< Ayyukan Manzanni 3 >

1 Sa'adda Bitrus da Yahaya suna hanya zuwa haikali a lokacin addu'ar karfe uku.
And Peter and John were going up at the same time to the temple, at the hour of the prayer, the ninth [hour],
2 Wani mutum, gurgu ne tun daga haihuwa, ana daukar sa kulluyomi zuwa kofar haikali da ake kira Kyakkyawa, domin bara gun mutanen da ke shiga haikalin.
and a certain man, being lame from the womb of his mother, was being carried, whom they were laying every day at the gate of the temple, called Beautiful, to ask a kindness from those entering into the temple,
3 Da ya ga Bitrus da Yahaya suna shiga haikalin, sai ya roke su sadaka.
who, having seen Peter and John about to go into the temple, was begging to receive a kindness.
4 Bitrus da Yahaya kuwa suka zuba masa ido, Bitrus ya ce, ''Ka dube mu.''
And Peter, having looked stedfastly toward him with John, said, 'Look toward us;'
5 Gurgun nan kuwa ya dube su, yana tsammanin zai sami wani abu a wurin su.
and he was giving heed to them, looking to receive something from them;
6 Amma Bitrus ya ce, “Azurfa da Zinariya ba ni da su, amma abin da nake da shi, zan baka. A cikin sunan Yesu Almasihu Banazare, Yi tafiya''
and Peter said, 'Silver and gold I have none, but what I have, that I give to thee; in the name of Jesus Christ of Nazareth, rise up and be walking.'
7 Bitrus ya kama hannun damarsa, ya daga shi; nan da nan kafafunsa da kashin idon sawayensa suka samu karfi.
And having seized him by the right hand, he raised [him] up, and presently his feet and ankles were strengthened,
8 Da gurgun ya yunkura, ya mike tsaye sai ya fara takawa; ya shiga haikali tare da Bitrus da Yahaya, yana takawa, yana tsalle, yana kuma girmama Allah.
and springing up, he stood, and was walking, and did enter with them into the temple, walking and springing, and praising God;
9 Dukan mutane suka gan shi yana tafiya yana kuma yabon Allah.
and all the people saw him walking and praising God,
10 Sun lura cewa, shine mutumin da ke zama yana bara a Kyakyawar kofar haikali; sai suka cika da mamaki domin abin da ya faru.
they were knowing him also that this it was who for a kindness was sitting at the Beautiful gate of the temple, and they were filled with wonder and amazement at what hath happened to him.
11 Yayin da yake rike da Bitrus da Yahaya, dukan jama'a suka matso wurinsu, a gefen dakalin Sulaimanu, suna ta mamaki kwarai.
And at the lame man who was healed holding Peter and John, all the people ran together unto them in the porch called Solomon's — greatly amazed,
12 Da Bitrus ya ga haka ya amsa wa jama'ar, “Ya ku mutanen Isra'ila, don me ku ke mamaki?” Don me ku ka zura mana ido, kamar mu ne muka sa shi ya yi tafiya da ikon kanmu ko adalcin mu?
and Peter having seen, answered unto the people, 'Men, Israelites! why wonder ye at this? or on us why look ye so earnestly, as if by our own power or piety we have made him to walk?
13 Allah na Ibrahim, da Ishaku, da Yakubu, Allah na iyayenmu ya girmama bawansa Yesu. Shi kuka ki kun kuma bashe shi a gaban Bilatus da ya so ya sake shi.
'The God of Abraham, and of Isaac, and of Jacob, the God of our fathers, did glorify His child Jesus, whom ye delivered up, and denied him in the presence of Pilate, he having given judgment to release [him],
14 Kuka ki Mai Tsarkin nan, Mai Adalcin, maimakon haka kuka ce a sakkar maku mai kisan kai.
and ye the Holy and Righteous One did deny, and desired a man — a murderer — to be granted to you,
15 Kun kashe mai ba da rai, wanda Allah ya tayar daga matattu, mu kuwa shaidu ne ga wannan al'amari.
and the Prince of the life ye did kill, whom God did raise out of the dead, of which we are witnesses;
16 Yanzu, ta bangaskiya ga sunansa - wannan mutum da kuke gani kuma kun san shi - ta wurin wannan sunan ne ya sami karfi. Bangaskiya cikin Yesu ta ba shi cikakkiyar lafiya, a gabanku duka.
and on the faith of his name, this one whom ye see and have known, his name made strong, even the faith that [is] through him did give to him this perfect soundness before you all.
17 Ya ku 'yan'uwa, na san kun yi haka ne cikin rashin sani, yadda shugabaninku suka yi.
'And now, brethren, I have known that through ignorance ye did [it], as also your rulers;
18 Amma duk abubuwan da Allah ya fada ta bakin dukan anabawansa, cewa Almasihunsa zai sha wahala, yanzu ya cika.
and God, what things before He had declared through the mouth of all His prophets, that the Christ should suffer, He did thus fulfil;
19 Saboda haka, Ku tuba, ku juyo, domin a shafe zunubanku, domin lokacin sabuntuwa daga wurin Ubangiji ya zo;
reform ye, therefore, and turn back, for your sins being blotted out, that times of refreshing may come from the presence of the Lord,
20 domin a aiko maku da Almasihu wanda aka kaddara wato, Yesu.
and He may send Jesus Christ who before hath been preached to you,
21 Shine wanda dole sama ta karbe shi har zuwa lokacin komo da dukan abubuwa, game da abubuwan da Allah ya fada tun da ta bakin annabawansa tsarkaka. (aiōn g165)
whom it behoveth heaven, indeed, to receive till times of a restitution of all things, of which God spake through the mouth of all His holy prophets from the age. (aiōn g165)
22 Musa hakika ya ce, 'Ubangiji Allah zai tayar maku da wani annabi kamar ni daga cikin, 'yan'uwanku. Za ku saurari dukan abin da zai fada maku.
'For Moses, indeed, unto the fathers said — A prophet to you shall the Lord your God raise up out of your brethren, like to me; him shall ye hear in all things, as many as he may speak unto you;
23 Zai kasance kowanne mutum da bai saurari annabin nan ba za a kau da shi gabadaya daga cikin mutanensa.'
and it shall be, every soul that may not hear that prophet shall be utterly destroyed out of the people;
24 I, dukan annabawa tun daga Sama'ila da wadanda suka zo bayansa, sun yi magana sun ambaci wadannan kwanaki.
and also all the prophets from Samuel and those following in order, as many as spake, did also foretell of these days.
25 Kune 'ya'yan annabawa da na alkawari wanda Allah ya yi da kakanninku, yadda ya ce wa Ibrahim, 'Daga zuriyarka dukan al'uman duniya za su sami albarka.'
'Ye are sons of the prophets, and of the covenant that God made unto our fathers, saying unto Abraham: And in thy seed shall be blessed all the families of the earth;
26 Bayan da Allah ya ta da bawansa, a gareku ne ya fara aiko shi, domin ya albarkace ku tawurin juyadda kowannenku daga muguntarsa.”
to you first, God, having raised up His child Jesus, did send him, blessing you, in the turning away of each one from your evil ways.'

< Ayyukan Manzanni 3 >