jo redzi, tikko tavas sveicināšanas balss manās ausīs atskanēja, tad tas bērniņš manās miesās ar līksmību uzlēca.
45 Kuma mai albarka ce wadda ta gaskanta cewa abubuwan da aka alkawarta mata daga wurin Ubangiji za su cika.
Un svētīga tu, kas esi ticējusi, jo tas taps piepildīts, kas tev no Tā Kunga sacīts.”
46 Maryamu ta ce, “Zuciyata ta yabi Ubangiji,
Un Marija sacīja: “Mana dvēsele teic augsti To Kungu,
47 kuma ruhu na ya yi murna da Allah mai ceto na.”
Un mans gars priecājās par Dievu, manu Pestītāju.
48 Domin ya dubi kaskancin baiwarsa. Duba, daga yanzu, dukkan tsararraki za su ce da ni mai albarka.
Jo Viņš ir uzlūkojis savas kalpones zemību; redzi, no šī laika visi bērnu bērni mani teiks svētīgu.
49 Domin shi madaukaki ya yi mani manyan abubuwa, kuma sunansa Mai Tsarki ne.
Jo Tas Spēcīgais lielas lietas pie manis darījis; un svēts ir Viņa Vārds.
50 Jinkansa ya tabbata daga tsara zuwa tsara wadanda suke girmama shi.
Un Viņa žēlastība paliek uz radu radiem pie tiem, kas Viņu bīstas.
51 Ya nuna karfinsa da hannuwansa; ya warwatsa ma su girman kai game da tunanin zuciyarsu.
Viņš darījis varenus darbus ar Savu elkoni un izkaisījis, kas ir lieli savā sirds prātā.
52 Ya nakasar da magada daga kursiyoyinsu, ya kuma fifita nakasassu.
Viņš varenos nogrūdis no augstiem krēsliem, un pacēlis pazemīgos.
53 Ya ciyar da mayunwata da abubuwa masu kyau, amma ya aiki attajirai wofi.
Izsalkušos Viņš pildījis ar labumiem, un bagātos Viņš atstājis tukšus.
54 Ya ba da taimako ga bawan sa Isra'ila, domin ya tuna ya kuma nuna jinkai
Viņš uzņēmis Savu kalpu Israēli un pieminējis Savu žēlastību,
55 (kamar yanda ya fada wa ubaninmu) ga Ibrahim da zuriyarsa har abada.” (aiōn g165)
Kā Viņš runājis mūsu tēviem, Ābrahāmam un viņa bērniem mūžīgi.” (aiōn g165)
56 Maryamu ta zauna da Alisabatu tsawon watanni uku sai ta koma gidanta.
Un Marija palika pie tās kādus trīs mēnešus, pēc tam viņa atgriezās atpakaļ uz savām mājām.
57 Da lokaci yayi da Alisabatu za ta haifi danta, ta kuma haifi da namiji.
Un Elizabetes laiks nāca, ka tai bija dzemdēt, un viņa dzemdēja dēlu.
58 Makwabtanta da 'yan'uwanta sun ji cewa Ubangiji ya ribanbanya jinkansa akanta, sai suka yi murna tare da ita
Un viņas kaimiņi un radi dzirdēja, ka Tas Kungs lielu žēlastību pie tās bija darījis, un tie priecājās līdz ar viņu.
59 Ya zama akan rana ta takwas, sun zo domin a yi wa yaron kaciya. Da sun kira sunansa “Zakariya” kamar sunan ubansa,
Un notikās astotā dienā, tad tie nāca, to bērniņu apgraizīt, un pēc viņa tēva vārda to sauca Zahariju.
60 amma mahaifiyarsa ta amsa ta ce, “A'a, za a kira shi Yahaya.”
Un viņa māte atbildēja un sacīja: “Nē, bet to būs nosaukt Jānis.”
61 Suka ce mata, “Babu wani a cikin danginku wanda ake kira da wannan suna.”
Un tie viņai sacīja: “Neviena nav tavos rados, kam tāds vārds.”
62 Sun nuna alama ga ubansa bisa ga yanda ya ke so a rada masa suna.
Un tie prasīja zīmes no viņa tēva, kā viņš gribētu, lai to sauc.
63 Ubansa ya nemi a ba shi allon rubutu, sai ya rubuta, “Sunansa Yahaya.” Dukan su suka yi mamaki kwarai da wannan.
Un tas galdiņu prasījis rakstīja tā: viņa vārds ir Jānis. Par to visi brīnījās.
64 Nan take, sai bakinsa ya bude kuma harshensa ya saki. Ya yi magana ya kuma yabi Allah.
Un tūdaļ viņa mute atdarījās, un viņa mēle tapa atraisīta, un tas runāja, Dievu slavēdams.
65 Tsoro ya kama dukan wadanda suke zama kewaye da su. Sai labarin ya bazu cikin dukan kasar duwatsu ta Yahudiya.
Un izbailes uznāca visiem kaimiņiem, un visa šī lieta tapa zināma pa visiem Jūdu zemes kalniem.
66 Kuma dukan wadanda suka ji su, sun ajiye su a cikin zuciyarsu, suna cewa, “To me wannan yaro zai zama ne?” Domin hannun Ubangiji yana nan tare da shi.
Un visi, kas to dzirdēja, to ņēma pie sirds un sacīja: “Kas būs ar šo bērniņu? Jo Tā Kunga roka bija ar viņu.”
67 Ruhu Mai-tsarki ya cika mahaifinsa Zakariya sai ya yi anabci cewa,
Un viņa tēvs Zaharija tapa Svēta Gara pilns, sludināja un sacīja:
68 “Yabo ga Ubangiji, Allah na Isra'ila domin ya zo ya taimaki mutanen sa kuma ya yi aikin ceto domin su.”
“Slavēts ir Tas Kungs, Israēla Dievs, jo tas Savus ļaudis piemeklējis un pestījis.
69 Ya ta da kahon ceto dominmu daga gidan bawansa Dauda, daga zuriyar Dauda bawansa,
Un mums uzcēlis pestīšanas ragu Sava kalpa Dāvida namā.
70 kamar yadda ya fada ta bakin annabawansa tsarkaka tun zamanin zamanai. (aiōn g165)
Kā Tas pirmajos laikos runājis caur Savu svēto praviešu muti; (aiōn g165)
71 Zai kawo mana ceto daga magabtan mu da kuma daga hannun makiyanmu.
Ka Viņš mūs pestītu no mūsu ienaidniekiem un no visu to rokas, kas mūs ienīst;
72 Zai yi haka domin ya nuna jinkai ga ubaninmu ya kuma tuna da alkawarinsa mai tsarki,
Un parādītu žēlastību mūsu tēviem un pieminētu Savu svēto derību
73 rantsuwar da ya fada wa ubanmu Ibrahim.
Un to stipro solīšanu, ko Viņš mūsu tēvam Ābrahāmam ir zvērējis, mums dot,
74 Ya rantse zai yardar mana, bayan da an kubutar da mu daga hannun makiyanmu, mu bauta masa ba tare da tsoro ba,
Ka mēs, no savu ienaidnieku rokām pestīti, Viņam bez bailības kalpojam
75 a cikin tsarki da adalci a gabansa dukan kwanakin ranmu.
Iekš svētības un taisnības Viņa priekšā visu savu mūžu.
76 I, kai kuma, yaro, za a kira ka annabi na Madaukaki, domin za ka tafi gaban fuskar Ubangiji ka shirya hanyoyinsa, ka shirya mutane domin zuwansa,
Un tu, bērniņ, tapsi nosaukts tā Visuaugstākā pravietis; un tu Tam Kungam iesi priekšā, Viņa ceļus sataisīt,
77 domin ba mutanensa ilimin ceto ta wurin gafarar zunubansu.
Un Viņa ļaudīm dot pestīšanas atzīšanu uz grēku piedošanu,
78 Wannan zai faru ne domin girman jinkan Allahnmu, sabili da hasken rana daga bisa za ya zo wurinmu,
Mūsu Dieva sirsnīgas žēlastības dēļ caur ko tas auseklis no augstības mūs apraudzījis;
79 domin haskakawa akan wadanda ke zaune a cikin duhu da kuma cikin inuwar mutuwa. Zai yi hakan nan domin ya kiyaye kafafunmu zuwa hanyar salama.
Ka tas tiem atspīdētu, kas sēž tumsībā un nāves ēnā, un mūsu kājas atgrieztu uz miera ceļu.”
80 Yaron ya yi girma ya kuma zama kakkarfa a cikin ruhu, yana kuma cikin jeji sai ranar bayyanuwarsa ga Isra'ila.
Un tas bērniņš auga un garā stiprinājās, un bija tuksnesī līdz tai dienai, kad tas parādījās priekš Israēla ļaudīm.

< Luka 1 >