< Ayyukan Manzanni 21 >

1 Da muka rabu da su, muka shiga jirgin ruwa muka mike hanya zuwa birnin Kos, washegari sai birnin Rodusa, daga nan sai kuma zuwa birnin Batara.
In pripetilo se je, da potem, ko smo odšli od njih in odrinili, smo z ravno smerjo prispeli na Kos in naslednji dan na Rodos in od tam v Pátaro,
2 Da muka sami jirgi mai hayewa zuwa Fonisiya sai muka shiga.
in ko smo našli ladjo, ki je jadrala preko do Fenikije, smo se vkrcali in odpotovali.
3 Da muka hango tsibirin Kubrus muka bar shi a hagun mu muka nufi Suriya, muka sauka a birnin Taya domin a nan ne jirgin ruwan zai sauke kayansa.
Torej ko smo odkrili Ciper, smo ga pustili na levi roki in odjadrali v Sirijo ter pristali v Tiru, kajti tam je ladja iztovorila svoj tovor.
4 Bayan mun sami almajirai sai muka zauna can kwana bakwai. Al'majiran suka ce ma Bulus, ta wurin Ruhu, kada ma ya je Urushalima.
In ko smo našli učence, smo tam ostali sedem dni. Ti so Pavlu po Duhu povedali, da naj ne bi šel gor v Jeruzalem.
5 Bayan 'yan kwanaki muka cigaba da tafiyarmu. Dukansu da matansu da 'ya'yansu suka raka mu har bayan birnin. Sa'annan muka durkusa a bakin gacci muka yi addu'a muka yi sallama da juna.
In ko smo te dneve dovršili, smo se odpravili in odšli [po] naši poti. In na našo pot so nas vsi pospremili z ženami in otroki, dokler nismo bili izven mesta, in pokleknili smo na obali ter molili.
6 Sai muka shiga jirgin ruwa, su kuma suka koma gida.
In ko smo se poslovili drug od drugega, smo se odpeljali z ladjo, oni pa so se ponovno vrnili domov.
7 Da muka gama tafiyarmu a Taya muka iso Talamayas. A nan ne muka gaisa da 'yan'uwa, muka zamna kwana daya da su.
In ko smo dokončali naše potovanje iz Tira, smo prišli v Ptolemáido in pozdravili brate in en dan ostali z njimi.
8 Washegari muka tashi muka tafi Kaisariya. Muka shiga gidan Filibus mai shaida bishara, daya daga cikin bakwai din, muka zauna da shi.
In naslednji dan smo mi, ki smo bili iz Pavlove skupine, odšli ter prišli v Cezarejo in vstopili v hišo evangelista Filipa, ki je bil eden izmed sedmih; in ostali z njim.
9 Wannan mutum yana da 'ya'ya hudu mata, budurwai masu yin annabci.
In isti mož je imel štiri hčere, device, ki so prerokovale.
10 Sa'anda muka zauna can 'yan kwanaki, wani annabi ya zo daga Yahudiya mai suna Agabus.
In ko smo se tam mudili mnogo dni, je prišel dol iz Judeje nek prerok, po imenu Agab.
11 Ya zo wurinmu ya dauki damarar Bulus ya daure tasa kafar da hannayensa ya ce, “Ruhu Mai Tsarki ya ce, 'Haka Yahudawa za su daure mai wannan damarar, zasu kuma bashe shi ga al'ummai.'”
In ko je prišel k nam, je vzel Pavlov pas ter si zvezal svoje lastne roke in stopala ter rekel: »Tako govori Sveti Duh: ›Tako bodo Judje v Jeruzalemu zvezali moža, ki ima v lasti ta pas in ga izročili v roke poganom.‹«
12 Da muka ji wannan sakon, sai dukanmu da mazaunan wurin muka roki Bulus kada ya tafi Urushalima.
In ko smo slišali te stvari, smo ga rotili, tako mi kakor tudi tisti iz tega kraja, naj ne hodi gor v Jeruzalem.
13 Sai Bulus ya amsa ya ce, “Me kuke yi, kuna kuka kuna karya mani zuciya? Bama a shirye don dauri kadai nake ba har ma da mutuwa a Urushalima, sabili da sunan Ubangiji Yesu.”
Potem je Pavel odgovoril: »Kaj mislite, da jokate in da mi lomite moje srce? Pripravljen sem ne samo biti zvezan, temveč v Jeruzalemu tudi umreti za ime Gospoda Jezusa.«
14 Tun da Bulus bashi da niyyar a rinjaye shi, muka daina kuka muka ce, “Bari nufin Ubangiji ya tabbata.”
In ko ni želel biti pregovorjen, smo prenehali, rekoč: »Zgôdi se Gospodova volja.«
15 Bayan wadannan kwanaki, muka dauki jakkunanmu muka haura Urushalima.
In po teh dneh smo vzeli svojo prtljago in odšli gor v Jeruzalem.
16 Wadansu almjirai daga Kaisariya suka bi mu. Sun zo ne tare da wani ana ce da shi Manason, mutumin Kuburus mai bi na farko, wanda za mu zauna da shi.
Z nami so šli tja tudi nekateri učenci iz Cezareje in s seboj so privedli nekega Mnazona iz Cipra, starega učenca, pri katerem naj bi prenočili.
17 Da muka isa Urushalima, 'yan'uwa suka marabce mu da farin ciki.
In ko smo prišli v Jeruzalem, so nas bratje veselo sprejeli.
18 Washegari Bulus ya tafi tare da mu zuwa wurin Bitrus, dukan dattawa kuma suna nan.
In naslednji dan je Pavel z nami odšel k Jakobu in prisotne so bile vse starešine.
19 Bayan ya gaishe su, sai ya shaida masu daya bayan daya abubuwan da Allah ya yi cikin al'ummai ta wurin hidimarsa.
In ko jih je pozdravil, je podrobno pojasnil, kakšne stvari je Bog po njegovi službi storil med pogani.
20 Da suka ji haka, suka yabi Ubangiji suka ce masa, “Ka gani, dan'uwa, dubban Yahudawa sun bada gaskiya suna kuma da niyyar kiyaye shari'a.
In ko so to slišali, so slavili Gospoda in mu rekli: »Vidiš, brat, kako mnogo tisočev Judov je tukaj, ki verujejo, in vsi so goreči za postavo,
21 An kuma gaya masu a kanka cewa, kana koya wa Yahudawan da suke zaune cikin al'ummai su yi watsi da Musa. Kana koya masu kada su yi wa 'ya'yansu kaciya, kada kuma su bi tsofaffin al'adu.
o tebi pa so obveščeni, da vse Jude, ki so med pogani, učiš, da zapustijo Mojzesa, rekoč, da jim ni treba obrezati njihovih otrok niti živeti po običajih.
22 Me ya kamata mu yi? Hakika za su ji ka zo.
Kaj je to torej? Množica mora brezpogojno priti skupaj, kajti slišali bodo, da si prišel.
23 Sabo da haka ka yi abin da muka fada maka yanzu. Muna da maza hudu da suka dauki wa'adi.
Pravimo ti, stôri torej tole: ›Imamo štiri može, ki imajo na sebi zaobljubo;
24 Tafi da wadannan ka tsarkake kanka tare da su, ka dauki dukan dawainiyar su dana askin kai. Ta haka kowanne mutum zai sani abubuwan da ake fadi a kanka karya ne. Za su sani cewa kai mai kiyaye shari'a ne.
vzemi jih in se z njimi očisti in naj bodo tvoji stroški, da si bodo lahko obrili svoje glave, in vsi bodo lahko spoznali, da te stvari, o katerih so bili glede tebe obveščeni, niso nič, temveč da tudi sam živiš redno in se držiš postave.‹
25 Game da al'umman da suka bada gaskiya mun yi masu wasika, mun bada umarni su kaurace kansu daga sadakokin da aka mika wa gumaku, da jini, da abin da aka makare da kuma fasikanci.
Kar zadeva pogane, ki verujejo, smo pisali in sklenili, da [naj] ne obeležujejo nobene takšne stvari, razen samo, da se varujejo pred stvarmi darovanim malikom in pred krvjo in pred zadavljenim in pred prešuštvom.«
26 Sai Bulus ya dauki mazannan, washegari ya tsarkake kansa tare da su, suka shiga haikali, domin ya sanar da cikar ranakun tsarkakewarsu, wato ranar ba da sadaka domin kowanne dayansu.
Tedaj je Pavel vzel može in naslednji dan, ko se je očistil, je z njimi vstopil v tempelj, da naznani dovršitev dni očiščevanja, dokler se ne bi za vsakega izmed njih darovala daritev.
27 Da kwanakin nan bakwai suka yi gab da cika, wadansu Yahudawa daga Asiya suka ga Bulus a haikali, sai suka zuga taro, suka danke shi.
In ko se je sedem dni skoraj dokončalo, so Judje, ki so bili iz Azije, ko so ga zagledali v templju, razvneli vso množico in nanj položili roke
28 Suna ta kururuwa, “Mutanen Isra'ila ku taimaka mana. Wannan shine mutumin da ke koya wa dukan mutane ko'ina abubuwa gaba da mutane, da shari'a da kuma wannan wurin. Banda haka ya kawo Helenawa cikin haikalin nan ya kazantar da wannan wuri tsatsarka.”
ter vzklikali: »Možje Izraelci, pomagajte: ›To je človek, ki povsod vse može uči proti ljudem in postavi ter temu kraju, in razen tega je tudi Grke privedel v tempelj in oskrunil ta sveti prostor.‹«
29 Domin dama sun ga Tarofimas mutumin Afisa tare da Bulus cikin birni, suka yi zaton ya kawo shi cikin haikali.
(Kajti prej so v mestu videli z njim Efežana Trofima, za katerega so domnevali, da ga je Pavel privedel v tempelj.)
30 Sai duk gari ya rude, mutane suka runtuma suka danke Bulus. Suka ja shi waje daga cikin haikalin, nan da nan aka rufe kofofin.
In vse mesto je bilo razdraženo in ljudje so tekli skupaj in prijeli so Pavla ter ga odvlekli iz templja in nemudoma so bila vrata zaprta.
31 Suna kokarin kashe shi kenan, sai labari ya kai wurin hafsan sojoji cewa Urushalima duk ta yamutse da tarzoma.
In medtem ko so ga poskušali ubiti, so prišle k vrhovnemu poveljniku čete novice, da je bil ves Jeruzalem v vstaji.
32 Nan take ya dauki mayaka da jarumawa, suka sheka da gudu wurin taron. Da mutane suka ga hafsan sojoji da rundunansa sai suka daina dukan Bulus.
Ki je takoj vzel vojake in stotnike ter stekel dol k njim. In ko so zagledali vrhovnega poveljnika in vojake, so Pavla prenehali pretepati.
33 Sai hafsan ya tafi ya danke Bulus ya sa aka daure shi da sarkoki biyu. Ya tambaya ko shi wanene da kuma laifinsa.
Tedaj se je približal vrhovni poveljnik in ga prijel ter mu ukazal, naj bo zvezan z dvema verigama in zahteval je kdo je bil in kaj je storil.
34 Wadansu cikin taron suna ta kururuwa wadansu su ce wannan, wadansu su ce, wancan. Tunda hafsan bai fahimci abin da suke fadi ba, sabo da ihunsu, ya dokaci a shigar da Bulus farfajiyar sojoji.
In nekateri so med množico vpili eno stvar, nekateri drugo in ko ni mogel zanesljivo izvedeti gotovosti za hrup, je ukazal, da ga s seboj vzamejo v grad.
35 Da suka kai matakala, sojoji suka dauki Bulus sabo da tsananin husatar taron jama'a.
In ko je prišel na stopnice, je bilo tako, da so ga zaradi nasilja množice nesli vojaki.
36 Domin taron suka biyo baya suna ihu suna cewa, “A kashe shi.”
Kajti množica ljudi je sledila za njimi in kričala: »Proč z njim.«
37 An kusa shigar da shi farfajiyan kenan sai Bulus ya ce wa babban hafsan, “Ko ka yarda inyi magana da kai?” Hafsan ya ce, “Ka iya Helenanci?
In ko naj bi bil Pavel odveden v grad, je vrhovnemu poveljniku rekel: »Ti smem spregovoriti?« Ki je rekel: »Znaš govoriti grško?
38 Ashe ba kai ne Bamasaren nan da kwanakin baya ka haddasa tawaye, ka dauki 'yan ta'adda dubu hudu ka kai su jeji ba?”
Ali nisi ti tisti Egipčan, ki je pred temi dnevi naredil vstajo in v divjino odvedel štiri tisoč mož, ki so bili morilci?«
39 Bulus ya ce, “Ni Ba'ibrane ne daga birnin Tarsus a Kilikiya. Ni dan kasar babban birni ne. Ka amince mani in yi magana da mutanen.”
Vendar je Pavel rekel: »Jaz sem človek, ki sem Jud iz Tarza, mesta v Kilikiji, meščan ne nepomembnega mesta, in rotim te, dovoli mi, da spregovorim ljudem.«
40 Da hafsan ya bashi izni, Bulus ya mike a kan matakala ya daga hannayensa sama ya yi nuni su yi shuru. Da wuri ya yi tsit, Bulus ya yi masu magana da Ibraniyanci. Ya ce,
In ko mu je dal dovoljenje, je Pavel stal na stopnicah in z roko dal znamenje ljudem. In ko je nastala velika tišina, jim je spregovoril v hebrejskem jeziku, rekoč:

< Ayyukan Manzanni 21 >