< Ayyukan Manzanni 15 >

1 Wadansu mutane suka zo daga Yahudiya suka koyar da 'yan'uwa, cewa, “Idan ba yi maku kaciya bisa ga al'addar Musa ba, ba za ku sami ceto ba.”
Some men came down from Yehuda and taught the brothers, "Unless you are circumcised after the custom of Mushe, you cannot be saved."
2 Da Bulus da Barnaba suka tunkare su da mahawara, sai 'yan'uwa suka yanke shawara Bulus da Barnaba da wasu su je Urushalima wurin manzanni da dattawa a kan wannan magana.
Therefore when Paul and Bar-Naba had no small discord and discussion with them, they appointed Paul and Bar-Naba, and some others of them, to go up to Urishlim to the apostles and elders about this question.
3 Da shike iklisiya ce ta aike su, sai suka bi ta Finikiya da ta Samariya suka sanar da tuban al'ummai. Ya kawo murna mai yawa a wurin 'yan'uwa.
They, being sent on their way by the church, passed through both Phoenicia and Samaria, describing in detail the conversion of the non-Jewish people. They caused great joy to all the brothers.
4 Bayan sun zo Urushalima, sai iklisiya da manzanni da dattawa, suka marabce su, sai suka fada masu abin da Allah ya yi ta wurinsu.
When they had come to Urishlim, they were received by the church and the apostles and the elders, and they reported all things that God had done with them.
5 Amma wadansu mutane wadanda suka ba da gaskiya daga cikin Farisawa, suka tashi suka ce, “Dole ne a yi masu kaciya a kuma umarce su su kiyaye dokar Musa.”
But some of the sect of the Pharisees who believed rose up, saying, "It is necessary to circumcise them, and to command them to keep the Law of Mushe."
6 Sai manzanin da dattawan suka taru don su duba wannan lamari.
The apostles and the elders were gathered together to see about this matter.
7 Bayan mahawara mai tsanani, sai Bitrus ya tashi ya ce masu, “'Yan'uwa, kun san lokacin baya da ya wuce, Allah ya yi zabi a cikinku, cewa ta bakina ne al'ummai za su ji bishara, su kuma ba da gaskiya.
When there had been much discussion, Kipha rose up and said to them, "Brothers, you know that a good while ago God made a choice among you, that by my mouth the nations should hear the word of the Good News, and believe.
8 Allah, wanda ya san zuciya, ya yi masu shaida, ya kuma basu Ruhu Mai Tsarki kamar yadda ya yi mana;
God, who knows the heart, testified about them by giving the Rukha d'Qudsha, just like he did to us.
9 kuma bai bambanta mu da su ba, ya tsabtace zuciyarsu ta wurin bangaskiya.
He made no distinction between us and them, cleansing their hearts by faith.
10 To, saboda haka don me kuke gwada Allah, kuna sa wa almajirai nauyi a wuya wanda ubanninmu duk da mu ba mu iya dauka ba?
Now therefore why do you tempt God, that you should put a yoke on the neck of the disciples which neither our fathers nor we were able to bear?
11 Amma mun gaskanta za mu samu ceto ta wurin alherin Ubangiji Yesu, kamar yadda suke.”
But we believe that we are saved through the grace of the Lord Yeshua, just as they are."
12 Dukan taron jama'ar suka yi shiru sa'adda suke sauraron sakon shaidar da mamakin abin da Allah ya yi ta wurin Bulus da Barnaba a cikin al'ummai.
And all the people kept quiet, and they listened to Bar-Naba and Paul reporting what signs and wonders God had done among the nations through them.
13 Bayan sun gama magana, Yakubu ya amsa, ya ce, “'Yan'uwa, ku ji ni.
After they were silent, Yaquv answered, "Brothers, listen to me.
14 Saminu ya fada yadda Allah ya fara nuna jinkai ga al'ummai domin ya dauke jama'a daga cikinsu domin sunansa.
Shimon has reported how God first visited the nations, to take out of them a people for his name.
15 Maganar annabawa ta yarda da wannan, kamar yadda yake a rubuce,
This agrees with the words of the prophets. As it is written,
16 'Bayan wadannan abubuwa zan dawo, zan gina gidan Dauda wanda ya fadi kasa; in sake gina bangonsa, in tsayar da shi,
'After these things I will return; and I will rebuild the tabernacle of David that has fallen, and I will rebuild its ruins, and I will restore it,
17 saboda sauran jama'a su nemi fuskar Ubangiji, har da al'ummai da ake kira da sunana.
that the rest of humanity may seek after the Lord, and all the nations who are called by my name, says the Lord, who makes these things
18 Wannan shine abin da Ubangiji ya fadi, shi wanda ya yi wadannan abubuwa da aka sani tun zamanin da. (aiōn g165)
known from long ago.' (aiōn g165)
19 Saboda haka, a gani na kada mu matsa wa al'umman da suka juyo gun Allah;
"Therefore my judgment is that we do not trouble those from among the non-Jewish people who turn to God,
20 amma zamu rubuta masu da cewa, su guje wa gumaka da zina da faskanci da maye da cin mushe.
but that we write to them that they abstain from things defiled by idols, from sexual immorality, from what is strangled, and from blood.
21 Tun zamanin da akwai mutane a kowanne birni wadanda suke wa'azi da karatun Musa a majami'u kowanne Asabaci.”
For Mushe from generations of old has in every city those who proclaim him, being read in the synagogues every Sabbath."
22 Sai ya yi wa manzanin kyau su da dattawa da dukan iklisiyar su zabi Yahuza da Barnaba da Sila da dattawan iklisiya a tura su Antakiya tare da Bulus da Barnaba.
Then it seemed good to the apostles and the elders, with the whole church, to choose men out of their company, and send them to Antioch with Paul and Bar-Naba: Yehudah called Bar-Shaba, and Silas, leaders among the brothers.
23 Sai suka rubuta wasika, “Manzani da dattawa da 'yan'uwa zuwa ga al'ummai 'yan'uwa a Antakiya da Suriya da Kilikiya, gaisuwa mai yawa.
They wrote these things by their hand: "The apostles, the elders, and the brothers, to the non-Jewish brothers who are in Antioch, Syria, and Cilicia: greetings.
24 Mun ji cewa wasu mutane daga cikinmu wadanda ba mu umarce su ba, sun fita daga cikinmu sun yi maku koyarwar da ta daga maku hankali.
Because we have heard that some who went out from us have troubled you with words, unsettling your souls, to whom we gave no commandment;
25 Ya yi kyau da dukanmu, muka amince mu zabi wadansu mutane mu tura su wurinku tare da Bulus da Barnaba,
it seemed good to us, having come to one accord, to choose out men and send them to you with our beloved Bar-Naba and Paul,
26 mutane wadanda suka sadaukar da ransu domin sunan Ubangiji Yesu Almasihu.
who have risked their lives for the name of our Lord Yeshua Meshikha.
27 Mun aika Yahuza da Sila su gaya maku wadannan abubuwa.
We have sent therefore Yehudah and Silas, who themselves will also tell you the same things by word of mouth.
28 Saboda haka ya yi kyau Ruhu Mai Tsarki da mu, kada mu sa maku nauyi fiye da wadannan abubuwan:
For it seemed good to the Rukha d'Qudsha, and to us, to lay no greater burden on you than these necessary things:
29 ku bar yi wa gumaka hadaya, ku bar cin mushe da shan kayan maye da zina da faskanci, in kun kiyaye wadannan abubuwa za ku zauna lafiya. Ku huta lafiya.”
that you abstain from things sacrificed to idols, from blood, from things strangled, and from sexual immorality, from which if you keep yourselves, it will be well with you. Farewell."
30 Da aka sallame su, sai suka je Antakiya. Bayan sun tara jama'a sai suka ba su wasikar.
So, when they were sent off, they came to Antioch, and having gathered the congregation together, they delivered the letter.
31 Bayan da suka karanta ta, sai suka yi murna sosai saboda karfafawa.
When they had read it, they rejoiced over the encouragement.
32 Yahuza da Sila, da shike su annabawa ne, suka karfafa 'yan'uwa da kalmomi masu yawa.
Yehudah and Silas, also being prophets themselves, encouraged the brothers with many words, and strengthened them.
33 Bayan sun yi kwananki a wurin, sai aka sallame su zuwa wurin 'yan'uwa wadanda suka aiko su.
After they had spent some time there, they were sent back with greetings from the brothers to those that had sent them forth.
34 Amma ya gamshe Sila ya zauna a wurin.
However, Silas decided to remain there.
35 Amma Bulus da Barnaba suka tsaya a Antakiya da sauran 'yan'uwa, suna koyar da maganar Ubangiji.
And Paul and Bar-Naba stayed in Antioch, teaching and proclaiming the word of the Lord, with many others also.
36 Bayan kwanaki kadan Bulus ya ce ma Barnaba, “Mu koma yanzu mu ziyarci dukan 'yan'uwa da muka yi masu bisharar Ubangiji, mu ga yadda suke.
After some days Paul said to Bar-Naba, "Let us return now and visit our brothers in every city in which we proclaimed the word of the Lord, to see how they are doing."
37 Barnaba yana so su dauki Yahaya wanda kuma ake kira Markus.
Bar-Naba planned to take Yukhanan, who was called Markos, with them also.
38 Amma Bulus ya yi tunanin bai kamata a tafi da Markus ba, tun da ya bar su a Bamfiliya bai ci gaba da su ba.
But Paul did not think that it was a good idea to take with them someone who had withdrawn from them in Pamphylia, and did not go with them to do the work.
39 Nan jayayya ta tashi tsakaninsu, har suka rabu da juna sai Barnaba ya tafi tare da Markus suka ketare zuwa Kuburus.
Then the contention grew so sharp that they separated from each other. Bar-Naba took Markos with him, and sailed away to Cyprus,
40 Amma Bulus ya zabi Sila suka tafi, bayan 'yan'uwa sun yi masu addu'ar alherin Allah ya kiyaye su.
but Paul chose Silas, and went out, being commended by the brothers to the grace of the Lord.
41 Bulus ya tafi ya zazzaga Suriya da Kilikiya yana ta karfafa iklisiyoyin.
He went through Syria and Cilicia, strengthening the congregations.

< Ayyukan Manzanni 15 >