< Galatiyawa 1 >

1 Wannan Bulus manzo ne. Manzancina kuwa, bai zo daga mutane ba ko mutum, amma ta wurin Yesu Almasihu da Allah Uba wanda da ya tashe shi daga matattu.
Paul, an apostle (not from men, neither through man, but through Jesus Christ, and God the Father, who raised him from the dead),
2 Ni da dukan 'yan'uwa da nake tare da su a nan, ina rubuto maku ku iklisiyoyi da ke a Galatiya.
and all the brethren which are with me, unto the churches of Galatia:
3 Alheri zuwa gare ku da salama daga Allah Ubanmu da kuma Ubangjinmu Yesu Almasihu,
Grace to you and peace from God the Father, and our Lord Jesus Christ,
4 wanda ya ba da kansa domin zunubanmu saboda ya kubutar da mu daga wannan mugun zamani, bisa ga nufin Allah da Ubanmu. (aiōn g165)
who gave himself for our sins, that he might deliver us out of this present evil world, according to the will of our God and Father: (aiōn g165)
5 Daukaka ta tabbata a gare shi har abada abadin. (aiōn g165)
to whom [be] the glory for ever and ever. Amen. (aiōn g165)
6 Na yi mamaki kwarai yadda kuka juya da sauri zuwa wata bishara daban. Na yi mamakin cewa kuna juyawa daga shi wanda ya kira ku ta wurin alherin Almasihu.
I marvel that ye are so quickly removing from him that called you in the grace of Christ unto a different gospel;
7 Ba wata bishara, amma akwai wadansu mutane da suke kawo maku rudani kuma suna so su gurbata bisharar Almasihu.
which is not another [gospel]: only there are some that trouble you, and would pervert the gospel of Christ.
8 Amma, ko da mu ne ko mala'ika daga sama ya yi maku shelar wata bishara ta daban da wadda muka yi shelar ta, la'ananne ne.
But though we, or an angel from heaven, should preach unto you any gospel other than that which we preached unto you, let him be anathema.
9 Kamar yadda muka fadi maku a da, yanzu kuma ina sake fada, “Idan wani ya yi maku shelar wata bishara ta daban da wadda kuka karba, la'ananne ne.”
As we have said before, so say I now again, If any man preacheth unto you any gospel other than that which ye received, let him be anathema.
10 To yanzu ina neman shaidar mutane ne ko Allah? Ina neman in gamshi mutane ne? Idan har yanzu ina kokarin in gamshi mutane ne, ni ba bawan Almasihu ba ne.
For am I now persuading men, or God? or am I seeking to please men? if I were still pleasing men, I should not be a servant of Christ.
11 Ina son ku sani fa 'yan'uwa, cewa bisharar da nake shelar ta ba daga mutane take ba.
For I make known to you, brethren, as touching the gospel which was preached by me, that it is not after man.
12 Ban karbe ta daga mutum ba, ba ma wanda ya koyar mani A maimakon haka, ta wurin wahayin Yesu Almasihu ne zuwa gare ni.
For neither did I receive it from man, nor was I taught it, but [it came to me] through revelation of Jesus Christ.
13 Kun riga kun ji game da rayuwa ta a da cikin Yahudanci, yadda da nake da kwazon tsananta wa iklisiyar Allah fiye da misali kuma ina lalatar da ita.
For ye have heard of my manner of life in time past in the Jews’ religion, how that beyond measure I persecuted the church of God, and made havock of it:
14 Ina gaba-gaba cikin Yahudanci fiye da yawancin tsararrakina. A kwazo kuwa fiye da kima game da al'adun ubannina.
and I advanced in the Jews’ religion beyond many of mine own age among my countrymen, being more exceedingly zealous for the traditions of my fathers.
15 Amma ya gamshi Allah ya zabe ni daga cikin mahaifiyata. Ya kira ni ta wurin alherinsa.
But when it was the good pleasure of God, who separated me, [even] from my mother’s womb, and called me through his grace,
16 Ya bayyana dansa a gareni, saboda in yi shelar sa cikin al'ummai. Nan da nan, ban nemi shawarar nama da jini ba
to reveal his Son in me, that I might preach him among the Gentiles; immediately I conferred not with flesh and blood:
17 kuma ban tafi Urushalima ba wurin wadanda suka zama manzanni kafin ni. Maimakon haka sai na tafi Arebiya, daga nan sai na dawo Dimashku.
neither went I up to Jerusalem to them which were apostles before me: but I went away into Arabia; and again I returned unto Damascus.
18 Bayan shekara uku na je Urushalima don in san Kefas, na zauna da shi na kwana goma sha biyar.
Then after three years I went up to Jerusalem to visit Cephas, and tarried with him fifteen days.
19 Amma ban ga ko daya daga cikin manzannin ba sai Yakubu kadai, dan'uwan Ubangiji.
But other of the apostles saw I none, save James the Lord’s brother.
20 Duba, a gaban Allah, ba karya nake yi ba cikin abin da na rubuta maku.
Now touching the things which I write unto you, behold, before God, I lie not.
21 Daga nan sai na je lardin Suriya da Kilikiya.
Then I came into the regions of Syria and Cilicia.
22 Har a lokacin babu wanda ya san ni a fuska a iklisiyoyin Yahudiya da suke cikin Almasihu,
And I was still unknown by face unto the churches of Judaea which were in Christ:
23 amma sai labari kawai suke ji, “Wanda a da yake tsananta mana yanzu yana shelar bangaskiyar da a da yake rusarwa.”
but they only heard say, He that once persecuted us now preacheth the faith of which he once made havock;
24 Suna ta daukaka Allah saboda ni.
and they glorified God in me.

< Galatiyawa 1 >