< Luka 1 >

1 Mutane da dayawa sun yi kokarin rubutu akan abubuwan da suka cika a tsakaninmu,
Vangi vachi vava liki ku vika i nswanelo lye kande lyezo indava zichi zive zuzilizwa mukati ketu,
2 kamar yanda suka danka mana su, wadanda tun daga farko suka zama shaidu da idanunsu kuma manzanni ne na sakon.
uvu vo vulyo mu vava zituheli mi avo kuzwila ku matangizo ivali impanki ni vahikana ve ñusa.
3 Sabili da haka, ni ma, bayan da na yi bincike da kyau akan yanayin wadannan abubuwa tun da farko na ga ya yi kyau in rubuta wadannan abubuwa bi da bi ya mafi girmaTiyofilas.
Cwale kwangu name ivali kuvoneka kuva hande - kuganisisa hande inzila ye indava yezo zintu kuzwila kuma tangizo - kuñola indava ye nswanelo yako iwe, Theophilus yo sepahala.
4 Ya zama haka domin ka san gaskiyar abin da aka koya maka ne.
Ili ku pangila kuti mwi zive vuniti vwezo zintu zimu va lutwa.
5 A cikin zamanin Hirudus, Sarkin Yahudiya, akwai wani firist mai suna Zakariya, daga yankin Abija. Matarsa daga cikin yaya mata na zuriyar Haruna ce, kuma sunan ta Alisabatu ne.
Muma zuva a Heroda, simwine wa Judeya ku vali kwina mu purisita we zina lya Zakariya, ya vali kuzwa kwi inkauhanyo ya Abija. Mwi hyavwe avali kuzwa kuvana vechi kazana va Arunì, Izina lyakwe ivali nji Elizabeta.
6 Dukan su biyu masu adalci ne a gaban Allah; marasa zargi a tafiyarsu cikin dukan dokoki da farilan Ubangiji.
Vonse vo vele vava shieme ha vusu vwa Ireza, ku kuteka zonse intaezo za Simwine.
7 Amma ba su da da, domin Alisabatu ba ta haihuwa, kuma a wannan lokacin dukansu sun tsufa kwarai.
Kono kana vavena mwana kakuli Elizabeta kana vena luzalo, mi hape vonse chi vava supele ahulu he iyi inako.
8 Ya zama kuma a lokacin da Zakariya yana gaban Allah, yana yin hidimar sa ta firist bisa ga tsari da ka'idar aikinsa.
Mi kuvezi kuchita kuti Zakaria avena mukwina kwa Ireza, kwi chilila ni kupanga iyo mintendo yovu purisita yava hewa mwi nswanelo ye inkauhanyo ya kwe.
9 Bisa ga al'adar zaben firist da zai yi hidima, an zabe shi ta wurin kuri'a ya shiga cikin haikalin Ubangiji domin ya kona turare.
Kuya ke chizo choku keta kuti njo zuhi mu purisita yese a tende, ava ketwa kwa loto kuti e njile mwi tempele ya Simwine kuti a hise minunkiso.
10 Dukan taron Jama'a suna addu'a a waje a sa'adda ake kona turaren.
Chonse chichava cha vantu chiva kwete ku lapela hanze heyo inako minunkiso iva hiswa.
11 A lokacin, mala'ikan Ubangiji ya bayana a gare shi yana tsaye a gefen daman bagadi na turaren.
Mi iñiloi lya Simwine livezi kuvoneka ha vusu vwake ni ku zimana ku vulyo vwe alutare ye minunkiso.
12 Zakariya ya firgita sa'adda ya gan shi; tsoro ya kama shi.
Zakaria ha muvona, ava tilimuki mi lyowa livezi hali.
13 Amma mala'ikan ya ce masa, “Kada ka ji tsoro, Zakariya, domin an ji addu'ar ka. Matar ka Alisabatu za ta haifa maka da. Za ka kira sunansa Yahaya.
Kono i ñiloi chi lya ti kwali, “sanzi uvi ni lyowa, Zakaria, kakuti intapelo yako iva tekwa. Mwi hyenu Elizabeta mwa pepe mwana o mwisisu. Kamu sumpe izina lyakwe Johani.
14 Za ka yi murna da farin ciki, kuma da yawa za su yi murna da haifuwarsa.
Ka muve ni ntabo ni kusanga, mi vangi vese va sangilile he mpepo yakwe.
15 Domin zai zama mai girma a gaban Ubangiji. Ba zai sha ruwan inabi ba ko wani abu mai sa maye, kuma zai cika da Ruhu Mai Tsarki tun daga cikin cikin mahaifiyarsa.
Kakuli mwave muntu mukando mu menso a Simwine. Sanzi na nywi i waine kapa zinywiwa zi kolete, mi mwe zule ni Luhuho lu Jolola ku zwilila mwi vumo li ba nyina.
16 Kuma mutanen Isra'ila da yawa za su juya zuwa ga Ubangiji Allahnsu.
Mi vantu vangi va Isiraele kava sandulwe kwali Simwine wavo Ireza.
17 Zai yi tafiya a gaban Unbangiji a cikin ruhu da ikon Iliya. Zai yi haka domin ya juya zuciyar Ubanni zuwa ga 'ya'yansu, domin marasa biyayya su yi tafiya a cikin tafarkin adalai. Don ya shirya wa Ubangiji mutanen da aka shirya dominsa.”
Mwa yende havusu bwe chifateho cha Simwine muluhuho ni ziho za Eliya. Mwa pange vovuti kupangila kuti a sandule inkulo za bashemi ve chikwame ku vana, ku pangila kuti vasa kuteki kava yende mu vutali vwa vantu va lukite - ku litukiseza kwa Simwine vantu valukisezwe iye.
18 Zakariya ya ce wa mala'ikan, “Ta yaya zan san wannan? Ga shi na tsufa kuma matata tana da shekaru da yawa.”
Zakariya cha wamba kwi ñiloi, “Ni wola kuzi ziva vule izi? kakuli chili ni Mukwame yo supele mi ni mwihyetu naye cho supele ahulu.
19 Mala'ikan ya amsa ya ce masa, “Nine Jibra'ilu, wanda ke tsaye a gaban Allah. An aiko ni in gaya maka wannan labari mai dadi.
Mi iñiloi chila mwi taba ni ku wamba kwali, “njime Gaburiyele yo zimene mwikwina Ireza.”Nivaka tumwa ku kwiza kuwamba nawe, kukuletela aa makande ma lotu.
20 Kuma duba, za ka zama bebe, ba za ka iya magana ba, sai ran da wadannan abubuwa suka cika. Ya zama haka domin ba ka gaskanta da kalmomina ba, wadanda za su cika a daidai lokacin.”
“Cwale uvone, mo tontole, kese uwole kuwamba heisi izuva izi zintu hese nizi pangahale. Ichi nji kuti kana uva zumini manzwi angu, ese e zuzilizwe he nako i swanezi.
21 Sa'adda mutane suke jiran Zakariya. Sun yi mamaki yadda ya dauki lokaci sosai a cikin haikali.
Cwale vantu vava lindile Zakariya. Vava komeketwe kakuli avali kwi kele inako ingi mwi tempele.
22 Amma da ya fita, bai iya yin magana da su ba. Sun gane da cewa ya ga wahayi lokacin da yake cikin haikali. Ya ci gaba da yi masu alamu, ba ya magana.
Kono haka zwa mo, kana vali ku wola ku wamba navo. Chiva bonisisa kuti ava voni i pono havali kwina mwi tempele. Ava zwili ku panga zi supo kuvali na shele u tontwele.
23 Ya zama bayan da kwanakin hidimarsa suka kare, ya tafi gidansa.
Ku vezi kuva kuti mazuva akwe oku tenda ha amana, cha yenda kwi nzuvo yakwe.
24 Bayan kwanakin nan, matarsa Alisabatu ta samu juna biyu. Ta boye kanta har na watani biyar. Ta ce,
Kuzwa aa mazuva, mwi hyavwe Elizabeta ava hi menzi ma hya. Avali zwisi ku vantu ka mwezi i hinda iyanza. Cha wamba,
25 “Wannan shi ne abin da Allah ya yi mani da ya dube ni domin ya dauke kunyata a gaban jama'a.”
“Izi za vani pangili Simwine ha vani loli ni chishemo ku pangila kuti a zwise maswavisisa angu ha vusu bwa bantu.”
26 A cikin watan ta na shidda, an aiki Mala'ika Jibra'ilu daga wurin Allah zuwa wani birni a Galili mai suna Nazarat,
Mu Mwezi we yanza ni kamwina, I ñiloi Gaburiyele liba tumwa ku zwa kwa Ireza kwi tolopo mwa Galileya i sumpwa Nazareta,
27 zuwa ga wata budurwa wanda aka ba da ita ga wani mutum mai suna Yusufu. Shi dan zuriyar Dauda ne, kuma ana kiran budurwar Maryamu.
kwa kamwale yaba vikilizwe ku mukwame we zina lya Josefa. A vali ku wila ku luzuvo lwa Davida, kamwale izina lyakwe i vali nji Maria.
28 Ya zo wurin ta ya ce, “A gaishe ki, ke da ki ke da tagomashi sosai! Ubangiji yana tare da ke.
Cheza kwali ni kuwamba, “Lumele, iwe yo shemuvitwe ahulu, Simwine wina nawe.”
29 Amma ta damu kwarai da wadannan kalmomi sai ta yi tunani ko wacce irin gaisuwa ce wannan.
Kono ava lyangene ahulu cha manzwi akwe, ava hupuli kuti iwola kuva mulumelisezo nzi uwu.
30 Mala'ikan ya ce mata, “Kada ki ji tsoro, Maryamu, domin kin samu tagomashi a wurin Allah.
Iñiloi chila wamba kwali, “Sanzi utiyi, Maria kakuli cho va wani chishemo ni Ireza.”
31 Duba, za ki sami juna biyu, za ki haifi da. Za ki kira sunansa 'Yesu'.
Mi u vwene, mo pange mwana mwi vumo mi mo pepe muswisu. Mo sumpe izina lyakwe “Jesu.”
32 Zai zama mai girma, kuma za a ce da shi Dan Allah Madaukaki. Ubangiji Allah zai ba shi kursiyin ubansa Dauda.
Mwa ve mukando mi mwa sumpwe kuti Mwana wa Sikwiwulu. Simwine Ireza mwa muhe chipula chavu simwine chika zwilila ku vasikulwe vave sikulwe Davida.
33 Zai yi mulkin dukkan gidan Yakubu har abada, kuma mulkinsa ba shi da iyaka.” (aiōn g165)
Mwa vuse inzubo ya Jakovo kuya kwile, mi kese kuve nima mani ku muvuso wakwe. (aiōn g165)
34 Maryamu ta ce wa mala'ikan, “Yaya wannan zai faru, tun da shike ni ban san namiji ba?”
Maria cha wamba kwi ñiloi, “Kai pangahale vule, kuvona kanini ku kopana ni mukwame?”,
35 Mala'ikan ya amsa ya ce mata, “Ruhu Mai-tsarki zai sauko a kan ki, kuma ikon Madaukaki zai lullube ki. Sabili da haka, za a kira mai tsarkin da za ki haifa Dan Allah.
Iñiloi chilye tava niku wamba kwali, Luhuho Lujolola ka lwize hako, miziho za Sikwiwulu ka zize hako. Cwale iye uzo yo jolola yenke yese apepwe mwa sumpwe Mwana wa Ireza.
36 Ki kuma duba, ga 'yar'uwarki Alisabatu ta samu juna biyu a tsufanta. Watannin ta shida kenan, ita wadda aka kira ta bakarariya.
Mi ubwene, mukwako Elizabeta naye aba pepi mwana o muswisu mu busupali. Uwu mwezi we yanza ni konke wali, uzo yabali kusumpwa kusa pepa.
37 Gama babu abin da ba shi yiwuwa a wurin Allah.”
Kakuli kakwina chese nichi sa woleki ni Ireza.
38 Maryamu ta ce, “To, ni baiwar Ubangiji ce. Bari ya faru da ni bisa ga sakonka.” Sai mala'ikan ya bar ta.
Maria chati “ubwene, ni muhikana wo mwanakazana wa Simwine.” Kuve vulyo kwangu kakuya che ñusa lyako. Mi iñiloi chilya musiya.
39 Sai Maryamu ta tashi da sauri a cikin kwanakin nan, zuwa kasa mai duwatsu, zuwa wani birni a Yahudiya.
Linu Maria ava vuki mwa awo mazuba, mi cha hwelela kuya kwi nkanda ye ziwulu, kwi tolopo mwa Judeya.
40 Ta shiga gidan Zakariya ta kuma gai da Alisabatu.
Ava yendi mwi nzuvo ya Zakariya mi chaka lumelisa Elizabeta.
41 Ya zama sa'adda Alisabatu ta ji gaisuwar Maryamu, sai dan da ke cikinta ya yi tsalle, an cika Alisabatu kuma da Ruhu Mai Tsarki.
Cwale kuva pangahali kuti Elizabeta ha zuwa mulumelisezo wa Maria, mbumbu mwi vumo lyakwe ava shili, mi Elizabeta ave zulwa Luhuho lu Jolola.
42 Ta daga murya, ta ce, “Mai albarka kike a cikin mata, kuma mai albarka ne dan cikinki.
Cha koza inzwi lyakwe ni kuwamba kaku huwa “Iwe njo fwiyoletwe mukati kavanakazi, mi ni muselo we vumo lyako ufuyoletwe.”
43 Kuma don me ya faru da ni da uwar Ubangijina ta ziyarce ni?
Mi chinzi hayi va pangahali kwangu kuti vanyina va Simwine wangu va swanela kwiza kwangu?
44 Kuma duba, da na ji karar gaisuwan ki sai dan ciki na ya yi tsalle domin murna.
Mu vwene, mulumo we ntumeliso zako ha ziza ku matwi angu, mbumbu yo wina mwi vumo lyangu ava shili nche intabo.
45 Kuma mai albarka ce wadda ta gaskanta cewa abubuwan da aka alkawarta mata daga wurin Ubangiji za su cika.
Mi uzo u fwiyoletwe yaba zumini kuti ka kuve ni kwizuzilizwa kwezo zintu ziva wambwa kwali ku zwilila kwa Simwine.
46 Maryamu ta ce, “Zuciyata ta yabi Ubangiji,
Maria cha wamba, “Luhuho lwangu lu temba Simwine”,
47 kuma ruhu na ya yi murna da Allah mai ceto na.”
mi luhuho lwangu lusanga mwe Ireza mutusi wangu.
48 Domin ya dubi kaskancin baiwarsa. Duba, daga yanzu, dukkan tsararraki za su ce da ni mai albarka.
Chaba loli ha mazimo avolele hansi a muhikana wakwe wo mwanakazana. Cwale mu vone, ku zwila hahanu onse masika ka a nisumpe kuti ni fwiyoletwe.
49 Domin shi madaukaki ya yi mani manyan abubuwa, kuma sunansa Mai Tsarki ne.
Kakuli iye yo wina ziho chavani pangili zintu zikando mi izina lyakwe li jolola.
50 Jinkansa ya tabbata daga tsara zuwa tsara wadanda suke girmama shi.
Chishemo chakwe chikalilile ku mahasi ni mahasi kwabo vamu tiya.
51 Ya nuna karfinsa da hannuwansa; ya warwatsa ma su girman kai game da tunanin zuciyarsu.
Chava tondezi ziho zakwe kache yanza: chaba hasani avo vavali kulikumuseza mihupulo ye nkulo zavo.
52 Ya nakasar da magada daga kursiyoyinsu, ya kuma fifita nakasassu.
Chava soheli hansi vaana vavene simwine vechi kwame ha vuyendisi vwavo. mi chava nyamuni avo ba mazimo mavi.
53 Ya ciyar da mayunwata da abubuwa masu kyau, amma ya aiki attajirai wofi.
Chave zuzi avo va fwile inzala ni zintu zilotu, kono va humite avava tumini kule niva sena chintu.
54 Ya ba da taimako ga bawan sa Isra'ila, domin ya tuna ya kuma nuna jinkai
Chava hi intuso kwa Isiraele muhikana wakwe, kupangila ku hupula ku tondeza chishemo
55 (kamar yanda ya fada wa ubaninmu) ga Ibrahim da zuriyarsa har abada.” (aiōn g165)
(mwava teli ku veshetu) kwa Aburahama niba mwi chilila kuya uko kusena mamanimani. (aiōn g165)
56 Maryamu ta zauna da Alisabatu tsawon watanni uku sai ta koma gidanta.
Maria ave kali ni Elizabeta ka miezi yo tatwe mi cha volela kwi nzuvo yakwe.
57 Da lokaci yayi da Alisabatu za ta haifi danta, ta kuma haifi da namiji.
Hanu inako chi iva sikite ya Elizabeta kuti ahwizumuke muchiche mi ava pepi mwanaswisu.
58 Makwabtanta da 'yan'uwanta sun ji cewa Ubangiji ya ribanbanya jinkansa akanta, sai suka yi murna tare da ita
Va vambene naye niva kwakwe vava zuwi kuti Simwine ava mutondenzi chishemo chakwe chikando kwali mi vava sangi naye.
59 Ya zama akan rana ta takwas, sun zo domin a yi wa yaron kaciya. Da sun kira sunansa “Zakariya” kamar sunan ubansa,
Hanu kuvezi kupangahala he zuva li hinda iyanza ni to tatwe vava kezi njeva muchite mupato muchiche. Ni vava musumpi “Zakariya,” ku zwila izina li vesi.
60 amma mahaifiyarsa ta amsa ta ce, “A'a, za a kira shi Yahaya.”
Kono va nyina chive tava ni kuwamba “Ne, mwa sumpwe Johani.”
61 Suka ce mata, “Babu wani a cikin danginku wanda ake kira da wannan suna.”
Chiva wamba kwali, “kakwina yenke mukati kava mwenu yo sumpwa keli zina.”
62 Sun nuna alama ga ubansa bisa ga yanda ya ke so a rada masa suna.
Vava pangi zi supo kuvesi kupangila kuti vesi ve zive muvavali kusakila kuti a hewe izina.
63 Ubansa ya nemi a ba shi allon rubutu, sai ya rubuta, “Sunansa Yahaya.” Dukan su suka yi mamaki kwarai da wannan.
Vesi chiba kumbila chiñolelo mi chiva ñola, “izina lyakwe nji Johani”. Vonse vava komokwa.
64 Nan take, sai bakinsa ya bude kuma harshensa ya saki. Ya yi magana ya kuma yabi Allah.
Haho vulyo kaholo kakwe kave yalulwa mi lulimi lwake luva lukululwa. Ava wambi niku lumba Ireza.
65 Tsoro ya kama dukan wadanda suke zama kewaye da su. Sai labarin ya bazu cikin dukan kasar duwatsu ta Yahudiya.
Lyowa livezi havo vavali kwi kala muma bali avo. Zonse izi zintu ziva twala monse mwi inkanda za ziwulu za Judeya.
66 Kuma dukan wadanda suka ji su, sun ajiye su a cikin zuciyarsu, suna cewa, “To me wannan yaro zai zama ne?” Domin hannun Ubangiji yana nan tare da shi.
Mi vonse vava vazuwi vava ziviki mwi nkulo zavo, kuwamba, “cwale uzu muhwile mwave chi?” Kakuli iyanza lya Simwine livena naye.
67 Ruhu Mai-tsarki ya cika mahaifinsa Zakariya sai ya yi anabci cewa,
Vesi Zakariya ave zwile ni Luhuho lu Jolola mi cha polofita, kuwamba,
68 “Yabo ga Ubangiji, Allah na Isra'ila domin ya zo ya taimaki mutanen sa kuma ya yi aikin ceto domin su.”
“Simwine a lumbwe, Ireza wa Isiraele, kakuli avezi kwiza ku tusa mi ava kwanisi kuvozekezwa kwa bantu bakwe”
69 Ya ta da kahon ceto dominmu daga gidan bawansa Dauda, daga zuriyar Dauda bawansa,
Chava tuzimikili luziya lwo kuhaza mwi nzuvo yo muhikana wakwe Davida,
70 kamar yadda ya fada ta bakin annabawansa tsarkaka tun zamanin zamanai. (aiōn g165)
hava wambi cha kaholo zama polofita va jolola bakwe va vena mwi nako ya kale kale. (aiōn g165)
71 Zai kawo mana ceto daga magabtan mu da kuma daga hannun makiyanmu.
Mwa lete vu hazo vuzwilila ku zila zetu mi ni ku mayanza avo batu toyete.
72 Zai yi haka domin ya nuna jinkai ga ubaninmu ya kuma tuna da alkawarinsa mai tsarki,
Mwa pange vovuti ku totendeza chishemo chakwe ku veshetu mi ni ku hupula ku jolola kwe ntumelelano yakwe,
73 rantsuwar da ya fada wa ubanmu Ibrahim.
ku lisumina kwava wambi kwa Aburahama ishe etu.
74 Ya rantse zai yardar mana, bayan da an kubutar da mu daga hannun makiyanmu, mu bauta masa ba tare da tsoro ba,
Ava sepisi kutuha kakuli tuba zwiswa muma yanza e zila zetu, katu mutendele niku sena lyowa,
75 a cikin tsarki da adalci a gabansa dukan kwanakin ranmu.
muku jolola ni muku shiama ha vusu bwake onse mazuva etu.
76 I, kai kuma, yaro, za a kira ka annabi na Madaukaki, domin za ka tafi gaban fuskar Ubangiji ka shirya hanyoyinsa, ka shirya mutane domin zuwansa,
Eni, nawe, mwana, mo sumpwe mupolofita wa Isiwulu, kakuti moye ha vusu bwe chifateho cha Simwine kuli tukisa inzila zakwe, ku lukisa bantu cha kukeza kwakwe,
77 domin ba mutanensa ilimin ceto ta wurin gafarar zunubansu.
kwiza kuha inzivo yo kuhazwa ku vantu vakwe kaku swalelwa kwa zivi zavo.
78 Wannan zai faru ne domin girman jinkan Allahnmu, sabili da hasken rana daga bisa za ya zo wurinmu,
Ichi kachi pangahale bakeñisa chishemo cha Ireza wetu, bakeñisa ke zuva lizwa kule lyese lize kuku tutusa.
79 domin haskakawa akan wadanda ke zaune a cikin duhu da kuma cikin inuwar mutuwa. Zai yi hakan nan domin ya kiyaye kafafunmu zuwa hanyar salama.
Ku venya havo ve kele mwi fifi navo vena mu munzunde we fu. Mwa pange vovuti kutondeza matende etu mwi nzila ye nkozo.
80 Yaron ya yi girma ya kuma zama kakkarfa a cikin ruhu, yana kuma cikin jeji sai ranar bayyanuwarsa ga Isra'ila.
Hanu mwana ava kuli niku kola mu luhuho, mi avena mumu zuka heisi izuva hali vonekisa kwa Isiraele.

< Luka 1 >