< Ayyukan Manzanni 5 >

1 Sai wani mai suna Hananiya da matarsa Safiratu, suka sayar da filinsu,
And a certain man, Ananias by name, with Sapphira his wife, sold a possession,
2 Hananiya kuwa ya boye wasu daga cikin kudin filin, (kuma da sanin matarsa), sa'annan suka kawo ragowar kudin a gaban manzannin.
and did keep back of the price — his wife also knowing — and having brought a certain part, at the feet of the apostles he laid [it].
3 Amma Bitrus ya ce, ''Hananiya don me shaidan ya cika zuciyarka, har ka yi wa Ruhu Mai Tsarki karya? Har ka boye wasu daga kudin filin?
And Peter said, 'Ananias, wherefore did the Adversary fill thy heart, for thee to lie to the Holy Spirit, and to keep back of the price of the place?
4 Sa'adda ba ka sayar da filin ba, ba mallakarka bane? Bayan da ka sayar ma, ba naka bane? Don me kayi irin wannan tunanin a zuciyarka? To ba mutane ka yi wa karya ba, Allah ka yi wa.”
while it remained, did it not remain thine? and having been sold, in thy authority was it not? why [is] it that thou didst put in thy heart this thing? thou didst not lie to men, but to God;'
5 Nan take da jin haka, Hananiya ya fadi ya ja numfashinsa na karshe. Dukan mutanen da suka ji labarin kuwa tsoro mai girma ya afko masu
and Ananias hearing these words, having fallen down, did expire, and great fear came upon all who heard these things,
6 Matasa suka zo suka nannade gawarsa, suka fitar da shi waje suka binne shi.
and having risen, the younger men wound him up, and having carried forth, they buried [him].
7 Bayan wajen sa'a uku, sai matarsa ta iso, ba tare da sanin abin da ya faru ba.
And it came to pass, about three hours after, that his wife, not knowing what hath happened, came in,
8 Sai Bitrus ya ce mata, ''ki gaya mini ko nawa kuka sayar da filin?'' Sai ta amsa, ''ta ce kaza ne.”
and Peter answered her, 'Tell me if for so much ye sold the place;' and she said, 'Yes, for so much.'
9 Sa'annan Bitrus ya ce mata, ''Don me kuka shirya wannan makidar tare da mijinki don ku gwada Ruhun Ubangiji? Kiji tafiyar wadanda suka bizne mijinki a bakin kofa, kuma za su dauke ki yanzu.''
And Peter said unto her, 'How was it agreed by you, to tempt the Spirit of the Lord? lo, the feet of those who did bury thy husband [are] at the door, and they shall carry thee forth;'
10 Nan take sai ta fadi a gabansa, ta ja numfashinta na karshe, matasan kuwa suka zo suka same ta ta mutu; sai suka dauki gawarta suka kai waje suka kuma bizne ta kusa da mijinta.
and she fell down presently at his feet, and expired, and the young men having come in, found her dead, and having carried forth, they buried [her] by her husband;
11 Tsoro mai girma kuwa ya afko wa iklisiyar gaba daya da dakan wadanda suka ji wadan nan al'amura.
and great fear came upon all the assembly, and upon all who heard these things.
12 Ayyukan alamu da ban mamaki masu yawa kuwa sun faru ga mutane, ta hannun manzannin. Dukansu kuma suna nan tare a dakalin Sulaimanu,
And through the hands of the apostles came many signs and wonders among the people, and they were with one accord all in the porch of Solomon;
13 Sai dai babu mai karfin halin ya hada kai tare dasu; amma suna da kwarjini sosai a gaban jama'a.
and of the rest no one was daring to join himself to them, but the people were magnifying them,
14 Har wa yau aka rika samun karin masu ba da gaskiya, dinbin jama'a, maza da mata,
(and the more were believers added to the Lord, multitudes both of men and women, )
15 har sukan dauki marasa lafiya su kai su bakin titi, suna kwantar da su a bisa gadaje da shinfidu, domin idan Bitrus ya zo wucewa ko da inuwarsa ma ta taba wasunsu.
so as into the broad places to bring forth the ailing, and to lay [them] upon couches and mats, that at the coming of Peter, even [his] shadow might overshadow some one of them;
16 Mutane dayawa kuwa sukan zo daga garuruwan da ke kewaye da Urushalima, suna kuma kawo masu rashin lafiya, da wadanda aljannu ke damunsu, aka kuma warkar da su duka.
and there were coming together also the people of the cities round about to Jerusalem, bearing ailing persons, and those harassed by unclean spirits — who were all healed.
17 Amma babban firist ya taso tare da duk wadanda ke tare da shi (wato 'yan darikar Sadukiyawa); suka cika da kishi matuka
And having risen, the chief priest, and all those with him — being the sect of the Sadducees — were filled with zeal,
18 suka kama manzannin suka kuma jefasu a kurkuku.
and laid their hands upon the apostles, and did put them in a public prison;
19 A cikin dare sai mala'ikan Ubangiji ya bude kofofin kurkukun ya kuma fito da su waje, ya ce,
and a messenger of the Lord through the night opened the doors of the prison, having also brought them forth, he said,
20 “Kuje ku tsaya a gaban haikali ku kuma gaya wa mutane maganar wannan rai.”
'Go on, and standing, speak in the temple to the people all the sayings of this life;'
21 Sa'adda suka ji haka, sai suka tafi haikalin da wayewar gari suka yi koyarwa. Amma babban firist da jama'arsa suka zo suka kuma kira taro da kuma dukan yan majalisa, da dattawan jama'ar Isra'ilawa suka fito suka kuma ba da umarni, a fito masu da manzannin.
and having heard, they did enter at the dawn into the temple, and were teaching. And the chief priest having come, and those with him, they called together the sanhedrim and all the senate of the sons of Israel, and they sent to the prison to have them brought,
22 Amma ma'aikatan da suka je kurkukun basu sami kowa, a kurkukunba, sai suka dawo suka ba da rahoto,
and the officers having come, did not find them in the prison, and having turned back, they told,
23 Su ka ce kurkukun a rufe gam da masu gadi suna nan a tsaye a bakin kofar amma da muka shiga, bamu sami kowa a ciki ba.
saying — 'The prison indeed we found shut in all safety, and the keepers standing without before the doors, and having opened — within we found no one.'
24 Yanzu sa'adda shugaban haikalin da manyan firistoci suka ji wadannan kalamai, sai suka rikice sosai game da su, suka ce yanzu me wannan zai haifar.
And as the priest, and the magistrate of the temple, and the chief priests, heard these words, they were doubting concerning them to what this would come;
25 Sai wani ya zo ya ce masu, ''Wadannan mutanen da kuka jefa a kurkuku suna can a cikin haikali suna koyar da jama'a.''
and coming near, a certain one told them, saying — 'Lo, the men whom ye did put in the prison are in the temple standing and teaching the people;'
26 Sai shugaban haikalin ya je da ma'aikatansa suka kawosu, ba tare da tashin hankali ba, domin gudun kada jama'a su jejjefesu.
then the magistrate having gone away with officers, brought them without violence, for they were fearing the people, lest they should be stoned;
27 Da suka kawo su, sai suka gabatar da su gaban majalisa, babban firist kuwa ya tuhume su,
and having brought them, they set [them] in the sanhedrim, and the chief priest questioned them,
28 cewa ''Ba mun yi maku kashedi da karfi kada ku yi koyarwa cikin wannan sunan ba? Amma ga shi duk kun cika Urushalima da koyarwarku, kuna kuma neman kusa jinin mutumin nan ya sauko kanmu.”
saying, 'Did not we strictly command you not to teach in this name? and lo, ye have filled Jerusalem with your teaching, and ye intend to bring upon us the blood of this man.'
29 Amma Bitrus da manzannin suka amsa suka ce, ''Dole mu yi wa Allah biyayya ba mutane ba.
And Peter and the apostles answering, said, 'To obey God it behoveth, rather than men;
30 Allah na ubanenmu ya ta da Yesu, wanda kuka kashe, ta wurin rateye shi a bisa itace,
and the God of our fathers did raise up Jesus, whom ye slew, having hanged upon a tree;
31 Allah kuwa ya daukaka shi a hannun damarsa, domin ya zama sarki da kuma mai ceto, ya ba Isra'ila tuba da gafarar zunubai.
this one God, a Prince and a Saviour, hath exalted with His right hand, to give reformation to Israel, and forgiveness of sins;
32 Mu kuwa shaidu ne ga wadannan al'amura, haka ma Ruhu Mai Tarki, wanda Allah ya bayar ga dukan wadanda suka yi biyayya a gareshi.''
and we are His witnesses of these sayings, and the Holy Spirit also, whom God gave to those obeying him.'
33 Da yan majalisa suka ji haka sai suka fusata kwarai da gaske, har suka nemi su kashe manzannin.
And they having heard, were cut [to the heart], and were taking counsel to slay them,
34 Amma wani Bafarise mai suna Gamaliel, malami ne kuma na attaura wanda dukan jama'a suna martabawa, sai ya mike ya ba da umarni cewa a fid da manzannin waje na dan lokaci.
but a certain one, having risen up in the sanhedrim — a Pharisee, by name Gamaliel, a teacher of law honoured by all the people — commanded to put the apostles forth a little,
35 Sai ya ce masu ''Ya ku mutanen Isra'ila, ku lura sosai da a binda kuke niyyar yi wa mutanen nan,
and said unto them, 'Men, Israelites, take heed to yourselves about these men, what ye are about to do,
36 A kwanakin baya wani ya zo mai suna Tudas ya dauki kansa wani abu, kimanin mutane dari hudu ne suka bishi, amma da aka kashe shi jama'arsa baki daya sai suka watse, ba wanda ya kara jin labarinsu.
for before these days rose up Theudas, saying, that himself was some one, to whom a number of men did join themselves, as it were four hundred, who was slain, and all, as many as were obeying him, were scattered, and came to nought.
37 Bayansa kuma, aka yi wani mai suna Yahuza na Galili wanda a kwanakin kidaya, ya zo ya rinjayi mutane da yawa, shima ya lalace, duk wadanda suka bi shi kuwa suka watse.
'After this one rose up, Judas the Galilean, in the days of the enrolment, and drew away much people after him, and that one perished, and all, as many as were obeying him, were scattered;
38 Don haka ina gaya maku ku rabu da mutanen nan, domin idan shirinsu ko kuma ayyukansu na mutane ne za su lalace.
and now I say to you, Refrain from these men, and let them alone, because if this counsel or this work may be of men, it will be overthrown,
39 Amnma idan abin nan daga Allah yake baza ku iya lalata su ba; kada ya zama kuna gaba da Allah.'' Sai suka rinjayu.
and if it be of God, ye are not able to overthrow it, lest perhaps also ye be found fighting against God.'
40 Da suka kira manzannin ciki suka yi masu duka, sai suka umarce su da cewa kada su sake koyarwa a cikin sunan Yesu, sai suka barsu suka tafi.
And to him they agreed, and having called near the apostles, having beaten [them], they commanded [them] not to speak in the name of Jesus, and let them go;
41 Suka fita daga cikin majalisar, suna murna domin sun cancanta su sha wulakanci saboda sunan.
they, indeed, then, departed from the presence of the sanhedrim, rejoicing that for his name they were counted worthy to suffer dishonour,
42 Bayan haka kullayomin suna zuwa haikali, suna bi gida gida, suna wa'azi, suna kuma koyarwa ba fasawa cewa Yesu shine Almasihu.
every day also in the temple, and in every house, they were not ceasing teaching and proclaiming good news — Jesus the Christ.

< Ayyukan Manzanni 5 >