< Zabura 89 >

1 Maskil na Etan dangin Ezra. Zan rera game da ƙauna mai girma ta Ubangiji har abada; da bakina zan sanar da amincinka a dukan zamanai.
A contemplation by Ethan, the Ezrahite. I will sing of the loving kindness of Yahweh forever. With my mouth, I will make known your faithfulness to all generations.
2 Zan furta cewa ƙaunarka tana nan daram har abada, cewa ka kafa amincinka a sama kanta.
I indeed declare, “Love stands firm forever. You established the heavens. Your faithfulness is in them.”
3 Ka ce, “Na yi alkawari da zaɓaɓɓena, na rantse wa Dawuda bawana,
“I have made a covenant with my chosen one, I have sworn to David, my servant,
4 cewa ‘Zan kafa zuriyarka har abada in kuma sa kursiyinka yă tsaya daram dukan zamanai.’” (Sela)
‘I will establish your offspring forever, and build up your throne to all generations.’” (Selah)
5 Sammai na yabon abubuwan banmamakinka, ya Ubangiji, amincinka shi ma, a cikin taron tsarkakanka.
The heavens will praise your wonders, Yahweh, your faithfulness also in the assembly of the holy ones.
6 Gama wane ne a sarari za a iya kwatanta da Ubangiji? Wane ne yake kamar Ubangiji a cikin talikan samaniya?
For who in the skies can be compared to Yahweh? Who among the sons of the heavenly beings is like Yahweh,
7 Cikin taron tsarkaka Allah ne aka fi tsoro; shi ne mafi bantsoro fiye da dukan waɗanda suka kewaye shi.
a very awesome God in the council of the holy ones, to be feared above all those who are around him?
8 Ya Ubangiji Allah Maɗaukaki, wane ne kamar ka? Kai mai iko ne, ya Ubangiji, kuma amincinka ya kewaye ka.
Yahweh, God of Armies, who is a mighty one, like you? Yah, your faithfulness is around you.
9 Kana mulkin teku mai tumbatsa; sa’ad da raƙuma sun tashi, kakan kwantar da su.
You rule the pride of the sea. When its waves rise up, you calm them.
10 Ka ragargaza Rahab kamar waɗanda aka kashe; da hannunka mai ƙarfi ka watsar da abokan gābanka.
You have broken Rahab in pieces, like one of the slain. You have scattered your enemies with your mighty arm.
11 Sammai naka ne, haka kuma duniya; ka kafa duniya da dukan abin da yake cikinta.
The heavens are yours. The earth also is yours, the world and its fullness. You have founded them.
12 Ka halicce arewa da kudu; Tabor da Hermon suna rera don farin ciki ga sunanka.
You have created the north and the south. Tabor and Hermon rejoice in your name.
13 Hannunka mai iko ne; hannunka yana da ƙarfi, hannunka na dama ya sami ɗaukaka.
You have a mighty arm. Your hand is strong, and your right hand is exalted.
14 Adalci da gaskiya su ne tushen kursiyinka; ƙauna da aminci suna tafiya a gabanka.
Righteousness and justice are the foundation of your throne. Loving kindness and truth go before your face.
15 Masu albarka ne waɗanda suka koyi yin maka kirari waɗanda suke tafiya cikin hasken da yake gabanka, Ubangiji.
Blessed are the people who learn to acclaim you. They walk in the light of your presence, Yahweh.
16 Suna farin ciki a cikin sunanka dukan yini; suna samun ɗaukaka cikin adalcinka.
In your name they rejoice all day. In your righteousness, they are exalted.
17 Gama kai ne ɗaukakarsu da ƙarfinsu, kuma ta wurin alherinka ka ɗaukaka ƙahonka.
For you are the glory of their strength. In your favor, our horn will be exalted.
18 Tabbatacce, garkuwarmu ta Ubangiji ce, ta sarkinmu ce, da kuma ta Mai Tsarki na Isra’ila ce.
For our shield belongs to Yahweh, our king to the Holy One of Israel.
19 Ka taɓa yin magana cikin wahayi, ga mutanenka masu aminci ka ce, “Na ba wa jarumi ƙarfi; na ɗaukaka saurayi daga cikin mutane.
Then you spoke in vision to your saints, and said, “I have given strength to the warrior. I have exalted a young man from the people.
20 Na sami Dawuda bawana; da mai na mai tsarki na shafe shi.
I have found David, my servant. I have anointed him with my holy oil,
21 Hannuna zai kasance tare da shi; tabbatacce hannuna zai ƙarfafa shi.
with whom my hand shall be established. My arm will also strengthen him.
22 Babu abokin gāban da zai sa yă biya haraji; babu mugun mutumin da zai danne shi.
No enemy will tax him. No wicked man will oppress him.
23 Zan murƙushe maƙiyansa a gabansa in kashe dukan abokan gābansa.
I will beat down his adversaries before him, and strike those who hate him.
24 Amintacciya ƙaunata za tă kasance tare da shi, kuma ta wurin sunana za a ɗaukaka ƙahonsa.
But my faithfulness and my loving kindness will be with him. In my name, his horn will be exalted.
25 Zan sa hannunsa a bisa teku, hannunsa na dama a bisa koguna.
I will set his hand also on the sea, and his right hand on the rivers.
26 Zai yi kira gare ni yă ce, ‘Kai ne Mahaifina, Allahna, Dutse mai cetona.’
He will call to me, ‘You are my Father, my God, and the rock of my salvation!’
27 Zan kuma naɗa shi ɗan farina, mafi ɗaukaka cikin sarakunan duniya.
I will also appoint him my firstborn, the highest of the kings of the earth.
28 Zan ci gaba da ƙaunarsa har abada, alkawarina da shi ba zai taɓa fasa ba.
I will keep my loving kindness for him forever more. My covenant will stand firm with him.
29 Zan kafa zuriyarsa har abada, kursiyinsa muddin sammai suna nan.
I will also make his offspring endure forever, and his throne as the days of heaven.
30 “In’ya’yansa maza suka yashe dokata ba su kuwa bi ƙa’idodina ba,
If his children forsake my law, and don’t walk in my ordinances;
31 in suka take ƙa’idodina suka kuma kāsa kiyaye umarnaina,
if they break my statutes, and don’t keep my commandments;
32 zan hukunta zunubinsu da sanda, laifinsu da bulala;
then I will punish their sin with the rod, and their iniquity with stripes.
33 amma ba zan ɗauke ƙaunata daga gare shi ba, ba kuwa zan taɓa rasa cika amincina ba.
But I will not completely take my loving kindness from him, nor allow my faithfulness to fail.
34 Ba zan take alkawarina ba ko in canja abin da leɓunana suka ambata.
I will not break my covenant, nor alter what my lips have uttered.
35 Sau ɗaya ba ƙari, na rantse da tsarkina, ba kuwa zan yi ƙarya wa Dawuda ba,
Once I have sworn by my holiness, I will not lie to David.
36 cewa zuriyarsa za tă ci gaba har abada kuma kursiyinsa zai dawwama a gabana kamar rana;
His offspring will endure forever, his throne like the sun before me.
37 zai kahu har abada kamar wata, amintacciyar shaida a cikin sarari.” (Sela)
It will be established forever like the moon, the faithful witness in the sky.” (Selah)
38 Amma ka ƙi, ka yi ƙyama ka kuma yi fushi sosai da shafaffenka.
But you have rejected and spurned. You have been angry with your anointed.
39 Ka soke alkawarin da ka yi da bawanka ka kuma ƙazantar da rawaninsa a ƙura.
You have renounced the covenant of your servant. You have defiled his crown in the dust.
40 Ka rurrushe dukan katangansa ka sa kagaransa suka zama kufai.
You have broken down all his hedges. You have brought his strongholds to ruin.
41 Dukan waɗanda suka wuce sun washe shi; ya zama abin dariya wajen maƙwabtansa.
All who pass by the way rob him. He has become a reproach to his neighbors.
42 Ka ɗaukaka hannun dama na maƙiyansa; ka sa dukan abokan gābansa suna farin ciki.
You have exalted the right hand of his adversaries. You have made all of his enemies rejoice.
43 Ka juye bakin takobinsa ba ka kuma taimake shi a cikin yaƙi ba.
Yes, you turn back the edge of his sword, and haven’t supported him in battle.
44 Ka kawo ƙarshen darajarsa ka kuma jefar da kursiyinsa ƙasa.
You have ended his splendor, and thrown his throne down to the ground.
45 Ka rage kwanakin ƙuruciyarsa; ka rufe shi da mayafin kunya. (Sela)
You have shortened the days of his youth. You have covered him with shame. (Selah)
46 Har yaushe, ya Ubangiji za ka ɓoye? Za ka ɓoye har abada ne? Har yaushe fushinka zai yi ta ci kamar wuta?
How long, Yahweh? Will you hide yourself forever? Will your wrath burn like fire?
47 Ka tuna yadda raina mai wucewa ne. Gama ka halicce dukan mutane ba amfani!
Remember how short my time is, for what vanity you have created all the children of men!
48 Wanda mutum ne zai rayu da ba zai ga mutuwa ba, ko yă cece kansa daga ikon kabari? (Sela) (Sheol h7585)
What man is he who shall live and not see death, who shall deliver his soul from the power of Sheol? (Selah) (Sheol h7585)
49 Ya Ubangiji, ina ƙaunar mai girma ta dā, wadda cikin amincinka ka rantse wa Dawuda?
Lord, where are your former loving kindnesses, which you swore to David in your faithfulness?
50 Ka tuna, Ubangiji, yadda aka yi wa bawanka ba’a, yadda na jimre a zuciyata da zage-zagen dukan al’ummai,
Remember, Lord, the reproach of your servants, how I bear in my heart the taunts of all the mighty peoples,
51 zage-zagen da abokan gābanka suka yi mini, ya Ubangiji, da suka yi wa kowane matakin da shafaffenka ya ɗauka.
With which your enemies have mocked, Yahweh, with which they have mocked the footsteps of your anointed one.
52 Yabo ya tabbata ga Ubangiji har abada!
Blessed be Yahweh forever more. Amen, and Amen.

< Zabura 89 >