< Waƙar Waƙoƙi 3 >

1 Dare farai a kan gadona na nemi wanda zuciyata take ƙauna; na neme shi amma ban same shi ba.
By night on my bed, I sought him whom my soul loves. I sought him, but I didn’t find him.
2 Zan tashi yanzu in zagaya gari, in ratsa titunansa da dandalinsa; zan nemi wanda zuciyata take ƙauna. Saboda haka na neme shi, amma ban same shi ba.
I will get up now, and go about the city; in the streets and in the squares I will seek him whom my soul loves. I sought him, but I didn’t find him.
3 Masu tsaro suka gamu da ni yayinda suke kai kawo a cikin birni, sai na ce, “Kun ga mini wanda zuciyata take ƙauna?”
The watchmen who go about the city found me; “Have you seen him whom my soul loves?”
4 Rabuwata da su ke nan sai na sami wanda zuciyata take ƙauna. Na riƙe shi, ban yarda yă tafi ba sai da na kawo shi gidan mahaifiyata, zuwa ɗakin wadda ta yi cikina.
I had scarcely passed from them, when I found him whom my soul loves. I held him, and would not let him go, until I had brought him into my mother’s house, into the room of her who conceived me.
5 ’Yan matan Urushalima, ku yi mini alkawari da bareyi da ƙishimai na jeji. Ba za ku tā da ko ku farka ƙauna ba sai haka ya zama lalle.
I adjure you, daughters of Jerusalem, by the roes, or by the hinds of the field, that you not stir up nor awaken love, until it so desires.
6 Wane ne wannan mai zuwa daga hamada kamar tunnuƙewar hayaƙi, cike da ƙanshin turaren mur da lubban da aka yi da kayan yajin’yan kasuwa?
Who is this who comes up from the wilderness like pillars of smoke, perfumed with myrrh and frankincense, with all spices of the merchant?
7 Duba! Abin ɗaukar Solomon ne, jarumawa sittin suke rakiya, zaɓaɓɓun sojojin Isra’ila,
Behold, it is Solomon’s carriage! Sixty mighty men are around it, of the mighty men of Israel.
8 dukansu suna saye da takobi dukansu ƙwararru ne a yaƙi, kowanne da takobinsa a rataye a gefensa, a shirye don abubuwan bantsoro na dare.
They all handle the sword, and are expert in war. Every man has his sword on his thigh, because of fear in the night.
9 Sarki Solomon ya yi wa kansa abin ɗauka; ya yi shi da katako daga Lebanon.
King Solomon made himself a carriage of the wood of Lebanon.
10 An yi sandunansa da azurfa, aka yi ƙasarsa da zinariya. An lulluɓe wurin zaman da zanen shunayya,’yan matan Urushalima sun yi mata irin yayen da ake yi na ƙauna.
He made its pillars of silver, its bottom of gold, its seat of purple, the middle of it being paved with love, from the daughters of Jerusalem.
11 Fito, ku’yan matan Sihiyona, ku ga Sarki Solomon yana saye da rawani, rawanin da mahaifiyarsa ta naɗa masa, a ranar aurensa, a ranar da zuciyarsa ta yi farin ciki.
Go out, you daughters of Zion, and see King Solomon, with the crown with which his mother has crowned him, in the day of his weddings, in the day of the gladness of his heart.

< Waƙar Waƙoƙi 3 >