< Ayyukan Manzanni 21 >

1 Da muka rabu da su, muka shiga jirgin ruwa muka mike hanya zuwa birnin Kos, washegari sai birnin Rodusa, daga nan sai kuma zuwa birnin Batara.
Nous étant donc embarqués, après nous être séparés d'eux, nous vînmes droit à Cos, et le jour suivant à Rhodes, et de là à Patara.
2 Da muka sami jirgi mai hayewa zuwa Fonisiya sai muka shiga.
Et ayant trouvé un vaisseau qui passait en Phénicie, nous y montâmes, et nous partîmes.
3 Da muka hango tsibirin Kubrus muka bar shi a hagun mu muka nufi Suriya, muka sauka a birnin Taya domin a nan ne jirgin ruwan zai sauke kayansa.
Puis, ayant découvert l'île de Cypre, et la laissant à gauche, nous fîmes route vers la Syrie, et nous abordâmes à Tyr, parce que le vaisseau y laissait sa charge.
4 Bayan mun sami almajirai sai muka zauna can kwana bakwai. Al'majiran suka ce ma Bulus, ta wurin Ruhu, kada ma ya je Urushalima.
Et ayant trouvé les disciples, nous y demeurâmes sept jours. Ils disaient par l'Esprit à Paul, de ne pas monter à Jérusalem.
5 Bayan 'yan kwanaki muka cigaba da tafiyarmu. Dukansu da matansu da 'ya'yansu suka raka mu har bayan birnin. Sa'annan muka durkusa a bakin gacci muka yi addu'a muka yi sallama da juna.
Mais ces jours étant passés, nous sortîmes pour partir, et ils nous accompagnèrent tous, avec leurs femmes et leurs enfants, jusque hors de la ville. Et nous mettant à genoux sur le rivage, nous fîmes la prière.
6 Sai muka shiga jirgin ruwa, su kuma suka koma gida.
Et après nous être embrassés les uns les autres, nous montâmes sur le vaisseau; et ils retournèrent chez eux.
7 Da muka gama tafiyarmu a Taya muka iso Talamayas. A nan ne muka gaisa da 'yan'uwa, muka zamna kwana daya da su.
Achevant notre navigation, de Tyr nous vînmes à Ptolémaïs, et après avoir salué les frères, nous demeurâmes un jour avec eux.
8 Washegari muka tashi muka tafi Kaisariya. Muka shiga gidan Filibus mai shaida bishara, daya daga cikin bakwai din, muka zauna da shi.
Le lendemain, Paul et nous qui étions avec lui, étant partis, nous vînmes à Césarée; et étant entrés dans la maison de Philippe l'évangéliste, qui était l'un des sept diacres, nous logeâmes chez lui.
9 Wannan mutum yana da 'ya'ya hudu mata, budurwai masu yin annabci.
Il avait quatre filles vierges, qui prophétisaient.
10 Sa'anda muka zauna can 'yan kwanaki, wani annabi ya zo daga Yahudiya mai suna Agabus.
Comme nous demeurâmes là plusieurs jours, un prophète, nommé Agabus, descendit de Judée.
11 Ya zo wurinmu ya dauki damarar Bulus ya daure tasa kafar da hannayensa ya ce, “Ruhu Mai Tsarki ya ce, 'Haka Yahudawa za su daure mai wannan damarar, zasu kuma bashe shi ga al'ummai.'”
Et étant venu vers nous, il prit la ceinture de Paul, et se liant les mains et les pieds, il dit: Le Saint-Esprit dit ceci: Les Juifs lieront de même à Jérusalem l'homme auquel appartient cette ceinture, ils le livreront entre les mains des Gentils.
12 Da muka ji wannan sakon, sai dukanmu da mazaunan wurin muka roki Bulus kada ya tafi Urushalima.
Et quand nous eûmes entendu cela, nous et les habitants du lieu, nous priâmes Paul de ne point monter à Jérusalem.
13 Sai Bulus ya amsa ya ce, “Me kuke yi, kuna kuka kuna karya mani zuciya? Bama a shirye don dauri kadai nake ba har ma da mutuwa a Urushalima, sabili da sunan Ubangiji Yesu.”
Mais Paul répondit: Que faites-vous, en pleurant et me brisant le cœur? Car je suis prêt, non seulement à être lié, mais même à mourir à Jérusalem pour le nom du Seigneur Jésus.
14 Tun da Bulus bashi da niyyar a rinjaye shi, muka daina kuka muka ce, “Bari nufin Ubangiji ya tabbata.”
Ainsi, n'ayant pu le persuader, nous nous tînmes tranquilles et nous dîmes: Que la volonté du Seigneur soit faite
15 Bayan wadannan kwanaki, muka dauki jakkunanmu muka haura Urushalima.
Quelques jours après, ayant fait nos préparatifs, nous montâmes à Jérusalem.
16 Wadansu almjirai daga Kaisariya suka bi mu. Sun zo ne tare da wani ana ce da shi Manason, mutumin Kuburus mai bi na farko, wanda za mu zauna da shi.
Et des disciples de Césarée vinrent aussi avec nous, amenant un certain Mnason, de Cypre, ancien disciple, chez qui nous devions loger.
17 Da muka isa Urushalima, 'yan'uwa suka marabce mu da farin ciki.
Quand nous fûmes arrivés à Jérusalem, les frères nous reçurent avec joie.
18 Washegari Bulus ya tafi tare da mu zuwa wurin Bitrus, dukan dattawa kuma suna nan.
Et le lendemain, Paul vint avec nous chez Jacques, et tous les anciens s'y assemblèrent.
19 Bayan ya gaishe su, sai ya shaida masu daya bayan daya abubuwan da Allah ya yi cikin al'ummai ta wurin hidimarsa.
Et après les avoir embrassés, il raconta en détail tout ce que Dieu avait fait parmi les Gentils, par son ministère.
20 Da suka ji haka, suka yabi Ubangiji suka ce masa, “Ka gani, dan'uwa, dubban Yahudawa sun bada gaskiya suna kuma da niyyar kiyaye shari'a.
Quant à eux, l'ayant entendu, ils glorifièrent le Seigneur et ils lui dirent: Frère, tu vois combien il y a de milliers de Juifs qui ont cru, et ils sont tous zélés pour la loi.
21 An kuma gaya masu a kanka cewa, kana koya wa Yahudawan da suke zaune cikin al'ummai su yi watsi da Musa. Kana koya masu kada su yi wa 'ya'yansu kaciya, kada kuma su bi tsofaffin al'adu.
Or, ils ont été informés que tu enseignes à tous les Juifs qui sont parmi les Gentils, à renoncer à Moïse, en leur disant de ne pas circoncire les enfants, et de ne pas se conformer aux coutumes.
22 Me ya kamata mu yi? Hakika za su ji ka zo.
Que faut-il donc faire? Certainement la multitude se rassemblera; car ils entendront dire que tu es arrivé.
23 Sabo da haka ka yi abin da muka fada maka yanzu. Muna da maza hudu da suka dauki wa'adi.
Fais donc ce que nous allons te dire: Nous avons quatre hommes qui ont fait un vou;
24 Tafi da wadannan ka tsarkake kanka tare da su, ka dauki dukan dawainiyar su dana askin kai. Ta haka kowanne mutum zai sani abubuwan da ake fadi a kanka karya ne. Za su sani cewa kai mai kiyaye shari'a ne.
Prends-les avec toi, purifie-toi avec eux, et paye leur dépense, afin qu'ils puissent se faire raser la tête, et que tous sachent qu'il n'est rien de tout ce qu'ils ont entendu dire de toi, mais que tu continues à garder la loi.
25 Game da al'umman da suka bada gaskiya mun yi masu wasika, mun bada umarni su kaurace kansu daga sadakokin da aka mika wa gumaku, da jini, da abin da aka makare da kuma fasikanci.
Quant aux Gentils qui ont cru, nous avons décidé et nous leur avons écrit qu'ils ne devaient rien observer de semblable, mais se garder seulement de ce qui est sacrifié aux idoles, du sang, de ce qui est étouffé et de la fornication.
26 Sai Bulus ya dauki mazannan, washegari ya tsarkake kansa tare da su, suka shiga haikali, domin ya sanar da cikar ranakun tsarkakewarsu, wato ranar ba da sadaka domin kowanne dayansu.
Alors, Paul ayant pris ces hommes, et s'étant purifié avec eux, entra dans le temple le jour suivant, déclarant la durée des jours dans lesquels la purification s'accomplirait, et quand l'offrande serait présentée pour chacun d'eux.
27 Da kwanakin nan bakwai suka yi gab da cika, wadansu Yahudawa daga Asiya suka ga Bulus a haikali, sai suka zuga taro, suka danke shi.
Et comme les sept jours allaient être accomplis, les Juifs d'Asie, l'ayant vu dans le temple, émurent toute la multitude, et se saisirent de lui,
28 Suna ta kururuwa, “Mutanen Isra'ila ku taimaka mana. Wannan shine mutumin da ke koya wa dukan mutane ko'ina abubuwa gaba da mutane, da shari'a da kuma wannan wurin. Banda haka ya kawo Helenawa cikin haikalin nan ya kazantar da wannan wuri tsatsarka.”
En criant: Hommes Israélites, aidez-nous. Voici l'homme qui prêche partout, et devant tous, contre la nation, la loi, et ce lieu-ci; il a même encore amené des Grecs dans le temple, et a profané ce saint lieu.
29 Domin dama sun ga Tarofimas mutumin Afisa tare da Bulus cikin birni, suka yi zaton ya kawo shi cikin haikali.
Car ils avaient vu auparavant dans la ville avec lui, Trophime d'Éphèse, et ils croyaient que Paul l'avait mené dans le temple.
30 Sai duk gari ya rude, mutane suka runtuma suka danke Bulus. Suka ja shi waje daga cikin haikalin, nan da nan aka rufe kofofin.
Et toute la ville fut émue, et il y eut un rassemblement du peuple; et ayant saisi Paul, ils le traînèrent hors du temple; et aussitôt les portes furent fermées.
31 Suna kokarin kashe shi kenan, sai labari ya kai wurin hafsan sojoji cewa Urushalima duk ta yamutse da tarzoma.
Mais, comme ils cherchaient à le tuer, le bruit vint au tribun de la cohorte que tout Jérusalem était en trouble.
32 Nan take ya dauki mayaka da jarumawa, suka sheka da gudu wurin taron. Da mutane suka ga hafsan sojoji da rundunansa sai suka daina dukan Bulus.
A l'instant il prit des soldats et des centeniers avec lui, et courut à eux; et voyant le tribun et les soldats, ils cessèrent de battre Paul.
33 Sai hafsan ya tafi ya danke Bulus ya sa aka daure shi da sarkoki biyu. Ya tambaya ko shi wanene da kuma laifinsa.
Alors le tribun s'approcha, et se saisit de lui, et commanda qu'on le liât de deux chaînes; puis il demanda qui il était, et ce qu'il avait fait.
34 Wadansu cikin taron suna ta kururuwa wadansu su ce wannan, wadansu su ce, wancan. Tunda hafsan bai fahimci abin da suke fadi ba, sabo da ihunsu, ya dokaci a shigar da Bulus farfajiyar sojoji.
Mais dans la foule les uns criaient d'une manière, et les autres d'une autre; ne pouvant donc rien apprendre de certain, à cause du tumulte, il commanda qu'on le menât dans la forteresse.
35 Da suka kai matakala, sojoji suka dauki Bulus sabo da tsananin husatar taron jama'a.
Et quand Paul fut sur les degrés, il dut être porté par les soldats, à cause de la violence de la populace,
36 Domin taron suka biyo baya suna ihu suna cewa, “A kashe shi.”
Car une foule de peuple le suivait, en criant: Fais-le mourir!
37 An kusa shigar da shi farfajiyan kenan sai Bulus ya ce wa babban hafsan, “Ko ka yarda inyi magana da kai?” Hafsan ya ce, “Ka iya Helenanci?
Comme Paul était sur le point d'entrer dans la forteresse, il dit au tribun: M'est-il permis de te dire quelque chose? Et celui-ci répondit: Tu sais donc le grec?
38 Ashe ba kai ne Bamasaren nan da kwanakin baya ka haddasa tawaye, ka dauki 'yan ta'adda dubu hudu ka kai su jeji ba?”
N'es-tu point cet Égyptien qui, ces jours passés, a excité une sédition, et conduit au désert quatre mille brigands
39 Bulus ya ce, “Ni Ba'ibrane ne daga birnin Tarsus a Kilikiya. Ni dan kasar babban birni ne. Ka amince mani in yi magana da mutanen.”
Paul répondit: Je suis Juif, de Tarse, citoyen de cette ville célèbre de Cilicie; je t'en prie, permets-moi de parler au peuple.
40 Da hafsan ya bashi izni, Bulus ya mike a kan matakala ya daga hannayensa sama ya yi nuni su yi shuru. Da wuri ya yi tsit, Bulus ya yi masu magana da Ibraniyanci. Ya ce,
Et quand il le lui eut permis, Paul, se tenant sur les degrés, fit signe de la main au peuple; et un grand silence s'étant établi, il parla en langue hébraïque, et dit:

< Ayyukan Manzanni 21 >