< Zabura 89 >

1 Maskil na Etan dangin Ezra. Zan rera game da ƙauna mai girma ta Ubangiji har abada; da bakina zan sanar da amincinka a dukan zamanai.
قصیده ایتان ازراحی رحمت های خداوند را تا به ابد خواهم سرایید. امانت تو را به دهان خود نسلابعد نسل اعلام خواهم کرد.۱
2 Zan furta cewa ƙaunarka tana nan daram har abada, cewa ka kafa amincinka a sama kanta.
زیرا گفتم رحمت بنا خواهد شد تا ابدالاباد و امانت خویش را درافلاک پایدار خواهی ساخت.۲
3 Ka ce, “Na yi alkawari da zaɓaɓɓena, na rantse wa Dawuda bawana,
با برگزیده خودعهد بسته‌ام. برای بنده خویش داود قسم خورده‌ام.۳
4 cewa ‘Zan kafa zuriyarka har abada in kuma sa kursiyinka yă tsaya daram dukan zamanai.’” (Sela)
که ذریت تو را پایدار خواهم ساخت تا ابدالاباد و تخت تو را نسلا بعد نسل بنا خواهم نمود، سلاه.۴
5 Sammai na yabon abubuwan banmamakinka, ya Ubangiji, amincinka shi ma, a cikin taron tsarkakanka.
و آسمانها کارهای عجیب تو را‌ای خداوند تمجید خواهند کرد و امانت تو را درجماعت مقدسان.۵
6 Gama wane ne a sarari za a iya kwatanta da Ubangiji? Wane ne yake kamar Ubangiji a cikin talikan samaniya?
زیرا کیست در آسمانها که باخداوند برابری تواند کرد؟ و از فرزندان زورآوران که را با خداوند تشبیه توان نمود؟۶
7 Cikin taron tsarkaka Allah ne aka fi tsoro; shi ne mafi bantsoro fiye da dukan waɗanda suka kewaye shi.
خدا بی‌نهایت مهیب است در جماعت مقدسان و ترسناک است بر آنانی که گرداگرد او هستند.۷
8 Ya Ubangiji Allah Maɗaukaki, wane ne kamar ka? Kai mai iko ne, ya Ubangiji, kuma amincinka ya kewaye ka.
‌ای یهوه خدای لشکرها! کیست‌ای یاه قدیرمانند تو؟ و امانت تو، تو را احاطه می‌کند.۸
9 Kana mulkin teku mai tumbatsa; sa’ad da raƙuma sun tashi, kakan kwantar da su.
برتکبر دریا تو مسلط هستی. چون امواجش بلندمی شود، آنها را ساکن می‌گردانی.۹
10 Ka ragargaza Rahab kamar waɗanda aka kashe; da hannunka mai ƙarfi ka watsar da abokan gābanka.
رهب را مثل کشته شده خرد شکسته‌ای. به بازوی زورآورخویش دشمنانت را پراکنده نموده‌ای.۱۰
11 Sammai naka ne, haka kuma duniya; ka kafa duniya da dukan abin da yake cikinta.
آسمان از آن تو است و زمین نیز از آن تو. ربع مسکون وپری آن را تو بنیاد نهاده‌ای.۱۱
12 Ka halicce arewa da kudu; Tabor da Hermon suna rera don farin ciki ga sunanka.
شمال و جنوب راتو آفریده‌ای. تابور و حرمون به نام تو شادی می‌کنند.۱۲
13 Hannunka mai iko ne; hannunka yana da ƙarfi, hannunka na dama ya sami ɗaukaka.
بازوی تو با قوت است. دست توزورآور است و دست راست تو متعال.۱۳
14 Adalci da gaskiya su ne tushen kursiyinka; ƙauna da aminci suna tafiya a gabanka.
عدالت و انصاف اساس تخت تو است. رحمت و راستی پیش روی تو می‌خرامند.۱۴
15 Masu albarka ne waɗanda suka koyi yin maka kirari waɗanda suke tafiya cikin hasken da yake gabanka, Ubangiji.
خوشابحال قومی که آواز شادمانی رامی دانند. در نور روی تو‌ای خداوند خواهندخرامید.۱۵
16 Suna farin ciki a cikin sunanka dukan yini; suna samun ɗaukaka cikin adalcinka.
در نام تو شادمان خواهند شد تمامی روز و در عدالت تو سرافراشته خواهند گردید.۱۶
17 Gama kai ne ɗaukakarsu da ƙarfinsu, kuma ta wurin alherinka ka ɗaukaka ƙahonka.
زیرا که فخر قوت ایشان تو هستی و به رضامندی تو شاخ ما مرتفع خواهد شد.۱۷
18 Tabbatacce, garkuwarmu ta Ubangiji ce, ta sarkinmu ce, da kuma ta Mai Tsarki na Isra’ila ce.
زیراکه سپر ما از آن خداوند است و پادشاه ما از آن قدوس اسرائیل.۱۸
19 Ka taɓa yin magana cikin wahayi, ga mutanenka masu aminci ka ce, “Na ba wa jarumi ƙarfi; na ɗaukaka saurayi daga cikin mutane.
آنگاه در عالم رویا به مقدس خود خطاب کرده، گفتی که نصرت را بر مردی زورآور نهادم و برگزیده‌ای از قوم را ممتاز کردم.۱۹
20 Na sami Dawuda bawana; da mai na mai tsarki na shafe shi.
بنده خود داود را یافتم و او را به روغن مقدس خود مسح کردم.۲۰
21 Hannuna zai kasance tare da shi; tabbatacce hannuna zai ƙarfafa shi.
که دست من با او استوارخواهد شد. بازوی من نیز او را قوی خواهدگردانید.۲۱
22 Babu abokin gāban da zai sa yă biya haraji; babu mugun mutumin da zai danne shi.
دشمنی بر او ستم نخواهد کرد و هیچ پسر ظلم بدو اذیت نخواهد رسانید.۲۲
23 Zan murƙushe maƙiyansa a gabansa in kashe dukan abokan gābansa.
و خصمان او را پیش روی وی خواهم گرفت و آنانی را که ازاو نفرت دارند مبتلا خواهم گردانید.۲۳
24 Amintacciya ƙaunata za tă kasance tare da shi, kuma ta wurin sunana za a ɗaukaka ƙahonsa.
و امانت ورحمت من با وی خواهد بود و در نام من شاخ اومرتفع خواهد شد.۲۴
25 Zan sa hannunsa a bisa teku, hannunsa na dama a bisa koguna.
دست او را بر دریا مستولی خواهم ساخت و دست راست او را بر نهرها.۲۵
26 Zai yi kira gare ni yă ce, ‘Kai ne Mahaifina, Allahna, Dutse mai cetona.’
او مرا خواهد خواند که تو پدر من هستی، خدای من و صخره نجات من.۲۶
27 Zan kuma naɗa shi ɗan farina, mafi ɗaukaka cikin sarakunan duniya.
من نیز او رانخست زاده خود خواهم ساخت، بلندتر ازپادشاهان جهان.۲۷
28 Zan ci gaba da ƙaunarsa har abada, alkawarina da shi ba zai taɓa fasa ba.
رحمت خویش را برای وی نگاه خواهم داشت تا ابدالاباد و عهد من با اواستوار خواهد بود.۲۸
29 Zan kafa zuriyarsa har abada, kursiyinsa muddin sammai suna nan.
و ذریت وی را باقی خواهم داشت تا ابدالاباد و تخت او را مثل روزهای آسمان.۲۹
30 “In’ya’yansa maza suka yashe dokata ba su kuwa bi ƙa’idodina ba,
اگر فرزندانش شریعت مرا ترک کنند، و دراحکام من سلوک ننمایند،۳۰
31 in suka take ƙa’idodina suka kuma kāsa kiyaye umarnaina,
اگر فرایض مرابشکنند، و اوامر مرا نگاه ندارند،۳۱
32 zan hukunta zunubinsu da sanda, laifinsu da bulala;
آنگاه معصیت ایشان را به عصا تادیب خواهم نمود وگناه ایشان را به تازیانه‌ها.۳۲
33 amma ba zan ɗauke ƙaunata daga gare shi ba, ba kuwa zan taɓa rasa cika amincina ba.
لیکن رحمت خود رااز او برنخواهم داشت و امانت خویش را باطل نخواهم ساخت.۳۳
34 Ba zan take alkawarina ba ko in canja abin da leɓunana suka ambata.
عهد خود را نخواهم شکست و آنچه را از دهانم صادر شد تغییر نخواهم داد.۳۴
35 Sau ɗaya ba ƙari, na rantse da tsarkina, ba kuwa zan yi ƙarya wa Dawuda ba,
یک چیز را به قدوسیت خود قسم خوردم و به داود هرگز دروغ نخواهم گفت.۳۵
36 cewa zuriyarsa za tă ci gaba har abada kuma kursiyinsa zai dawwama a gabana kamar rana;
که ذریت اوباقی خواهد بود تا ابدالاباد و تخت او به حضورمن مثل آفتاب،۳۶
37 zai kahu har abada kamar wata, amintacciyar shaida a cikin sarari.” (Sela)
مثل ماه ثابت خواهد بود تاابدالاباد و مثل شاهد امین در آسمان، سلاه.۳۷
38 Amma ka ƙi, ka yi ƙyama ka kuma yi fushi sosai da shafaffenka.
لیکن تو ترک کرده‌ای و دور انداخته‌ای و بامسیح خود غضبناک شده‌ای.۳۸
39 Ka soke alkawarin da ka yi da bawanka ka kuma ƙazantar da rawaninsa a ƙura.
عهد بنده خودرا باطل ساخته‌ای و تاج او را بر زمین انداخته، بی‌عصمت کرده‌ای.۳۹
40 Ka rurrushe dukan katangansa ka sa kagaransa suka zama kufai.
جمیع حصارهایش راشکسته و قلعه های او را خراب نموده‌ای.۴۰
41 Dukan waɗanda suka wuce sun washe shi; ya zama abin dariya wajen maƙwabtansa.
همه راه گذران او را تاراج می‌کنند و او نزد همسایگان خود عار گردیده است.۴۱
42 Ka ɗaukaka hannun dama na maƙiyansa; ka sa dukan abokan gābansa suna farin ciki.
دست راست خصمان او را برافراشته، و همه دشمنانش را مسرورساخته‌ای.۴۲
43 Ka juye bakin takobinsa ba ka kuma taimake shi a cikin yaƙi ba.
دم شمشیر او را نیز برگردانیده‌ای واو را در جنگ پایدار نساخته‌ای.۴۳
44 Ka kawo ƙarshen darajarsa ka kuma jefar da kursiyinsa ƙasa.
جلال او راباطل ساخته و تخت او را به زمین انداخته‌ای.۴۴
45 Ka rage kwanakin ƙuruciyarsa; ka rufe shi da mayafin kunya. (Sela)
ایام شبابش را کوتاه کرده، و او را به خجالت پوشانیده‌ای، سلاه.۴۵
46 Har yaushe, ya Ubangiji za ka ɓoye? Za ka ɓoye har abada ne? Har yaushe fushinka zai yi ta ci kamar wuta?
تا به کی‌ای خداوند خود را تا به ابد پنهان خواهی کرد و غضب تو مثل آتش افروخته خواهد شد؟۴۶
47 Ka tuna yadda raina mai wucewa ne. Gama ka halicce dukan mutane ba amfani!
به یاد آور که ایام حیاتم چه کم است. چرا تمامی بنی آدم را برای بطالت آفریده‌ای؟۴۷
48 Wanda mutum ne zai rayu da ba zai ga mutuwa ba, ko yă cece kansa daga ikon kabari? (Sela) (Sheol h7585)
کدام آدمی زنده است که موت رانخواهد دید؟ و جان خویش را از دست قبرخلاص خواهد ساخت؟ سلاه. (Sheol h7585)۴۸
49 Ya Ubangiji, ina ƙaunar mai girma ta dā, wadda cikin amincinka ka rantse wa Dawuda?
‌ای خداوندرحمت های قدیم تو کجاست؟ که برای داود به امانت خود قسم خوردی.۴۹
50 Ka tuna, Ubangiji, yadda aka yi wa bawanka ba’a, yadda na jimre a zuciyata da zage-zagen dukan al’ummai,
‌ای خداوند ملامت بنده خود را به یاد آور که آن را از قومهای بسیاردر سینه خود متحمل می‌باشم.۵۰
51 zage-zagen da abokan gābanka suka yi mini, ya Ubangiji, da suka yi wa kowane matakin da shafaffenka ya ɗauka.
که دشمنان توای خداوند ملامت کرده‌اند، یعنی آثار مسیح تورا ملامت نموده‌اند.۵۱
52 Yabo ya tabbata ga Ubangiji har abada!
خداوند متبارک باد تاابدالاباد. آمین و آمین.۵۲

< Zabura 89 >