< Rut 4 >

1 Ana cikin haka Bowaz ya haura zuwa ƙofar gari ya tafi ya zauna a can. Sa’ad da dangi mai fansan da ya yi zance ya iso, Bowaz ya ce, “Zo nan abokina ka zauna.” Saboda haka ya ratso ya zauna.
Now Boaz went up to the gate and sat down there. Soon, the near kinsman of whom Boaz had spoken came by. Boaz said to him, “My friend, come over and sit down here.” The man came over and sat down.
2 Bowaz kuwa ya kira dattawa guda goma na garin ya ce, “Ku zauna a nan,” suka kuwa zauna.
Then Boaz took ten men of the elders of the city and said, “Sit down here.” So they sat down.
3 Sa’an nan ya ce wa dangin nan mai fansa, “Na’omi, wadda ta dawo daga Mowab, tana so ta sayar da filin da yake na ɗan’uwanmu Elimelek.
Boaz said to the near kinsman, “Naomi, who has returned from the country of Moab, is selling the parcel of land that was our brother Elimelek's.
4 Na ga ya kamata in jawo hankalinka ga batun in kuma ba da shawara ka saye shi a gaban waɗannan da suke zazzaune a nan da kuma a gaban dattawan jama’a. In kana so ka fanshe shi, to, sai ka yi. Amma in ba za ka yi ba, sai ka faɗa mini, don in sani. Gama babu wani mai izinin yin haka sai kai, ni ne kuwa na biye.” Sai ya ce, “Zan fansa.”
I thought to inform you and say to you, 'Buy it in the presence of those who are sitting here, and in the presence of the elders of my people.' If you wish to redeem it, redeem it. But if you do not wish to redeem it, then tell me, so that I may know, for there is no one to redeem it besides you, and I am after you.” Then the other man said, “I will redeem it.”
5 Sa’an nan Bowaz ya ce, “A ranar da ka saya filin daga Na’omi da kuma daga Rut mutuniyar Mowab, ka sayi gwauruwar marigayin nan, domin ka riƙe sunan marigayin da kuma kayansa.”
Then Boaz said, “On the day that you buy the field from the hand of Naomi, you must also take Ruth the Moabite woman, the widow of a dead man, in order to raise up the name of the dead on his inheritance.”
6 Da jin haka, sai dangin nan mai fansa ya ce, “To, ba zan iya fanshe shi ba don kada in yi wa nawa mallakar rauni. Za ka iya fanshe shi wa kanka. Ni dai ba zan iya ba.”
Then the near kinsman said, “I cannot redeem it for myself without damaging my own inheritance. You take my right of redemption for yourself, for I cannot redeem it.”
7 (To, a kwanakin can a Isra’ila, domin a tabbatar da fansa da kuma musayar da mallaka, mutum zai cire takalminsa ya ba wa ɗayan. Wannan ita ce hanyar tabbatar da al’amarin a hukumance a cikin Isra’ila.)
Now this was the custom in former times in Israel concerning the redemption and exchange of goods. To confirm all things, a man took off his shoe and gave it to his neighbor; this was the manner of making legal agreements in Israel.
8 Saboda haka dangin nan mai fansa ya ce wa Bowaz, “Saye shi wa kanka.” Sai ya cire takalminsa.
So the near kinsman said to Boaz, “Buy it for yourself,” and he took off his sandal.
9 Sa’an nan Bowaz ya yi shela wa dattawa da kuma dukan mutane, “A yau ku ne shaidu cewa na saya daga Na’omi dukan mallakar Elimelek, Kiliyon da kuma Malon.
Then Boaz said to the elders and to all the people, “You are witnesses today that I have bought all that was Elimelek's and all that was Kilion's and Mahlon's from the hand of Naomi.
10 Na kuma ɗauki Rut mutuniyar Mowab, gwauruwar Malon a matsayin matata domin sunan mamaci da kuma mallakarsa yă ci gaba, domin kada sunansa yă ɓace daga cikin iyali ko daga tarihin gari. A yau ku ne shaidu!”
Also Ruth the Moabite woman, the wife of Mahlon, I have acquired to be my wife, in order that I might raise up the name of the dead man on his inheritance, so that his name will not be cut off from among his brothers and from the gate of his place. Today you are witnesses!”
11 Sai dattawan da kuma dukan waɗanda suke a ƙofar suka ce, “Mu shaidu ne. Bari Ubangiji yă sa macen da take zuwa cikin gidanka ta zama kamar Rahila da Liyatu, waɗanda tare suka gina gidan Isra’ila. Bari ka sami martaba a cikin Efrata ka kuma zama sananne cikin Betlehem.
All the people who were in the gate and the elders said, “We are witnesses. May Yahweh make the woman who has come into your house like Rachel and Leah, the two who built up the house of Israel; and may you prosper in Ephrathah and be renowned in Bethlehem.
12 Ta wurin’ya’yan da Ubangiji zai ba ka ta wurin wannan mace, bari iyalinka yă zama kamar na Ferez, wanda Tamar ta haifa wa Yahuda.”
May your house be like the house of Perez, whom Tamar bore to Judah, through the offspring that Yahweh will give you with this young woman.”
13 Sai Bowaz ya ɗauki Rut ta kuwa zama matarsa. Sa’an nan ya kwana da ita, Ubangiji kuma ya sa ta yi ciki, ta haifi ɗa.
So Boaz took Ruth, and she became his wife. He slept with her, and Yahweh allowed her to become pregnant, and she bore a son.
14 Mata suka ce wa Na’omi, “Yabo ya tabbata ga Ubangiji, wanda a wannan rana bai bar ki ba tare da dangi mai fansa ba. Allah yă sa yă zama sananne a dukan Isra’ila!
The women said to Naomi, “May Yahweh be blessed, who has not left you today without a near kinsman, this baby. May his name be famous in Israel.
15 Zai sabunta rayuwarki yă adana ki a tsufanki. Gama surukarki wadda take ƙaunarki wadda kuma take mafi kyau gare ki fiye da’ya’ya maza bakwai, ta haife shi.”
May he be for you a restorer of life and a nourisher of your old age, for your daughter-in-law, who loves you, who is better to you than seven sons, has borne him.”
16 Sai Na’omi ta ɗauki yaron, ta kwantar da shi a cinyarta ta kuma kula da shi.
Naomi took the child, laid him in her bosom, and took care of him.
17 Matan da suke zama a wurin suka ce, “Na’omi ta sami yaro.” Suka kuwa ba shi suna Obed. Shi ne ya haifi Yesse, mahaifin Dawuda.
The women of the neighborhood gave him a name, saying, “A son has been born to Naomi.” They named him Obed. He became the father of Jesse, who became the father of David.
18 Ga asalin zuriyar Ferez. Ferez shi ne mahaifin Hezron,
Now these were the descendants of Perez: Perez became the father of Hezron,
19 Hezron ya haifi Ram, Ram ya haifi Amminadab,
Hezron became the father of Ram, Ram became the father of Amminadab,
20 Amminadab ya haifi Nashon, Nashon ya haifi Salmon,
Amminadab became the father of Nahshon, Nahshon became the father of Salmon,
21 Salmon ya haifi Bowaz, Bowaz ya haifi Obed,
Salmon became the father of Boaz, Boaz became the father of Obed,
22 Obed ya haifi Yesse, Yesse kuwa ya haifi Dawuda.
Obed became the father of Jesse, and Jesse became the father of David.

< Rut 4 >