< Zabura 89 >

1 Maskil na Etan dangin Ezra. Zan rera game da ƙauna mai girma ta Ubangiji har abada; da bakina zan sanar da amincinka a dukan zamanai.
Maschil of Ethan the Ezrahite. I will sing of the mercies of the LORD for ever: with my mouth will I make known thy faithfulness to all generations.
2 Zan furta cewa ƙaunarka tana nan daram har abada, cewa ka kafa amincinka a sama kanta.
For I have said, Mercy shall be built up for ever: thy faithfulness shalt thou establish in the very heavens.
3 Ka ce, “Na yi alkawari da zaɓaɓɓena, na rantse wa Dawuda bawana,
I have made a covenant with my chosen, I have sworn unto David my servant,
4 cewa ‘Zan kafa zuriyarka har abada in kuma sa kursiyinka yă tsaya daram dukan zamanai.’” (Sela)
Thy seed will I establish for ever, and build up thy throne to all generations. (Selah)
5 Sammai na yabon abubuwan banmamakinka, ya Ubangiji, amincinka shi ma, a cikin taron tsarkakanka.
And the heavens shall praise thy wonders, O LORD: thy faithfulness also in the congregation of the saints.
6 Gama wane ne a sarari za a iya kwatanta da Ubangiji? Wane ne yake kamar Ubangiji a cikin talikan samaniya?
For who in the heaven can be compared unto the LORD? [who] among the sons of the mighty can be likened unto the LORD?
7 Cikin taron tsarkaka Allah ne aka fi tsoro; shi ne mafi bantsoro fiye da dukan waɗanda suka kewaye shi.
God is greatly to be feared in the assembly of the saints, and to be had in reverence of all [them that are] about him.
8 Ya Ubangiji Allah Maɗaukaki, wane ne kamar ka? Kai mai iko ne, ya Ubangiji, kuma amincinka ya kewaye ka.
O LORD God of hosts, who [is] a strong LORD like unto thee? or to thy faithfulness round about thee?
9 Kana mulkin teku mai tumbatsa; sa’ad da raƙuma sun tashi, kakan kwantar da su.
Thou rulest the raging of the sea: when the waves thereof arise, thou stillest them.
10 Ka ragargaza Rahab kamar waɗanda aka kashe; da hannunka mai ƙarfi ka watsar da abokan gābanka.
Thou hast broken Rahab in pieces, as one that is slain; thou hast scattered thine enemies with thy strong arm.
11 Sammai naka ne, haka kuma duniya; ka kafa duniya da dukan abin da yake cikinta.
The heavens [are] thine, the earth also [is] thine: [as for] the world and the fulness thereof, thou hast founded them.
12 Ka halicce arewa da kudu; Tabor da Hermon suna rera don farin ciki ga sunanka.
The north and the south thou hast created them: Tabor and Hermon shall rejoice in thy name.
13 Hannunka mai iko ne; hannunka yana da ƙarfi, hannunka na dama ya sami ɗaukaka.
Thou hast a mighty arm: strong is thy hand, [and] high is thy right hand.
14 Adalci da gaskiya su ne tushen kursiyinka; ƙauna da aminci suna tafiya a gabanka.
Justice and judgment [are] the habitation of thy throne: mercy and truth shall go before thy face.
15 Masu albarka ne waɗanda suka koyi yin maka kirari waɗanda suke tafiya cikin hasken da yake gabanka, Ubangiji.
Blessed [is] the people that know the joyful sound: they shall walk, O LORD, in the light of thy countenance.
16 Suna farin ciki a cikin sunanka dukan yini; suna samun ɗaukaka cikin adalcinka.
In thy name shall they rejoice all the day: and in thy righteousness shall they be exalted.
17 Gama kai ne ɗaukakarsu da ƙarfinsu, kuma ta wurin alherinka ka ɗaukaka ƙahonka.
For thou [art] the glory of their strength: and in thy favour our horn shall be exalted.
18 Tabbatacce, garkuwarmu ta Ubangiji ce, ta sarkinmu ce, da kuma ta Mai Tsarki na Isra’ila ce.
For the LORD [is] our defence; and the Holy One of Israel [is] our king.
19 Ka taɓa yin magana cikin wahayi, ga mutanenka masu aminci ka ce, “Na ba wa jarumi ƙarfi; na ɗaukaka saurayi daga cikin mutane.
Then thou spakest in vision to thy holy one, and saidst, I have laid help upon [one that is] mighty; I have exalted [one] chosen out of the people.
20 Na sami Dawuda bawana; da mai na mai tsarki na shafe shi.
I have found David my servant; with my holy oil have I anointed him:
21 Hannuna zai kasance tare da shi; tabbatacce hannuna zai ƙarfafa shi.
With whom my hand shall be established: mine arm also shall strengthen him.
22 Babu abokin gāban da zai sa yă biya haraji; babu mugun mutumin da zai danne shi.
The enemy shall not exact upon him; nor the son of wickedness afflict him.
23 Zan murƙushe maƙiyansa a gabansa in kashe dukan abokan gābansa.
And I will beat down his foes before his face, and plague them that hate him.
24 Amintacciya ƙaunata za tă kasance tare da shi, kuma ta wurin sunana za a ɗaukaka ƙahonsa.
But my faithfulness and my mercy [shall be] with him: and in my name shall his horn be exalted.
25 Zan sa hannunsa a bisa teku, hannunsa na dama a bisa koguna.
I will set his hand also in the sea, and his right hand in the rivers.
26 Zai yi kira gare ni yă ce, ‘Kai ne Mahaifina, Allahna, Dutse mai cetona.’
He shall cry unto me, Thou [art] my father, my God, and the rock of my salvation.
27 Zan kuma naɗa shi ɗan farina, mafi ɗaukaka cikin sarakunan duniya.
Also I will make him [my] firstborn, higher than the kings of the earth.
28 Zan ci gaba da ƙaunarsa har abada, alkawarina da shi ba zai taɓa fasa ba.
My mercy will I keep for him for evermore, and my covenant shall stand fast with him.
29 Zan kafa zuriyarsa har abada, kursiyinsa muddin sammai suna nan.
His seed also will I make [to endure] for ever, and his throne as the days of heaven.
30 “In’ya’yansa maza suka yashe dokata ba su kuwa bi ƙa’idodina ba,
If his children forsake my law, and walk not in my judgments;
31 in suka take ƙa’idodina suka kuma kāsa kiyaye umarnaina,
If they break my statutes, and keep not my commandments;
32 zan hukunta zunubinsu da sanda, laifinsu da bulala;
Then will I visit their transgression with the rod, and their iniquity with stripes.
33 amma ba zan ɗauke ƙaunata daga gare shi ba, ba kuwa zan taɓa rasa cika amincina ba.
Nevertheless my lovingkindness will I not utterly take from him, nor suffer my faithfulness to fail.
34 Ba zan take alkawarina ba ko in canja abin da leɓunana suka ambata.
My covenant will I not break, nor alter the thing that is gone out of my lips.
35 Sau ɗaya ba ƙari, na rantse da tsarkina, ba kuwa zan yi ƙarya wa Dawuda ba,
Once have I sworn by my holiness that I will not lie unto David.
36 cewa zuriyarsa za tă ci gaba har abada kuma kursiyinsa zai dawwama a gabana kamar rana;
His seed shall endure for ever, and his throne as the sun before me.
37 zai kahu har abada kamar wata, amintacciyar shaida a cikin sarari.” (Sela)
It shall be established for ever as the moon, and [as] a faithful witness in heaven. (Selah)
38 Amma ka ƙi, ka yi ƙyama ka kuma yi fushi sosai da shafaffenka.
But thou hast cast off and abhorred, thou hast been wroth with thine anointed.
39 Ka soke alkawarin da ka yi da bawanka ka kuma ƙazantar da rawaninsa a ƙura.
Thou hast made void the covenant of thy servant: thou hast profaned his crown [by casting it] to the ground.
40 Ka rurrushe dukan katangansa ka sa kagaransa suka zama kufai.
Thou hast broken down all his hedges; thou hast brought his strong holds to ruin.
41 Dukan waɗanda suka wuce sun washe shi; ya zama abin dariya wajen maƙwabtansa.
All that pass by the way spoil him: he is a reproach to his neighbours.
42 Ka ɗaukaka hannun dama na maƙiyansa; ka sa dukan abokan gābansa suna farin ciki.
Thou hast set up the right hand of his adversaries; thou hast made all his enemies to rejoice.
43 Ka juye bakin takobinsa ba ka kuma taimake shi a cikin yaƙi ba.
Thou hast also turned the edge of his sword, and hast not made him to stand in the battle.
44 Ka kawo ƙarshen darajarsa ka kuma jefar da kursiyinsa ƙasa.
Thou hast made his glory to cease, and cast his throne down to the ground.
45 Ka rage kwanakin ƙuruciyarsa; ka rufe shi da mayafin kunya. (Sela)
The days of his youth hast thou shortened: thou hast covered him with shame. (Selah)
46 Har yaushe, ya Ubangiji za ka ɓoye? Za ka ɓoye har abada ne? Har yaushe fushinka zai yi ta ci kamar wuta?
How long, LORD? wilt thou hide thyself for ever? shall thy wrath burn like fire?
47 Ka tuna yadda raina mai wucewa ne. Gama ka halicce dukan mutane ba amfani!
Remember how short my time is: wherefore hast thou made all men in vain?
48 Wanda mutum ne zai rayu da ba zai ga mutuwa ba, ko yă cece kansa daga ikon kabari? (Sela) (Sheol h7585)
What man [is he that] liveth, and shall not see death? shall he deliver his soul from the hand of the grave? (Selah) (Sheol h7585)
49 Ya Ubangiji, ina ƙaunar mai girma ta dā, wadda cikin amincinka ka rantse wa Dawuda?
Lord, where [are] thy former lovingkindnesses, [which] thou swarest unto David in thy truth?
50 Ka tuna, Ubangiji, yadda aka yi wa bawanka ba’a, yadda na jimre a zuciyata da zage-zagen dukan al’ummai,
Remember, Lord, the reproach of thy servants; [how] I do bear in my bosom [the reproach of] all the mighty people;
51 zage-zagen da abokan gābanka suka yi mini, ya Ubangiji, da suka yi wa kowane matakin da shafaffenka ya ɗauka.
Wherewith thine enemies have reproached, O LORD; wherewith they have reproached the footsteps of thine anointed.
52 Yabo ya tabbata ga Ubangiji har abada!
Blessed [be] the LORD for evermore. Amen, and Amen.

< Zabura 89 >