< Luka 1 >

1 Mutane da dayawa sun yi kokarin rubutu akan abubuwan da suka cika a tsakaninmu,
Vingi vitangile ukhuvikho vunonu amamenyu (simulizi) amamenyu galo ugukavombikhe kati yunyo,
2 kamar yanda suka danka mana su, wadanda tun daga farko suka zama shaidu da idanunsu kuma manzanni ne na sakon.
Nduvuvatupile ufwe, yufwe ukhuhuma khuvutengulilo twalolile na miho gito na vavombi va limenyu.
3 Sabili da haka, ni ma, bayan da na yi bincike da kyau akan yanayin wadannan abubuwa tun da farko na ga ya yi kyau in rubuta wadannan abubuwa bi da bi ya mafi girmaTiyofilas.
Pwu nayune, vwu nilolile vunonu uvutengulilo wa mbombo inchi nchoni ukuhuma khuvute ngulilo - nikwene lunonu kulyune ukhukhwandikila vunonu mhesimiwa fincho Theofilo.
4 Ya zama haka domin ka san gaskiyar abin da aka koya maka ne.
Inave vwinogwa ulumanye uvwa yihwe li vwa mbombo iyumanyile.
5 A cikin zamanin Hirudus, Sarkin Yahudiya, akwai wani firist mai suna Zakariya, daga yankin Abija. Matarsa daga cikin yaya mata na zuriyar Haruna ce, kuma sunan ta Alisabatu ne.
Mfigono fya Herode, umbaha va Yuta, ali pwa ukuhani yumo ale vi Sakhaliya, va khikolo kya Abiya. UU dala ahumile khyu kuvana va Haruni, ni litavwa lya mwene ale vi Elizabeti.
6 Dukan su biyu masu adalci ne a gaban Allah; marasa zargi a tafiyarsu cikin dukan dokoki da farilan Ubangiji.
Voni vale va yilweli kuvulongolo kwa Nguluve; valikugenda khisita lunoninoni mu ndagilo nchoni ncha Nguluve.
7 Amma ba su da da, domin Alisabatu ba ta haihuwa, kuma a wannan lokacin dukansu sun tsufa kwarai.
Khange savakhale nu mwana, ulwa khuva u sabati ale gumba, khange voni vala vagogolo fincho.
8 Ya zama kuma a lokacin da Zakariya yana gaban Allah, yana yin hidimar sa ta firist bisa ga tsari da ka'idar aikinsa.
Pwu lino yikhahumila ukhuva u sakhaliya ale va Nguluve, vwivomba imbombo ya vukuhani msamu ya mwene.
9 Bisa ga al'adar zaben firist da zai yi hidima, an zabe shi ta wurin kuri'a ya shiga cikin haikalin Ubangiji domin ya kona turare.
Ukhukongana nu lwiho ulwa khuhala vi kuhani alikhu uvi ya khave ivomba, vahalaga ni kura ukhwingile mmtembile ya Nguluve nu ukhufukhutila uvumba.
10 Dukan taron Jama'a suna addu'a a waje a sa'adda ake kona turaren.
Ikhipuga kyoni kya vanu lili kudova khunji unsikhi gwa kufukhutila uvumba.
11 A lokacin, mala'ikan Ubangiji ya bayana a gare shi yana tsaye a gefen daman bagadi na turaren.
Pwu usungwa va Nguluve akha ngumila nu khoima khunelyo khwu nekhelo ya khufukhutila.
12 Zakariya ya firgita sa'adda ya gan shi; tsoro ya kama shi.
Usakhelia akha dwada vu ambene uvudwanchi vukhagwila.
13 Amma mala'ikan ya ce masa, “Kada ka ji tsoro, Zakariya, domin an ji addu'ar ka. Matar ka Alisabatu za ta haifa maka da. Za ka kira sunansa Yahaya.
Pwu unsugwa akhambula akhata ulekhe ukhudwada, “Sakhaliya, ulwakhuva uludovo lwakho lupulikhikhe. UU ndala vakho uelisabeti ikhukhuholela umwana. Elifavwa lya mwene vukhumwilanya Yohana.
14 Za ka yi murna da farin ciki, kuma da yawa za su yi murna da haifuwarsa.
Vwiva nu luhekhelo nu khukimagila, khenye vingi vikhv khuhovokhele ukhu holiwa khumwene
15 Domin zai zama mai girma a gaban Ubangiji. Ba zai sha ruwan inabi ba ko wani abu mai sa maye, kuma zai cika da Ruhu Mai Tsarki tun daga cikin cikin mahaifiyarsa.
is ulwakhuva iva mbahahi pavulongolo pamiho ga mmbaha. Sakhanywinchage idivai na ikivinywa ikhikali, khange iva adigile nu mepo umbanche, ukhuma mwitumbu mwa mamaye.
16 Kuma mutanen Isra'ila da yawa za su juya zuwa ga Ubangiji Allahnsu.
Na vanu vingi va mu Israeli vi vipindukha kwa nkuludeva Unguluve va vene.
17 Zai yi tafiya a gaban Unbangiji a cikin ruhu da ikon Iliya. Zai yi haka domin ya juya zuciyar Ubanni zuwa ga 'ya'yansu, domin marasa biyayya su yi tafiya a cikin tafarkin adalai. Don ya shirya wa Ubangiji mutanen da aka shirya dominsa.”
Ihitage khuvulongolo khumiho ga Ntwa nu mepo na makha ga Eliya. Ayivomba evo ukhukilivula inumbula ya baba kwu vana, uvu savidwa yavitota nu luhala lwa avalinu vwa yihweli. Ayimba wvo ukhuvika kwa Ntwa avanu uvu vavikhwe khu nongwa ya mwene.”
18 Zakariya ya ce wa mala'ikan, “Ta yaya zan san wannan? Ga shi na tsufa kuma matata tana da shekaru da yawa.”
Sakhalia akambula usungwa, “Nikulumanyandakhekhe ukhulu manya eeli? Ulwakhuva une niligogolo na yu ndala vanga imgakha gya mwene givile mingi fincho.”
19 Mala'ikan ya amsa ya ce masa, “Nine Jibra'ilu, wanda ke tsaye a gaban Allah. An aiko ni in gaya maka wannan labari mai dadi.
Usung'wa akhambula akhata, “Une nene gabileli, uvikhwima pamiho ga Nguluve nikhasuhiwe kukhumbula, ukhukhugegela inongwa iyi inonu.
20 Kuma duba, za ka zama bebe, ba za ka iya magana ba, sai ran da wadannan abubuwa suka cika. Ya zama haka domin ba ka gaskanta da kalmomina ba, wadanda za su cika a daidai lokacin.”
Ulolage, sayawilola, vwivamye, sukhanchove mpaka isikhu yila yakhave yihumila. Yehumile ulwakhuva amamenyu ganyo yagihumila khunsikhi unonu.”
21 Sa'adda mutane suke jiran Zakariya. Sun yi mamaki yadda ya dauki lokaci sosai a cikin haikali.
Pwu lino avanu vali khugulila u Sakhalia. Walikudega ukhuta unsikhi gwoni ale mtembile.
22 Amma da ya fita, bai iya yin magana da su ba. Sun gane da cewa ya ga wahayi lokacin da yake cikin haikali. Ya ci gaba da yi masu alamu, ba ya magana.
Vwu ahumile khunji alikhulemwa ukhunchova na vene. Vakhalumanya ukhuta upile amagono fivi vwali mtembile, alikhupi vonesya mufihwano akhanchiga mye.
23 Ya zama bayan da kwanakin hidimarsa suka kare, ya tafi gidansa.
Yukhahumela ukhuta amanchuva ga vuvombi vwa mwene vuvusilile akhahega ukhuvuya khumiave.
24 Bayan kwanakin nan, matarsa Alisabatu ta samu juna biyu. Ta boye kanta har na watani biyar. Ta ce,
Usakheliya vu avuyile khumiave ukhuhuma khuvuvombi wa mwene mu tembile, uu dala va mwene va akhava nu luleme. Navope sakhahuma mu nyumba ya mwene khu mienchi gihano akhata,
25 “Wannan shi ne abin da Allah ya yi mani da ya dube ni domin ya dauke kunyata a gaban jama'a.”
“Ili lyu utwa avombile khulione upwa khandolile kwu vupendelelo ahenche isoni khuliune khange pamiho ga vanu.”
26 A cikin watan ta na shidda, an aiki Mala'ika Jibra'ilu daga wurin Allah zuwa wani birni a Galili mai suna Nazarat,
Pwu lino umwenchi ugwa ntunato gwa mimba gya Elisabeti, Unguluve akhambula unsung'wa Gabilieli ukhuhila ikhilunga khya Mgalilaya khu khwilangiwa Nasaleti,
27 zuwa ga wata budurwa wanda aka ba da ita ga wani mutum mai suna Yusufu. Shi dan zuriyar Dauda ne, kuma ana kiran budurwar Maryamu.
Khu ng'inja uvyalondwe nu gosi uvi ikhwilangiwa vi Yusufu. Umwene ale va khivumbu kho kya Ndaveli, khange ilifavwa lya g'inja uyu ale vi Ihaliya.
28 Ya zo wurin ta ya ce, “A gaishe ki, ke da ki ke da tagomashi sosai! Ubangiji yana tare da ke.
Akhincha khumwene nukhuta, “Nikukhuponia, uveve vyu pokhile uluhungu uluvaha! Untwa ahovwikhe nuve.”
29 Amma ta damu kwarai da wadannan kalmomi sai ta yi tunani ko wacce irin gaisuwa ce wannan.
Limo amamenyu ga Nsungwa ga nja nchiche nu khusifa ukhulumanya khekhi unusungwa akhatile nikhu khupoia (salaam) ukhuu nchakhudege khu mwene.
30 Mala'ikan ya ce mata, “Kada ki ji tsoro, Maryamu, domin kin samu tagomashi a wurin Allah.
Unsungwa akhambula, “Ulekhe ukhu dwadwa, Maliya, ulwakhuva vwupilile uhehungu ukhuhuma khwa Nguluve.
31 Duba, za ki sami juna biyu, za ki haifi da. Za ki kira sunansa 'Yesu'.
Khange lola, vwigega uheleme mulitumbu lyakho vwihola umwana. Nayuve yavukhumwilaga ilitavwa lyamwene vi 'Yisu.'
32 Zai zama mai girma, kuma za a ce da shi Dan Allah Madaukaki. Ubangiji Allah zai ba shi kursiyin ubansa Dauda.
Iva mmbaha ikwilangiwaga mwa ve khukhanya fincho. Utwa Unguluve ikhumpa ikhigoda ikhinyahwangulo ikya Ndaveli ubaha va mwene.
33 Zai yi mulkin dukkan gidan Yakubu har abada, kuma mulkinsa ba shi da iyaka.” (aiōn g165)
Ayilongoncha pa kyanya pa kwumbu kho kya Yakhobo myakha gyoni nu ludeva lwa mwene lwiva luchila vumalilo. (aiōn g165)
34 Maryamu ta ce wa mala'ikan, “Yaya wannan zai faru, tun da shike ni ban san namiji ba?”
Umaliya akhambula unsung'wa, ili lihumela ndekhekhi ulwakhuva sanegele nigone nu ng'osi uvi ave, nchaga?
35 Mala'ikan ya amsa ya ce mata, “Ruhu Mai-tsarki zai sauko a kan ki, kuma ikon Madaukaki zai lullube ki. Sabili da haka, za a kira mai tsarkin da za ki haifa Dan Allah.
Usung'wa akhamwanda nu khumbula, “Umepo umbalancho ikhwo khwinchela paliyuve pwu lina umbalanche uviyakhave iholiwa ayikhwi langivwa mwane va va Nguluve.
36 Ki kuma duba, ga 'yar'uwarki Alisabatu ta samu juna biyu a tsufanta. Watannin ta shida kenan, ita wadda aka kira ta bakarariya.
Pwu lola, uhekhulolwakho u Elisabeti alinuleme lwa mwana khu vutamo wa vugogolo vwa mwene. Ugu mwenchigwa sita khumwene, uvivalikhu ihwilanya igomba.
37 Gama babu abin da ba shi yiwuwa a wurin Allah.”
Uhwakhuva lisikhuli ilyo likhuntola Unguluve.”
38 Maryamu ta ce, “To, ni baiwar Ubangiji ce. Bari ya faru da ni bisa ga sakonka.” Sai mala'ikan ya bar ta.
Umaliya akhala, “Lola une nili mbombi va khidala va Nguluve. Ilakhe lwe yive vule vule khulione nduvo ilimenyu lyakho.” Pwu unsung'wa akhandekha.
39 Sai Maryamu ta tashi da sauri a cikin kwanakin nan, zuwa kasa mai duwatsu, zuwa wani birni a Yahudiya.
Pwu pafigono ifyo Umaliya akhahega khimbivi mbivi akhaluta khukhelunga khya twamba, khu jini gwa khilonga ya Yuta.
40 Ta shiga gidan Zakariya ta kuma gai da Alisabatu.
Khaluta mnyumba ya Sakhaliya nu khumponia Uelisabeti.
41 Ya zama sa'adda Alisabatu ta ji gaisuwar Maryamu, sai dan da ke cikinta ya yi tsalle, an cika Alisabatu kuma da Ruhu Mai Tsarki.
Pyu yikhahumila ukhuta Usabeti avile apolikhe uheponio mwene akhanchumba, nu Sabeti akhadiga umepo umbalenche.
42 Ta daga murya, ta ce, “Mai albarka kike a cikin mata, kuma mai albarka ne dan cikinki.
Akhatoncha ilimenyu lya mwene nu khunchova khulinyu ili vaha, “Usayivwe uve mumbadala, nu mwana uvyalimwitumbu lyakho asayivwe.
43 Kuma don me ya faru da ni da uwar Ubangijina ta ziyarce ni?
Khange yiva ndakhikhi kyulune ukhuva, mama va Nkuludeva vango ukhuta inche khulione?
44 Kuma duba, da na ji karar gaisuwan ki sai dan ciki na ya yi tsalle domin murna.
Ulwakhuva, likhavile lipulikhikhemu mbulukhutu nchango ilimenyu lya khuponia uve umwana mwandileme lyango akhanchumbo nu hehovokho.
45 Kuma mai albarka ce wadda ta gaskanta cewa abubuwan da aka alkawarta mata daga wurin Ubangiji za su cika.
Khange asayivwage dala uvi alikwidikha ukhuta vukhala vuhumila khuvumalilo vwa Nkhuludeva.”
46 Maryamu ta ce, “Zuciyata ta yabi Ubangiji,
Mariamu akasema, nafsi yangu inamsifu Bwana,
47 kuma ruhu na ya yi murna da Allah mai ceto na.”
Nu mepo yango yihovwikhile mwa Nguluve umpokhi vango.
48 Domin ya dubi kaskancin baiwarsa. Duba, daga yanzu, dukkan tsararraki za su ce da ni mai albarka.
Uhwa khuva alolile pasi pa mbombi va mwene udala. Lola, ukhuhuma lino ifipepo fyoni fikhunyi langaga insayiwa.
49 Domin shi madaukaki ya yi mani manyan abubuwa, kuma sunansa Mai Tsarki ne.
Ulwa khuva umwene ummanyi avombile imbombo imbaha khuliune, khulitavwa lya mwene ilivalenche.
50 Jinkansa ya tabbata daga tsara zuwa tsara wadanda suke girmama shi.
Uluhungu lwa mwene lutama khipaponi khipato khuvala avikhudwada umwene.
51 Ya nuna karfinsa da hannuwansa; ya warwatsa ma su girman kai game da tunanin zuciyarsu.
Avonisye amakha kwu khwa khivokho kya mwene; avahaselihimie vala ava likwiginie pa masago ga numbula yu vene.
52 Ya nakasar da magada daga kursiyoyinsu, ya kuma fifita nakasassu.
Avisinche pasi avana va vavaha ukhuhuma kwu fitamilo fya vene ifinya hvangulo nu khuvavikha kwu khyanya uvavale va pasi.
53 Ya ciyar da mayunwata da abubuwa masu kyau, amma ya aiki attajirai wofi.
Alikuvigusya avalininjala kwu finu ifinonu, pwu atayili avaswimile mavakho gene.
54 Ya ba da taimako ga bawan sa Isra'ila, domin ya tuna ya kuma nuna jinkai
Ahuminche uvutangile kwa Israeli umbombi va mwene, ukhukumbu kha ukhuvonesya uhihungu lwa mwene
55 (kamar yanda ya fada wa ubaninmu) ga Ibrahim da zuriyarsa har abada.” (aiōn g165)
(Nduvu anchovile kwa dada yetu) khwa Abrahamu ni khipapo kya mwene milele.” (aiōn g165)
56 Maryamu ta zauna da Alisabatu tsawon watanni uku sai ta koma gidanta.
Umaliya akhatama nu Elisabeti iminchi gidatu ndee pwa khavuya kwu nyumba ya mwene.
57 Da lokaci yayi da Alisabatu za ta haifi danta, ta kuma haifi da namiji.
Pwu lino unsikhi gukhavile guhege lile ugwa Elisabeti ukhuhola umwana udimi.
58 Makwabtanta da 'yan'uwanta sun ji cewa Ubangiji ya ribanbanya jinkansa akanta, sai suka yi murna tare da ita
Awambunchege na vahukhulolwe vakhapu likha umwu unkuludeva vwa kunchinche uluhunge hwa mwene, pwu vakhahovokha paninie nu mwene.
59 Ya zama akan rana ta takwas, sun zo domin a yi wa yaron kaciya. Da sun kira sunansa “Zakariya” kamar sunan ubansa,
Pwu yikhahumila ikhigono ikya nane ukhuta vali kwincha kwigida umwana. Yikhenong'ikwa ukhumwilanga ilitavwa lya mwene, “Zekaria,” Ukhuva liyavwa lya dada va mwene,
60 amma mahaifiyarsa ta amsa ta ce, “A'a, za a kira shi Yahaya.”
Pwa mama va mwene akhamula akhata, “Ate; ikwilangiwa Yohana.”
61 Suka ce mata, “Babu wani a cikin danginku wanda ake kira da wannan suna.”
Vakhambula, asikhuli nu via liyumo mukikolo kyako uviikwila ngiwa nilitawa ili.”
62 Sun nuna alama ga ubansa bisa ga yanda ya ke so a rada masa suna.
Vakhambombela ikhimanyilo udadaye ukhumbula umwene ukhuta alikunongwa ampe ilitavwa iliveni.
63 Ubansa ya nemi a ba shi allon rubutu, sai ya rubuta, “Sunansa Yahaya.” Dukan su suka yi mamaki kwarai da wannan.
Udadaye alikhunongwa ikbavo kya kwandika, pwu akhandikha, “Ilitavwa lya mwene vi Yohana.” Voni valikhudegu pa ili.
64 Nan take, sai bakinsa ya bude kuma harshensa ya saki. Ya yi magana ya kuma yabi Allah.
Unsikhi ndugu undomo kwa mwene gulichadinduliwa nu lulimi lwa mwene lulikukyega. Alikhunchova nu khuginia u Nguluve.
65 Tsoro ya kama dukan wadanda suke zama kewaye da su. Sai labarin ya bazu cikin dukan kasar duwatsu ta Yahudiya.
Uwudwanchi vukhevinchele voni uvuvatamaga paninie nevene. Imbimbo nchikhagenda ikhulunga kyoni ikya fyamba fya Yuta.
66 Kuma dukan wadanda suka ji su, sun ajiye su a cikin zuciyarsu, suna cewa, “To me wannan yaro zai zama ne?” Domin hannun Ubangiji yana nan tare da shi.
Pwu voni uvuvapulikhe vakha gavika munumbula ncha vene vita, “Umwana uyu viva ndekhekhi nela khekhi?” Ulwakhuva ikhivokho kya Nkuludeva khi khale nu mwene.
67 Ruhu Mai-tsarki ya cika mahaifinsa Zakariya sai ya yi anabci cewa,
Udadaye va Sakhaliya adigile umepo umbalanche nu khuhumya uvunyamalago, akhata,
68 “Yabo ga Ubangiji, Allah na Isra'ila domin ya zo ya taimaki mutanen sa kuma ya yi aikin ceto domin su.”
“Aginivwage Unkuludeva, Unguluve va Israeli, ulwakhuva atangile nu khuvombela uvapokhi vwa vanu va mwene.
69 Ya ta da kahon ceto dominmu daga gidan bawansa Dauda, daga zuriyar Dauda bawansa,
Atwimikile ulusuga lwa vupokhi mnyumba ya mbombi va mwene Undaveti, ukuhuhuma mkhikolo kya mbombi va mwene Undaveti,
70 kamar yadda ya fada ta bakin annabawansa tsarkaka tun zamanin zamanai. (aiōn g165)
Nduvu anchovvile kwu ndomo gwa va nyamalago va mwene uvulalepwo imisi khi ikya khatele. (aiōn g165)
71 Zai kawo mana ceto daga magabtan mu da kuma daga hannun makiyanmu.
Ikhutupokha khuvavivi vito nu khumyammavoko ga voni avikhutuvipila.
72 Zai yi haka domin ya nuna jinkai ga ubaninmu ya kuma tuna da alkawarinsa mai tsarki,
Ayivomba evwo ukhuvonesya ikisa khuva dada vito, nu khumbukha uhwidihano lwa mwene uluvalanche,
73 rantsuwar da ya fada wa ubanmu Ibrahim.
Ulwidiko ulwu anchovile kwa Abrahamu udada vito.
74 Ya rantse zai yardar mana, bayan da an kubutar da mu daga hannun makiyanmu, mu bauta masa ba tare da tsoro ba,
Akhidiga ukhugangancha ukhuta yiwesekhano ukhumbombela U Nguluve khesita vudwanchi, vwu tupokiwe ukhuma mumavokho ga vavivi veto.
75 a cikin tsarki da adalci a gabansa dukan kwanakin ranmu.
Mu vuvalanche nu vwa yehweli mbolongolo mmwene ifigono fyeto fyoni.
76 I, kai kuma, yaro, za a kira ka annabi na Madaukaki, domin za ka tafi gaban fuskar Ubangiji ka shirya hanyoyinsa, ka shirya mutane domin zuwansa,
Ena, na yuve mwana, vwikhwalaa ngivwa nyamalago va uvali khu kyanya fincho, ulwakhuva ayigendelaga mmbolongolo mwa Nkuludeva ukhuvavikhila injila, ukhuvavikha avanu ukhumulu pilila, umwene,
77 domin ba mutanensa ilimin ceto ta wurin gafarar zunubansu.
Ukhuvavula avanu ukhuta ya vipokhi vwa kwu njila ya khusyikheliwa imbivincha vene.
78 Wannan zai faru ne domin girman jinkan Allahnmu, sabili da hasken rana daga bisa za ya zo wurinmu,
Ili yalihumila ulwakhuva khisa kya Nguluve vito, ulwakhuva ilinehuva ukhuhuma khukhenya likhutinchela
79 domin haskakawa akan wadanda ke zaune a cikin duhu da kuma cikin inuwar mutuwa. Zai yi hakan nan domin ya kiyaye kafafunmu zuwa hanyar salama.
ukhuvala khuvala avitama mhisi na mnu mwafuli gwa vufwe ayivombavo ugalongoncha amalunde gitu kwu njila ya lunonchehencho.”
80 Yaron ya yi girma ya kuma zama kakkarfa a cikin ruhu, yana kuma cikin jeji sai ranar bayyanuwarsa ga Isra'ila.
Pwu, mwana ula akhavula nu khuva na makha mumepo pwa akatama mchagalawe mpakha ihincho lya khuhumila umwene khu Israeli.

< Luka 1 >