< Zabura 9 >

1 Don mai bi da kaɗe-kaɗe. Ga muryar “Mutuwar Ɗa.” Zabura ta Dawuda. Zan yabe ka, ya Ubangiji, da dukan zuciyata; zan faɗa dukan abubuwan banmamakinka.
For the Chief Musician. Set to “The Death of the Son.” A Psalm by David. I will give thanks to Yahweh with my whole heart. I will tell of all your marvelous works.
2 Zan yi murna in kuma yi farin ciki a cikinka; zan rera yabo ga sunanka, ya Mafi Ɗaukaka.
I will be glad and rejoice in you. I will sing praise to your name, O Most High.
3 Abokan gābana sun ja da baya; suka yi tuntuɓe suka hallaka a gabanka.
When my enemies turn back, they stumble and perish in your presence.
4 Gama ka tabbata da gaskiyata da kuma abin da nake yi; ka zauna a kujerarka, kana yin shari’a da adalci.
For you have maintained my just cause. You sit on the throne judging righteously.
5 Ka tsawata wa ƙasashe ka kuma hallakar da mugaye; ka shafe sunansu har abada abadin.
You have rebuked the nations. You have destroyed the wicked. You have blotted out their name forever and ever.
6 Lalaci marar ƙarewa ya cimma abokan gābanmu, ka tuttumɓuke biranensu; yadda ma ba aka ƙara tunaninsu.
The enemy is overtaken by endless ruin. The very memory of the cities which you have overthrown has perished.
7 Ubangiji yana mulki har abada; ya kafa kujerarsa don shari’a.
But Yahweh reigns forever. He has prepared his throne for judgment.
8 Zai hukunta duniya da adalci; zai yi mulkin mutane cikin gaskiya.
He will judge the world in righteousness. He will administer judgment to the peoples in uprightness.
9 Ubangiji shi ne mafakan waɗanda ake danniya, mafaka a lokutan wahala.
Yahweh will also be a high tower for the oppressed; a high tower in times of trouble.
10 Waɗanda suka san sunanka za su dogara da kai, gama kai, Ubangiji, ba ka taɓa yashe waɗanda suke nemanka ba.
Those who know your name will put their trust in you, for you, Yahweh, have not forsaken those who seek you.
11 Rera yabai ga Ubangiji, wanda yake zaune a kursiyi a Sihiyona; yi shela a cikin al’ummai abin da ya aikata.
Sing praises to Yahweh, who dwells in Zion, and declare among the people what he has done.
12 Gama shi da yakan ɗauki fansa a kan mai kisa yakan tuna; ba ya ƙyale kukan masu wahala.
For he who avenges blood remembers them. He doesn’t forget the cry of the afflicted.
13 Ya Ubangiji, dubi yadda abokan gābana suna tsananta mini! Ka yi jinƙai ka kuma ɗaga ni daga ƙofofin mutuwa,
Have mercy on me, Yahweh. See my affliction by those who hate me, and lift me up from the gates of death,
14 don in furta yabanka cikin ƙofofin’Yar Sihiyona a can kuwa in yi farin ciki cikin cetonka.
that I may show all of your praise. I will rejoice in your salvation in the gates of the daughter of Zion.
15 Al’umma sun fāɗa cikin ramin da suka haƙa wa waɗansu; aka kama ƙafafunsu a ragar da suka ɓoye.
The nations have sunk down in the pit that they made. In the net which they hid, their own foot is taken.
16 An san Ubangiji ta wurin gaskiyarsa; an kama mugaye da aikin hannuwansu. Haggayiyon. (Sela)
Yahweh has made himself known. He has executed judgment. The wicked is snared by the work of his own hands. (Meditation, Selah)
17 Mugaye za su koma kabari, dukan al’umman da suka manta da Allah. (Sheol h7585)
The wicked shall be turned back to Sheol, even all the nations that forget God. (Sheol h7585)
18 Amma har abada ba za a manta da mai bukata ba, ba kuwa sa zuciyar mai wahala zai taɓa hallaka.
For the needy shall not always be forgotten, nor the hope of the poor perish forever.
19 Ka tashi, ya Ubangiji, kada ka bar wani yă yi nasara; bari a hukunta al’ummai a gabanka.
Arise, Yahweh! Don’t let man prevail. Let the nations be judged in your sight.
20 Ka buge su da rawar jiki, ya Ubangiji; bari al’ummai su sani su mutane ne kurum. (Sela)
Put them in fear, Yahweh. Let the nations know that they are only men. (Selah)

< Zabura 9 >