< Rut 1 >

1 A kwanakin da mahukunta suke mulki an yi yunwa a ƙasar, sai wani mutum daga Betlehem a Yahuda tare da matarsa da’ya’yansu maza biyu, suka tafi su yi zama na ɗan lokaci a ƙasar Mowab.
I de dager da dommerne styrte, blev det engang hungersnød i landet. Da drog en mann med sin hustru og sine to sønner avsted fra Betlehem i Juda for å opholde sig nogen tid i Moabs land.
2 Sunan mutumin, Elimelek ne, sunan matarsa Na’omi; sunayen’ya’yan nan nasu biyu, su ne Malon da Kiliyon. Su Efratawa ne daga Betlehem ta Yahuda. Suka kuwa tafi Mowab suka zauna a can.
Mannen hette Elimelek, hans hustru No'omi og hans to sønner Mahlon og Kiljon; de var efratitter - fra Betlehem i Juda. De kom nu til Moabs land og blev der.
3 To, Elimelek mijin Na’omi ya rasu, aka bar ta da’ya’yanta maza biyu.
Så døde Elimelek, No'omis mann, og hun blev tilbake med sine to sønner.
4 Suka auri mata Mowabawa, sunan ɗaya Orfa ɗayan kuma Rut. Bayan sun zauna a can kamar shekara goma,
De tok sig moabittiske hustruer, den ene hette Orpa og den andre Rut; og de bodde der omkring en ti års tid.
5 sai Malon da Kiliyon suka mutu su ma, aka kuma bar Na’omi babu’ya’yanta maza biyu da kuma mijinta.
Da døde også begge sønnene, Mahlon og Kiljon; og kvinnen var tilbake efter sine to sønner og efter sin mann.
6 Sa’ad da ta ji a Mowab cewa Ubangiji ya zo don yă taimaki mutanensa ta wurin tanada musu da abinci, sai Na’omi tare da surukanta suka shirya su koma gida daga can.
Da brøt hun op med sine sønnekoner og vendte tilbake fra Moabs land; for hun hadde hørt i Moabs land at Herren hadde sett til sitt folk og gitt dem brød.
7 Tare da surukanta biyu suka bar inda suka zauna suka kuma kama hanya da za tă komar da su zuwa ƙasar Yahuda.
Hun drog bort fra det sted hvor hun hadde vært, og begge hennes sønnekoner var med henne. Mens de nu gikk frem efter veien for å vende tilbake til Juda land,
8 Sai Na’omi ta ce wa surukanta biyu, “Ku koma, kowannenku, zuwa gidan mahaifiyarta. Bari Ubangiji yă nuna muku alheri yadda kuka nuna wa matattun nan da kuma gare ni.
sa No'omi til sine to sønnekoner: Vend om og gå hjem igjen, hver til sin mors hus. Herren vise godhet mot eder, som I har gjort mot de døde og mot mig!
9 Bari Ubangiji yă sa kowannenku ta sami hutu a gidan wani miji.” Sa’an nan ta sumbace su suka kuma yi kuka da ƙarfi
Herren gi eder at I må finne et hjem, hver i sin manns hus! Og hun kysset dem; men de brast i gråt
10 suka ce mata, “Za mu tafi tare da ke zuwa ga mutanenki.”
og sa til henne: Nei, vi vil følge dig tilbake til ditt folk.
11 Amma Na’omi ta ce, “Ku koma gida,’ya’yana mata. Don me za ku tafi tare da ni? Zan ƙara samun waɗansu’ya’ya maza da za su zama mazanku ne?
Da sa No'omi: Vend om, mine døtre! Hvorfor vil I gå med mig? Har jeg da ennu sønner i mitt liv som kunde bli eders menn?
12 Ku koma gida’ya’yana mata; na tsufa ainun da zan sāke samun wani miji. Ko ma na yi tsammani har yanzu ina da bege, ko ma na sami miji a wannan dare na kuma haifi’ya’ya maza,
Vend om, mine døtre, og gå hjem! For jeg er for gammel til å bli en manns hustru. Om jeg så tenkte: Jeg har ennu håp, ja, om jeg så ennu inatt fikk en mann og så fødte sønner,
13 za ku jira sai sun yi girma? Za ku ci gaba da kasance babu aure saboda su? A’a,’ya’yana mata. Ina da baƙin ciki ƙwarai fiye da ku, domin hannun Ubangiji ya yi gāba da ni!”
skulde I derfor vente til de blev store? Skulde I derfor stenge eder inne og ikke få eder menn? Nei, mine døtre! For det er meget bitrere for mig enn for eder, eftersom Herrens hånd har rammet mig så hårdt.
14 A kan wannan suka sāke ɓarke da kuka. Sa’an nan Orfa ta sumbaci surukarta ta yi bankwana, amma Rut ta manne mata.
Da brast de atter i gråt. Og Orpa kysset sin svigermor og sa henne farvel, men Rut vilde ikke skilles fra henne.
15 Sai Na’omi ta ce, “Duba,’yar’uwanki ta koma zuwa ga mutanenta da kuma allolinta. Ki koma tare da ita.”
Da sa hun: Du ser din svigerinne er vendt tilbake til sitt folk og til sin gud; vend nu du og tilbake og følg din svigerinne!
16 Rut Amma Rut ta amsa, “Kada ki roƙe ni in bar ki ko in koma daga gare ki. Inda za ki, zan tafi, kuma inda za ki zauna, zan zauna. Mutanenki, za su zama mutanena kuma Allahnki, zai zama Allahna.
Men Rut sa: Søk ikke å overtale mig til å forlate dig og vende tilbake! For dit du går, vil jeg gå, og hvor du blir, vil jeg bli; ditt folk er mitt folk, og din Gud er min Gud;
17 Inda za ki mutu zan mutu, zan mutu a can kuma za a binne ni. Bari Ubangiji ya hukunta ni da tsanani sosai, in wani abu in ba mutuwa ce ta raba ke da ni ba.”
hvor du dør, vil jeg dø, og der vil jeg begraves. Herren la det gå mig ille både nu og siden om noget annet enn døden skal skille mig fra dig.
18 Sa’ad da Na’omi ta gane cewa Rut ta ƙudura tă tafi tare da ita, sai ta daina nema tă koma.
Da No'omi så at hun var fast i sitt forsett om å gå med henne, holdt hun op med å tale til henne om det.
19 Saboda haka matan biyu suka ci gaba da tafiya sai da suka isa Betlehem. Da suka isa Betlehem, sai dukan garin ya ruɗe saboda su, matan kuwa suka ce, “Na’omi ce wannan kuwa?”
Så gikk de begge videre til de kom til Betlehem. Og da de kom til Betlehem, kom hele byen i bevegelse for deres skyld, og kvinnene sa: Er dette No'omi?
20 Ta ce musu, “Kada ku kira ni Na’omi. Ku kira ni Mara gama Maɗaukaki ya sa raina ya yi ɗaci sosai.
Da sa hun til dem: Kall mig ikke No'omi, kall mig Mara! For den Allmektige har gjort det meget bittert for mig;
21 In tafi cikakke, amma Ubangiji ya dawo da ni ba kome. Don me kuke kirana Na’omi? Ubangiji ya wahalshe ni, Maɗaukaki ya kawo mini masifa.”
med fulle hender drog jeg bort, men med tomme hender har Herren latt mig vende tilbake. Hvorfor kaller I mig No'omi, når Herren har vidnet imot mig, og den Allmektige har latt det gå mig ille?
22 Na’omi fa ta koma daga Mowab tare da Rut mutuniyar Mowab, surukarta, suka kai Betlehem a lokacin da ake fara girbin sha’ir.
Så kom da No'omi tilbake med sin sønnekone, moabittinnen Rut - hun var vendt tilbake fra Moabs land; og de kom til Betlehem i begynnelsen av bygghøsten.

< Rut 1 >