< Luka 1 >

1 Mutane da dayawa sun yi kokarin rubutu akan abubuwan da suka cika a tsakaninmu,
Many have taken on the work of putting together an account of the things that have been fulfilled among us,
2 kamar yanda suka danka mana su, wadanda tun daga farko suka zama shaidu da idanunsu kuma manzanni ne na sakon.
just as they were passed down to us by those who from the first were eyewitnesses and servants of the word.
3 Sabili da haka, ni ma, bayan da na yi bincike da kyau akan yanayin wadannan abubuwa tun da farko na ga ya yi kyau in rubuta wadannan abubuwa bi da bi ya mafi girmaTiyofilas.
So it seemed good to me also, because I have accurately investigated everything from the beginning, to write an orderly account for you, most excellent Theophilus,
4 Ya zama haka domin ka san gaskiyar abin da aka koya maka ne.
so that you might know the certainty of the things you have been taught.
5 A cikin zamanin Hirudus, Sarkin Yahudiya, akwai wani firist mai suna Zakariya, daga yankin Abija. Matarsa daga cikin yaya mata na zuriyar Haruna ce, kuma sunan ta Alisabatu ne.
In the days of Herod, king of Judea, there was a certain priest named Zechariah, from the division of Abijah. His wife was from the daughters of Aaron, and her name was Elizabeth.
6 Dukan su biyu masu adalci ne a gaban Allah; marasa zargi a tafiyarsu cikin dukan dokoki da farilan Ubangiji.
They were both righteous before God, obeying all the commandments and ordinances of the Lord.
7 Amma ba su da da, domin Alisabatu ba ta haihuwa, kuma a wannan lokacin dukansu sun tsufa kwarai.
But they had no child, because Elizabeth was barren, and they were both very old by this time.
8 Ya zama kuma a lokacin da Zakariya yana gaban Allah, yana yin hidimar sa ta firist bisa ga tsari da ka'idar aikinsa.
Now it came about that Zechariah was in God's presence, carrying out the priestly duties in the order of his division.
9 Bisa ga al'adar zaben firist da zai yi hidima, an zabe shi ta wurin kuri'a ya shiga cikin haikalin Ubangiji domin ya kona turare.
According to the customary way of choosing which priest would serve, he had been chosen by lot to enter into the temple of the Lord to burn incense.
10 Dukan taron Jama'a suna addu'a a waje a sa'adda ake kona turaren.
The whole crowd of people was praying outside at the hour when the incense was burned.
11 A lokacin, mala'ikan Ubangiji ya bayana a gare shi yana tsaye a gefen daman bagadi na turaren.
Now an angel of the Lord appeared to him and stood at the right side of the incense altar.
12 Zakariya ya firgita sa'adda ya gan shi; tsoro ya kama shi.
When Zechariah saw him, he was terrified and fear fell on him.
13 Amma mala'ikan ya ce masa, “Kada ka ji tsoro, Zakariya, domin an ji addu'ar ka. Matar ka Alisabatu za ta haifa maka da. Za ka kira sunansa Yahaya.
But the angel said to him, “Do not be afraid, Zechariah, because your prayer has been heard. Your wife Elizabeth will bear you a son. You will call his name John.
14 Za ka yi murna da farin ciki, kuma da yawa za su yi murna da haifuwarsa.
You will have joy and gladness, and many will rejoice at his birth.
15 Domin zai zama mai girma a gaban Ubangiji. Ba zai sha ruwan inabi ba ko wani abu mai sa maye, kuma zai cika da Ruhu Mai Tsarki tun daga cikin cikin mahaifiyarsa.
For he will be great in the sight of the Lord. He must never drink wine or strong drink, and he will be filled with the Holy Spirit from his mother's womb.
16 Kuma mutanen Isra'ila da yawa za su juya zuwa ga Ubangiji Allahnsu.
Many of the people of Israel will be turned to the Lord their God.
17 Zai yi tafiya a gaban Unbangiji a cikin ruhu da ikon Iliya. Zai yi haka domin ya juya zuciyar Ubanni zuwa ga 'ya'yansu, domin marasa biyayya su yi tafiya a cikin tafarkin adalai. Don ya shirya wa Ubangiji mutanen da aka shirya dominsa.”
He will go before the face of the Lord in the spirit and power of Elijah, to turn the hearts of the fathers to the children and the disobedient to the wisdom of the righteous—to make ready for the Lord a people prepared for him.”
18 Zakariya ya ce wa mala'ikan, “Ta yaya zan san wannan? Ga shi na tsufa kuma matata tana da shekaru da yawa.”
Zechariah said to the angel, “How can I know this? For I am an old man and my wife is very old.”
19 Mala'ikan ya amsa ya ce masa, “Nine Jibra'ilu, wanda ke tsaye a gaban Allah. An aiko ni in gaya maka wannan labari mai dadi.
The angel answered and said to him, “I am Gabriel, who stands in the presence of God. I was sent to speak to you, to bring you this good news.
20 Kuma duba, za ka zama bebe, ba za ka iya magana ba, sai ran da wadannan abubuwa suka cika. Ya zama haka domin ba ka gaskanta da kalmomina ba, wadanda za su cika a daidai lokacin.”
Behold! You will be silent, unable to speak, until the day these things take place. This is because you did not believe my words, which will be fulfilled at the right time.”
21 Sa'adda mutane suke jiran Zakariya. Sun yi mamaki yadda ya dauki lokaci sosai a cikin haikali.
Now the people were waiting for Zechariah. They were surprised that he was spending so much time in the temple.
22 Amma da ya fita, bai iya yin magana da su ba. Sun gane da cewa ya ga wahayi lokacin da yake cikin haikali. Ya ci gaba da yi masu alamu, ba ya magana.
But when he came out, he could not speak to them. They realized that he had seen a vision while he was in the temple. He kept on making signs to them and remained silent.
23 Ya zama bayan da kwanakin hidimarsa suka kare, ya tafi gidansa.
It came about that when the days of his service were over, he went to his house.
24 Bayan kwanakin nan, matarsa Alisabatu ta samu juna biyu. Ta boye kanta har na watani biyar. Ta ce,
After these days, his wife Elizabeth conceived and for five months she kept herself hidden. She said,
25 “Wannan shi ne abin da Allah ya yi mani da ya dube ni domin ya dauke kunyata a gaban jama'a.”
“This is what the Lord has done for me when he looked at me with favor in order to take away my shame before people.”
26 A cikin watan ta na shidda, an aiki Mala'ika Jibra'ilu daga wurin Allah zuwa wani birni a Galili mai suna Nazarat,
In the sixth month, the angel Gabriel was sent from God to a city in Galilee named Nazareth,
27 zuwa ga wata budurwa wanda aka ba da ita ga wani mutum mai suna Yusufu. Shi dan zuriyar Dauda ne, kuma ana kiran budurwar Maryamu.
to a virgin engaged to a man whose name was Joseph. He belonged to the house of David, and the virgin's name was Mary.
28 Ya zo wurin ta ya ce, “A gaishe ki, ke da ki ke da tagomashi sosai! Ubangiji yana tare da ke.
He came to her and said, “Greetings, you who are highly favored! The Lord is with you.”
29 Amma ta damu kwarai da wadannan kalmomi sai ta yi tunani ko wacce irin gaisuwa ce wannan.
But she was very confused by his words and she wondered what kind of greeting this could be.
30 Mala'ikan ya ce mata, “Kada ki ji tsoro, Maryamu, domin kin samu tagomashi a wurin Allah.
The angel said to her, “Do not be afraid, Mary, for you have found favor with God.
31 Duba, za ki sami juna biyu, za ki haifi da. Za ki kira sunansa 'Yesu'.
See, you will conceive in your womb and bear a son. You will call his name 'Jesus.'
32 Zai zama mai girma, kuma za a ce da shi Dan Allah Madaukaki. Ubangiji Allah zai ba shi kursiyin ubansa Dauda.
He will be great and will be called the Son of the Most High. The Lord God will give him the throne of his ancestor David.
33 Zai yi mulkin dukkan gidan Yakubu har abada, kuma mulkinsa ba shi da iyaka.” (aiōn g165)
He will reign over the house of Jacob forever, and there will be no end to his kingdom.” (aiōn g165)
34 Maryamu ta ce wa mala'ikan, “Yaya wannan zai faru, tun da shike ni ban san namiji ba?”
Mary said to the angel, “How will this happen, since I have not slept with any man?”
35 Mala'ikan ya amsa ya ce mata, “Ruhu Mai-tsarki zai sauko a kan ki, kuma ikon Madaukaki zai lullube ki. Sabili da haka, za a kira mai tsarkin da za ki haifa Dan Allah.
The angel answered and said to her, “The Holy Spirit will come upon you, and the power of the Most High will come over you. So the holy one to be born will be called the Son of God.
36 Ki kuma duba, ga 'yar'uwarki Alisabatu ta samu juna biyu a tsufanta. Watannin ta shida kenan, ita wadda aka kira ta bakarariya.
See, your relative Elizabeth has also conceived a son in her old age. This is the sixth month for her, she who was called barren.
37 Gama babu abin da ba shi yiwuwa a wurin Allah.”
For nothing will be impossible for God.”
38 Maryamu ta ce, “To, ni baiwar Ubangiji ce. Bari ya faru da ni bisa ga sakonka.” Sai mala'ikan ya bar ta.
Mary said, “See, I am the female servant of the Lord. Let it be for me according to your message.” Then the angel left her.
39 Sai Maryamu ta tashi da sauri a cikin kwanakin nan, zuwa kasa mai duwatsu, zuwa wani birni a Yahudiya.
Then Mary arose in those days and quickly went into the hill country, to a city in Judea.
40 Ta shiga gidan Zakariya ta kuma gai da Alisabatu.
She went into the house of Zechariah and greeted Elizabeth.
41 Ya zama sa'adda Alisabatu ta ji gaisuwar Maryamu, sai dan da ke cikinta ya yi tsalle, an cika Alisabatu kuma da Ruhu Mai Tsarki.
Now it happened that when Elizabeth heard Mary's greeting, the baby in her womb jumped, and Elizabeth was filled with the Holy Spirit.
42 Ta daga murya, ta ce, “Mai albarka kike a cikin mata, kuma mai albarka ne dan cikinki.
She raised her voice and said loudly, “Blessed are you among women, and blessed is the fruit of your womb.
43 Kuma don me ya faru da ni da uwar Ubangijina ta ziyarce ni?
Why has it happened to me that the mother of my Lord should come to me?
44 Kuma duba, da na ji karar gaisuwan ki sai dan ciki na ya yi tsalle domin murna.
For see, when the sound of your greeting came to my ears, the baby in my womb jumped for joy.
45 Kuma mai albarka ce wadda ta gaskanta cewa abubuwan da aka alkawarta mata daga wurin Ubangiji za su cika.
Blessed is she who believed that there would be a fulfillment of the things that were told her from the Lord.”
46 Maryamu ta ce, “Zuciyata ta yabi Ubangiji,
Mary said, “My soul praises the Lord,
47 kuma ruhu na ya yi murna da Allah mai ceto na.”
and my spirit has rejoiced in God my savior.
48 Domin ya dubi kaskancin baiwarsa. Duba, daga yanzu, dukkan tsararraki za su ce da ni mai albarka.
For he has looked at the low condition of his female servant. For see, from now on all generations will call me blessed.
49 Domin shi madaukaki ya yi mani manyan abubuwa, kuma sunansa Mai Tsarki ne.
For he who is mighty has done great things for me, and his name is holy.
50 Jinkansa ya tabbata daga tsara zuwa tsara wadanda suke girmama shi.
His mercy lasts from generation to generation for those who fear him.
51 Ya nuna karfinsa da hannuwansa; ya warwatsa ma su girman kai game da tunanin zuciyarsu.
He has displayed strength with his arm; he has scattered those who were proud about the thoughts of their hearts.
52 Ya nakasar da magada daga kursiyoyinsu, ya kuma fifita nakasassu.
He has thrown down princes from their thrones and he has raised up those of low condition.
53 Ya ciyar da mayunwata da abubuwa masu kyau, amma ya aiki attajirai wofi.
He has filled the hungry with good things, but the rich he has sent away empty.
54 Ya ba da taimako ga bawan sa Isra'ila, domin ya tuna ya kuma nuna jinkai
He has given help to Israel his servant, so as to remember to show mercy
55 (kamar yanda ya fada wa ubaninmu) ga Ibrahim da zuriyarsa har abada.” (aiōn g165)
(as he said to our fathers) to Abraham and his descendants forever.” (aiōn g165)
56 Maryamu ta zauna da Alisabatu tsawon watanni uku sai ta koma gidanta.
Mary stayed with Elizabeth about three months and then returned to her house.
57 Da lokaci yayi da Alisabatu za ta haifi danta, ta kuma haifi da namiji.
Now the time had come for Elizabeth to deliver her baby and she gave birth to a son.
58 Makwabtanta da 'yan'uwanta sun ji cewa Ubangiji ya ribanbanya jinkansa akanta, sai suka yi murna tare da ita
Her neighbors and her relatives heard that the Lord had shown his great mercy to her, and they rejoiced with her.
59 Ya zama akan rana ta takwas, sun zo domin a yi wa yaron kaciya. Da sun kira sunansa “Zakariya” kamar sunan ubansa,
Now it happened on the eighth day that they came to circumcise the child. They would have called him “Zechariah,” after the name of his father.
60 amma mahaifiyarsa ta amsa ta ce, “A'a, za a kira shi Yahaya.”
But his mother answered and said, “No. He will be called John.”
61 Suka ce mata, “Babu wani a cikin danginku wanda ake kira da wannan suna.”
They said to her, “There is no one among your relatives who is called by this name.”
62 Sun nuna alama ga ubansa bisa ga yanda ya ke so a rada masa suna.
They made signs to his father as to how he wanted him to be named.
63 Ubansa ya nemi a ba shi allon rubutu, sai ya rubuta, “Sunansa Yahaya.” Dukan su suka yi mamaki kwarai da wannan.
His father asked for a writing tablet and wrote, “His name is John.” They all were astonished at this.
64 Nan take, sai bakinsa ya bude kuma harshensa ya saki. Ya yi magana ya kuma yabi Allah.
Immediately his mouth was opened and his tongue was freed. He spoke and praised God.
65 Tsoro ya kama dukan wadanda suke zama kewaye da su. Sai labarin ya bazu cikin dukan kasar duwatsu ta Yahudiya.
Fear came on all who lived around them. All these matters were spread throughout all the hill country of Judea.
66 Kuma dukan wadanda suka ji su, sun ajiye su a cikin zuciyarsu, suna cewa, “To me wannan yaro zai zama ne?” Domin hannun Ubangiji yana nan tare da shi.
All who heard them stored them in their hearts, saying, “What then will this child become?” For the hand of the Lord was with him.
67 Ruhu Mai-tsarki ya cika mahaifinsa Zakariya sai ya yi anabci cewa,
His father Zechariah was filled with the Holy Spirit and prophesied, saying,
68 “Yabo ga Ubangiji, Allah na Isra'ila domin ya zo ya taimaki mutanen sa kuma ya yi aikin ceto domin su.”
“Praised be the Lord, the God of Israel, for he has come to help and he has accomplished redemption for his people.
69 Ya ta da kahon ceto dominmu daga gidan bawansa Dauda, daga zuriyar Dauda bawansa,
He has raised up a horn of salvation for us in the house of his servant David
70 kamar yadda ya fada ta bakin annabawansa tsarkaka tun zamanin zamanai. (aiōn g165)
(as he spoke by the mouth of his holy prophets from long ago), (aiōn g165)
71 Zai kawo mana ceto daga magabtan mu da kuma daga hannun makiyanmu.
salvation from our enemies and from the hand of all who hate us.
72 Zai yi haka domin ya nuna jinkai ga ubaninmu ya kuma tuna da alkawarinsa mai tsarki,
He will do this to show mercy to our fathers and to remember his holy covenant,
73 rantsuwar da ya fada wa ubanmu Ibrahim.
the oath that he spoke to Abraham our father.
74 Ya rantse zai yardar mana, bayan da an kubutar da mu daga hannun makiyanmu, mu bauta masa ba tare da tsoro ba,
He swore to grant to us that we, having been delivered out of the hand of our enemies, would serve him without fear,
75 a cikin tsarki da adalci a gabansa dukan kwanakin ranmu.
in holiness and righteousness before him all our days.
76 I, kai kuma, yaro, za a kira ka annabi na Madaukaki, domin za ka tafi gaban fuskar Ubangiji ka shirya hanyoyinsa, ka shirya mutane domin zuwansa,
Yes, and you, child, will be called a prophet of the Most High, for you will go before the face of the Lord to prepare his paths, to prepare people for his coming,
77 domin ba mutanensa ilimin ceto ta wurin gafarar zunubansu.
to give knowledge of salvation to his people by the forgiveness of their sins.
78 Wannan zai faru ne domin girman jinkan Allahnmu, sabili da hasken rana daga bisa za ya zo wurinmu,
This will happen because of the tender mercy of our God, because of which the sunrise from on high will come to help us,
79 domin haskakawa akan wadanda ke zaune a cikin duhu da kuma cikin inuwar mutuwa. Zai yi hakan nan domin ya kiyaye kafafunmu zuwa hanyar salama.
to shine on those who sit in darkness and in the shadow of death. He will do this to guide our feet into the path of peace.”
80 Yaron ya yi girma ya kuma zama kakkarfa a cikin ruhu, yana kuma cikin jeji sai ranar bayyanuwarsa ga Isra'ila.
Now the child grew and became strong in spirit, and he was in the wilderness until the day of his public appearance to Israel.

< Luka 1 >