< Luka 1 >

1 Mutane da dayawa sun yi kokarin rubutu akan abubuwan da suka cika a tsakaninmu,
To his Excellency, Theophilus. Many attempts have been already made to draw up an account of those events which have reached their conclusion among us,
2 kamar yanda suka danka mana su, wadanda tun daga farko suka zama shaidu da idanunsu kuma manzanni ne na sakon.
just as they were reported to us by those who from the beginning were eye-witnesses, and afterwards became bearers of the Message.
3 Sabili da haka, ni ma, bayan da na yi bincike da kyau akan yanayin wadannan abubuwa tun da farko na ga ya yi kyau in rubuta wadannan abubuwa bi da bi ya mafi girmaTiyofilas.
And, therefore, I also, since I have investigated all these events with great care from their very beginning, have resolved to write a connected history of them for you,
4 Ya zama haka domin ka san gaskiyar abin da aka koya maka ne.
in order that you may be able to satisfy yourself of the accuracy of the story which you have heard from the lips of others.
5 A cikin zamanin Hirudus, Sarkin Yahudiya, akwai wani firist mai suna Zakariya, daga yankin Abija. Matarsa daga cikin yaya mata na zuriyar Haruna ce, kuma sunan ta Alisabatu ne.
In the reign of Herod, King of Judea, there was a priest named Zechariah, who belonged to the Division called after Abijah. His wife, whose name was Elizabeth, was also a descendant of Aaron.
6 Dukan su biyu masu adalci ne a gaban Allah; marasa zargi a tafiyarsu cikin dukan dokoki da farilan Ubangiji.
They were both righteous people, who lived blameless lives, guiding their steps by all the commandments and ordinances of the Lord.
7 Amma ba su da da, domin Alisabatu ba ta haihuwa, kuma a wannan lokacin dukansu sun tsufa kwarai.
But they had no child, Elizabeth being barren; and both of them were advanced in years.
8 Ya zama kuma a lokacin da Zakariya yana gaban Allah, yana yin hidimar sa ta firist bisa ga tsari da ka'idar aikinsa.
One day, when Zechariah was officiating as priest before God, during the turn of his Division,
9 Bisa ga al'adar zaben firist da zai yi hidima, an zabe shi ta wurin kuri'a ya shiga cikin haikalin Ubangiji domin ya kona turare.
it fell to him by lot, in accordance with the practice among the priests, to go into the Temple of the Lord and burn incense;
10 Dukan taron Jama'a suna addu'a a waje a sa'adda ake kona turaren.
and, as it was the Hour of Incense, the people were all praying outside.
11 A lokacin, mala'ikan Ubangiji ya bayana a gare shi yana tsaye a gefen daman bagadi na turaren.
And an angel of the Lord appeared to him, standing on the right of the Altar of Incense.
12 Zakariya ya firgita sa'adda ya gan shi; tsoro ya kama shi.
Zechariah was startled at the sight and was awe-struck.
13 Amma mala'ikan ya ce masa, “Kada ka ji tsoro, Zakariya, domin an ji addu'ar ka. Matar ka Alisabatu za ta haifa maka da. Za ka kira sunansa Yahaya.
But the angel said to him: “Do not be afraid, Zechariah; your prayer has been heard, and your wife Elizabeth shall bear you a son, whom you shall call by the name John.
14 Za ka yi murna da farin ciki, kuma da yawa za su yi murna da haifuwarsa.
He shall be to you a joy and a delight; and many shall rejoice over his birth.
15 Domin zai zama mai girma a gaban Ubangiji. Ba zai sha ruwan inabi ba ko wani abu mai sa maye, kuma zai cika da Ruhu Mai Tsarki tun daga cikin cikin mahaifiyarsa.
For he shall be great in the sight of the Lord; he shall not drink any wine or strong drink, and he shall be filled with the Holy Spirit from the very hour of his birth,
16 Kuma mutanen Isra'ila da yawa za su juya zuwa ga Ubangiji Allahnsu.
and shall reconcile many of the Israelites to the Lord their God.
17 Zai yi tafiya a gaban Unbangiji a cikin ruhu da ikon Iliya. Zai yi haka domin ya juya zuciyar Ubanni zuwa ga 'ya'yansu, domin marasa biyayya su yi tafiya a cikin tafarkin adalai. Don ya shirya wa Ubangiji mutanen da aka shirya dominsa.”
He shall go before him in the spirit and with the power of Elijah, ‘to reconcile fathers to their children’ and the disobedient to the wisdom of the righteous, and so make ready for the Lord a people prepared for him.”
18 Zakariya ya ce wa mala'ikan, “Ta yaya zan san wannan? Ga shi na tsufa kuma matata tana da shekaru da yawa.”
“How can I be sure of this?” Zechariah asked the angel. “For I am an old man and my wife is advanced in years.”
19 Mala'ikan ya amsa ya ce masa, “Nine Jibra'ilu, wanda ke tsaye a gaban Allah. An aiko ni in gaya maka wannan labari mai dadi.
“I am Gabriel,” the angel answered, “who stand in the presence of God, and I have been sent to speak to you and to bring you this good news.
20 Kuma duba, za ka zama bebe, ba za ka iya magana ba, sai ran da wadannan abubuwa suka cika. Ya zama haka domin ba ka gaskanta da kalmomina ba, wadanda za su cika a daidai lokacin.”
And now you shall be silent and unable to speak until the day when this takes place, because you did not believe what I said, though my words will be fulfilled in due course.”
21 Sa'adda mutane suke jiran Zakariya. Sun yi mamaki yadda ya dauki lokaci sosai a cikin haikali.
Meanwhile the people were watching for Zechariah, wondering at his remaining so long in the Temple.
22 Amma da ya fita, bai iya yin magana da su ba. Sun gane da cewa ya ga wahayi lokacin da yake cikin haikali. Ya ci gaba da yi masu alamu, ba ya magana.
When he came out, he was unable to speak to them, and they perceived that he had seen a vision there. But Zechariah kept making signs to them, and remained dumb.
23 Ya zama bayan da kwanakin hidimarsa suka kare, ya tafi gidansa.
And, as soon as his term of service was finished, he returned home.
24 Bayan kwanakin nan, matarsa Alisabatu ta samu juna biyu. Ta boye kanta har na watani biyar. Ta ce,
After this his wife, Elizabeth, expecting to become a mother, lived in seclusion for five months.
25 “Wannan shi ne abin da Allah ya yi mani da ya dube ni domin ya dauke kunyata a gaban jama'a.”
“This is what the Lord has done for me,” she said, “now that he has deigned to take away the reproach under which I have been living.”
26 A cikin watan ta na shidda, an aiki Mala'ika Jibra'ilu daga wurin Allah zuwa wani birni a Galili mai suna Nazarat,
Six months later the angel Gabriel was sent from God to a town in Galilee called Nazareth,
27 zuwa ga wata budurwa wanda aka ba da ita ga wani mutum mai suna Yusufu. Shi dan zuriyar Dauda ne, kuma ana kiran budurwar Maryamu.
to a maiden there who was betrothed to a man named Joseph, a descendant of David. Her name was Mary.
28 Ya zo wurin ta ya ce, “A gaishe ki, ke da ki ke da tagomashi sosai! Ubangiji yana tare da ke.
Gabriel came into her presence and said: “Hail, you who have been highly favoured! The Lord is with you.”
29 Amma ta damu kwarai da wadannan kalmomi sai ta yi tunani ko wacce irin gaisuwa ce wannan.
Mary was much disturbed at his words, and was wondering to herself what such a greeting could mean,
30 Mala'ikan ya ce mata, “Kada ki ji tsoro, Maryamu, domin kin samu tagomashi a wurin Allah.
when the angel spoke again: “Do not be afraid, Mary, for you have found favour with God.
31 Duba, za ki sami juna biyu, za ki haifi da. Za ki kira sunansa 'Yesu'.
And now, you shall be with child and give birth to a son, and you shall give him the name Jesus.
32 Zai zama mai girma, kuma za a ce da shi Dan Allah Madaukaki. Ubangiji Allah zai ba shi kursiyin ubansa Dauda.
The child shall be great and shall be called ‘Son of the Most High,’ and the Lord God will give him the throne of his ancestor David,
33 Zai yi mulkin dukkan gidan Yakubu har abada, kuma mulkinsa ba shi da iyaka.” (aiōn g165)
and he shall reign over the descendants of Jacob for ever; And to his kingdom there shall be no end.” (aiōn g165)
34 Maryamu ta ce wa mala'ikan, “Yaya wannan zai faru, tun da shike ni ban san namiji ba?”
“How can this be?” Mary asked the angel. “For I have no husband.”
35 Mala'ikan ya amsa ya ce mata, “Ruhu Mai-tsarki zai sauko a kan ki, kuma ikon Madaukaki zai lullube ki. Sabili da haka, za a kira mai tsarkin da za ki haifa Dan Allah.
“The Holy Spirit shall descend upon you,” answered the angel, “and the Power of the Most High shall overshadow you; and therefore the child will be called ‘holy,’ and ‘Son of God.’
36 Ki kuma duba, ga 'yar'uwarki Alisabatu ta samu juna biyu a tsufanta. Watannin ta shida kenan, ita wadda aka kira ta bakarariya.
And Elizabeth, your cousin, is herself also expecting a son in her old age; and it is now the sixth month with her, though she is called barren;
37 Gama babu abin da ba shi yiwuwa a wurin Allah.”
for no promise from God shall fail to be fulfilled.”
38 Maryamu ta ce, “To, ni baiwar Ubangiji ce. Bari ya faru da ni bisa ga sakonka.” Sai mala'ikan ya bar ta.
“I am the servant of the Lord,” exclaimed Mary; “let it be with me as you have said.” Then the angel left her.
39 Sai Maryamu ta tashi da sauri a cikin kwanakin nan, zuwa kasa mai duwatsu, zuwa wani birni a Yahudiya.
Soon after this Mary set out, and made her way quickly into the hill-country, to a town in Judah;
40 Ta shiga gidan Zakariya ta kuma gai da Alisabatu.
and there she went into Zechariah’s house and greeted Elizabeth.
41 Ya zama sa'adda Alisabatu ta ji gaisuwar Maryamu, sai dan da ke cikinta ya yi tsalle, an cika Alisabatu kuma da Ruhu Mai Tsarki.
When Elizabeth heard Mary’s greeting, the child moved within her, and Elizabeth herself was filled with the Holy Spirit,
42 Ta daga murya, ta ce, “Mai albarka kike a cikin mata, kuma mai albarka ne dan cikinki.
and cried aloud: “Blessed are you among women, and blessed is your unborn child!
43 Kuma don me ya faru da ni da uwar Ubangijina ta ziyarce ni?
But how have I this honour, that the mother of my Lord should come to me?
44 Kuma duba, da na ji karar gaisuwan ki sai dan ciki na ya yi tsalle domin murna.
For, as soon as your greeting reached my ears, the child moved within me with delight!
45 Kuma mai albarka ce wadda ta gaskanta cewa abubuwan da aka alkawarta mata daga wurin Ubangiji za su cika.
Happy indeed is she who believed that the promise which she received from the Lord would be fulfilled.”
46 Maryamu ta ce, “Zuciyata ta yabi Ubangiji,
And Mary said: “My soul exalts the Lord,
47 kuma ruhu na ya yi murna da Allah mai ceto na.”
my spirit delights in God my Saviour;
48 Domin ya dubi kaskancin baiwarsa. Duba, daga yanzu, dukkan tsararraki za su ce da ni mai albarka.
for he has remembered his servant in her lowliness; And from this hour all ages will count me happy!
49 Domin shi madaukaki ya yi mani manyan abubuwa, kuma sunansa Mai Tsarki ne.
Great things has the Almighty done for me; And holy is his name.
50 Jinkansa ya tabbata daga tsara zuwa tsara wadanda suke girmama shi.
From age to age his mercy rests On those who reverence him.
51 Ya nuna karfinsa da hannuwansa; ya warwatsa ma su girman kai game da tunanin zuciyarsu.
Mighty are the deeds of his arm; He scatters the proud with their own devices,
52 Ya nakasar da magada daga kursiyoyinsu, ya kuma fifita nakasassu.
he casts down princes from their thrones, and the lowly he uplifts,
53 Ya ciyar da mayunwata da abubuwa masu kyau, amma ya aiki attajirai wofi.
the hungry he loads with gifts, and the rich he sends empty away.
54 Ya ba da taimako ga bawan sa Isra'ila, domin ya tuna ya kuma nuna jinkai
He has stretched out his hand to his servant Israel, Ever mindful of his mercy
55 (kamar yanda ya fada wa ubaninmu) ga Ibrahim da zuriyarsa har abada.” (aiōn g165)
(As he promised to our forefathers) For Abraham and his race for ever.” (aiōn g165)
56 Maryamu ta zauna da Alisabatu tsawon watanni uku sai ta koma gidanta.
Mary stayed with Elizabeth about three months, and then returned to her home.
57 Da lokaci yayi da Alisabatu za ta haifi danta, ta kuma haifi da namiji.
When Elizabeth’s time came, she gave birth to a son;
58 Makwabtanta da 'yan'uwanta sun ji cewa Ubangiji ya ribanbanya jinkansa akanta, sai suka yi murna tare da ita
and her neighbours and relations, hearing of the great goodness of the Lord to her, came to share her joy.
59 Ya zama akan rana ta takwas, sun zo domin a yi wa yaron kaciya. Da sun kira sunansa “Zakariya” kamar sunan ubansa,
A week later they met to circumcise the child, and were about to call him ‘Zechariah’ after his father,
60 amma mahaifiyarsa ta amsa ta ce, “A'a, za a kira shi Yahaya.”
when his mother interposed: “No, he is to be called John.”
61 Suka ce mata, “Babu wani a cikin danginku wanda ake kira da wannan suna.”
“You have no relation of that name!” they exclaimed;
62 Sun nuna alama ga ubansa bisa ga yanda ya ke so a rada masa suna.
and they made signs to the child’s father, to find out what he wished the child to be called.
63 Ubansa ya nemi a ba shi allon rubutu, sai ya rubuta, “Sunansa Yahaya.” Dukan su suka yi mamaki kwarai da wannan.
Asking for a writing-tablet, he wrote the words — ‘His name is John.’ Every one was surprised;
64 Nan take, sai bakinsa ya bude kuma harshensa ya saki. Ya yi magana ya kuma yabi Allah.
and immediately Zechariah recovered his voice and the use of his tongue, and began to bless God.
65 Tsoro ya kama dukan wadanda suke zama kewaye da su. Sai labarin ya bazu cikin dukan kasar duwatsu ta Yahudiya.
All their neighbours were awe-struck at this; and throughout the hill-country of Judea the whole story was much talked about;
66 Kuma dukan wadanda suka ji su, sun ajiye su a cikin zuciyarsu, suna cewa, “To me wannan yaro zai zama ne?” Domin hannun Ubangiji yana nan tare da shi.
and all who heard it kept it in mind, asking one another — “What can this child be destined to become?” For the Power of the Lord was with him.
67 Ruhu Mai-tsarki ya cika mahaifinsa Zakariya sai ya yi anabci cewa,
Then his father Zechariah was filled with the Holy Spirit, and, speaking under inspiration, said:
68 “Yabo ga Ubangiji, Allah na Isra'ila domin ya zo ya taimaki mutanen sa kuma ya yi aikin ceto domin su.”
“Blessed is the Lord, the God of Israel, Who has visited his people and wrought their deliverance,
69 Ya ta da kahon ceto dominmu daga gidan bawansa Dauda, daga zuriyar Dauda bawansa,
and has raised up for us the Strength of our Salvation In the House of his servant David —
70 kamar yadda ya fada ta bakin annabawansa tsarkaka tun zamanin zamanai. (aiōn g165)
As he promised by the lips of his Holy Prophets of old — (aiōn g165)
71 Zai kawo mana ceto daga magabtan mu da kuma daga hannun makiyanmu.
Salvation from our enemies and from the hands of all that hate us,
72 Zai yi haka domin ya nuna jinkai ga ubaninmu ya kuma tuna da alkawarinsa mai tsarki,
showing mercy to our forefathers, And mindful of his sacred Covenant.
73 rantsuwar da ya fada wa ubanmu Ibrahim.
This was the oath which he swore to our forefather Abraham —
74 Ya rantse zai yardar mana, bayan da an kubutar da mu daga hannun makiyanmu, mu bauta masa ba tare da tsoro ba,
That we should be rescued from the hands of our enemies,
75 a cikin tsarki da adalci a gabansa dukan kwanakin ranmu.
and should serve him without fear in holiness and righteousness, In his presence all our days.
76 I, kai kuma, yaro, za a kira ka annabi na Madaukaki, domin za ka tafi gaban fuskar Ubangiji ka shirya hanyoyinsa, ka shirya mutane domin zuwansa,
And thou, Child, shalt be called Prophet of the Most High, For thou shalt go before the Lord to make ready his way,
77 domin ba mutanensa ilimin ceto ta wurin gafarar zunubansu.
to give his people the knowledge of salvation In the forgiveness of their sins,
78 Wannan zai faru ne domin girman jinkan Allahnmu, sabili da hasken rana daga bisa za ya zo wurinmu,
through the tender mercy of our God, Whereby the Dawn will break on us from Heaven,
79 domin haskakawa akan wadanda ke zaune a cikin duhu da kuma cikin inuwar mutuwa. Zai yi hakan nan domin ya kiyaye kafafunmu zuwa hanyar salama.
to give light to those who dwell in darkness and the shadow of death, And guide our feet into the way of peace.”
80 Yaron ya yi girma ya kuma zama kakkarfa a cikin ruhu, yana kuma cikin jeji sai ranar bayyanuwarsa ga Isra'ila.
The child grew and became strong in spirit; and he lived in the Wilds till the time came for his appearance before Israel.

< Luka 1 >