< Zefaniya 1 >

1 Domin mai bi da kaɗe-kaɗe. A kan kayan kiɗi masu tsirkiyata. Maganar Ubangiji da ta zo wa Zefaniya ɗan Kushi, ɗan Gedaliya, ɗan Amariya, ɗan Hezekiya, a zamanin Yosiya ɗan Amon sarkin Yahuda.
The word of Yahweh which came unto Zephaniah, son of Cushi, son of Gedaliah, son of Amariah, son of Hezekiah, —in the days of Josiah son of Amon, king of Judah.
2 “Zan hallaka kome a fuskar duniya,” in ji Ubangiji.
I will take clean away everything from off the face of the ground, Declareth Yahweh.
3 “Zan hallaka mutane da dabbobi; zan kuma hallaka tsuntsayen sama da kifayen teku, da gumakan da suke sa mugaye su yi tuntuɓe.” “Sa’ad da zan kawar da mutum daga fuskar duniya,” in ji Ubangiji.
I will take away man and beast, I will take away the bird of the heavens and the fishes of the sea, and the stumblingblocks, even them who are lawless, —and will cut off mankind, from off the face of the ground, Declareth Yahweh.
4 “Zan miƙa hannuna gāba da Yahuda da kuma dukan mazaunan Urushalima. Zan datse raguwar Ba’al daga wannan wuri, da sunayen firistocin gumaka da na marasa sanin Allah,
And I will stretch out my hand—over Judah, and over all the inhabitants of Jerusalem, —and will cut off out of this place, the name of Baal, the name of the priestlings, with the priests;
5 waɗanda suka rusuna a kan rufin ɗaki don su yi sujada ga rundunar taurari. Waɗanda suka rusuna suka kuma yi rantsuwa da sunan Ubangiji suke kuma rantsuwa da sunan Molek.
And them who bow down upon the housetops to the host of the heavens, —and them who bow down—who swear to Yahweh, and swear by Milcom;
6 Waɗanda suka juya daga bin Ubangiji, ba sa kuma neman Ubangiji ko su nemi nufinsa.”
And them who turn away from following Yahweh, —and have neither sought Yahweh, nor enquired for him.
7 Ku yi shiru a gaban Ubangiji Mai Iko Duka, gama ranar Ubangiji ta yi kusa. Ubangiji ya shirya hadaya; ya kuma tsarkake waɗanda ya gayyato.
Hush! at the presence of My Lord, Yahweh, —for, near, is the day of Yahweh, for Yahweh hath prepared his sacrifice, hath hallowed his guests.
8 “A ranar hadayar Ubangiji zan hukunta sarakuna da kuma’ya’yan sarakuna da duk waɗanda suke sanye da rigunan ƙasashen waje.
And it shall come to pass, in the day of Yahweh’s sacrifice, that I will punish the rulers, and the sons of the king, —and all such as are clothed with foreign apparel;
9 A wannan rana zan hukunta dukan waɗanda suke kauce taka madogarar ƙofa, waɗanda suke cika haikalin allolinsu da rikici da ruɗu.
And I will punish every one who leapeth over the threshold, in that day, —those who fill the house of their lords with violence and deceit.
10 “A wannan rana,” in ji Ubangiji, “Za a ji kuka daga Ƙofar Kifi, kururuwa daga Sabon Mazauni, da kuma amo mai ƙarfi daga tuddai.
And there shall come to be, in that day, declareth Yahweh, The noise of an outcry from the fish-gate, and of a howling out of the new city, —and of a great crashing, from the hills.
11 Ku yi kururuwa, ku da kuke zaune a yankin kasuwa; za a hallaka dukan’yan kasuwanku, dukan waɗanda suke kasuwanci da azurfa za su lalace.
Howl, ye inhabitants of the lower city, —because destroyed are all the people of traffic, cut off are all they who were laden with silver.
12 A wannan lokaci zan bincike Urushalima da fitilu in kuma hukunta waɗanda ba su kula ba, waɗanda suke kamar ruwan inabin da aka bar a ƙasan tukunya, waɗanda suke tsammani, ‘Ubangiji ba zai yi kome ba nagari ko mummuna.’
And it shall come to pass, at that time, that I will search through Jerusalem, with lamps, —and will punish the men who are thickened upon their lees, who are saying in their heart, Yahweh, will not give blessing, neither will he bring calamity.
13 Za a washe dukiyarsu, a rurrushe gidajensu. Za su gina gidaje amma ba za su zauna a ciki ba; za su shuka inabi amma ba za su sha ruwansa ba.”
Therefore shall their goods become a booty, and their houses, a desolation, —and they shall build houses, but not inhabit them, and plant vineyards, but not drink the wine thereof.
14 Babbar ranar Ubangiji ta yi kusa, ta yi kusa kuma tana zuwa da sauri. Ku saurara! Kukan ranar Ubangiji za tă yi zafi, za a ji kururuwan jarumi a can.
Near is the great day of Yahweh, near, and very speedy, —The noise of the day of Yahweh, a strong man—there!—bitterly crying out!
15 Ranan nan za tă zama ranar fushi, rana ce ta baƙin ciki da azaba, rana ce ta tashin hankali da lalacewa, ranar duhu baƙi ƙirin, ranar gizagizai da baƙin duhu,
A day of indignation, —that day! day of danger and distress, day of rush, and of crash, day of obscurity, and deep gloom, day of cloud, and thick darkness;
16 rana ce ta busa ƙaho da kururuwar yaƙi gāba da birane masu mafaka, da kuma kusurwar hasumiyoyi.
day of horn, and war-shout, —against the fortified cities, and against the high towers.
17 “Zan kawo baƙin ciki a kan mutane za su kuma yi tafiya kamar makafi, domin sun yi wa Ubangiji zunubi. Za a zubar da jininsu kamar ƙura kayan cikinsu kuma kamar najasa.
And I will bring distress to mankind, and they shall walk like them who are blind, because, against Yahweh, have they sinned, —and their blood, shall be poured out, as dust, and their bowels like dung.
18 Azurfarsu ko zinariyarsu ba za su iya cetonsu ba a ranar fushin Ubangiji.” A cikin zafin kishinsa za a hallaka dukan duniya gama zai kawo ƙarshen dukan mazaunan duniya nan da nan.
Neither their silver nor yet their gold, shall be able to deliver them, in the day of the indignation of Yahweh, but, in the fire of his jealousy, shall the whole earth be consumed; For, a destruction, surely a terrible one, will he make, with all them who dwell in the earth.

< Zefaniya 1 >