< Zabura 78 >

1 Maskil na Asaf. Ya mutanena, ku ji koyarwata; ku saurari kalmomin bakina.
[A Psalm] of instruction for Asaph. Give heed, O my people, to my law: incline your ear to the words of my mouth.
2 Zan buɗe bakina da misalai, zan faɗi ɓoyayyun abubuwa, abubuwan dā,
I will open my mouth in parables: I will utter dark sayings [which have been] from the beginning.
3 abin da muka ji muka kuma sani, abubuwan da kakanninmu suka faɗa mana.
All which we have heard and known, and our fathers have declared to us.
4 Ba za mu ɓoye su wa’ya’yanmu ba; za mu faɗa wa tsara mai zuwa ayyukan da suka zama yabo na Ubangiji, ikonsa, da abubuwan banmamakin da ya aikata.
They were not hid from their children to a second generations; [the fathers] declaring the praises of the Lord, and his mighty acts, and his wonders which he wrought.
5 Ya kafa ƙa’idodi wa Yaƙub ya kuma kafa doka a cikin Isra’ila, wadda ya umarce kakanni-kakanninmu su koya wa’ya’yansu,
And he raised up a testimony in Jacob, and appointed a law in Israel, which he commanded our fathers, to make it known to their children:
6 don tsara na biye su san su, har da’ya’yan da ba a riga an haifa ba, su kuma su faɗa wa’ya’yansu.
that another generation might know, even the sons which should be born; and they should arise and declare them to their children.
7 Ta haka za su dogara ga Allah ba kuwa za su manta da ayyukansa ba amma za su kiyaye umarnansa.
That they might set their hope on God, and not forget the works of God, but diligently seek his commandments.
8 Ba za su zama kamar kakanni kakanninsu ba, masu taurinkai da kuma tsara masu tayarwa, waɗanda zukatansu ba su yi biyayya ga Allah ba, waɗanda zukatansu ba su yi aminci ga Allah ba.
That they should not be as their fathers, a perverse and provoking generation; a generation which set not its heart aright, and its spirit was not steadfast with God.
9 Mutanen Efraim, ko da yake suna da bakkuna, suka juya da baya a ranar yaƙi;
The children of Ephraim, bending and shooting [with] the bow, turned [back] in the day of battle.
10 ba su kiyaye alkawarin Allah ba suka kuma ƙi su yi rayuwa ta wurin dokarsa.
They kept not the covenant of God, and would not walk in his law.
11 Suka manta da abin da ya aikata, abubuwan banmamakin da ya nuna musu.
And they forgot his benefits, and his miracles which he [had] showed them;
12 Ya yi mu’ujizai a idanun kakanninsu a ƙasar Masar, a yankin Zowan.
the miracles which he wrought before their fathers, in the land of Egypt, in the plain of Tanes.
13 Ya raba teku ya kuma bi da su ciki; ya sa ruwa ya tsaya daram kamar bango.
He clave the sea, and led them through: he made the waters to stand as [in] a bottle.
14 Ya bishe su da girgije da rana da kuma haske daga wuta dukan dare.
And he guided them with a cloud by day, and all the night with a light of fire.
15 Ya tsage duwatsu a cikin hamada ya kuma ba su ruwaye a yalwace kamar tekuna;
he clave a rock in the wilderness, and made them drink as in a great deep.
16 ya fid da rafuffuka daga dutsen da ya tsaga ya sa ruwa ya gudu kamar koguna.
And he brought water out of the rock, and caused waters to flow down as rivers.
17 Amma suka ci gaba da yin masa zunubi, suna tayarwa a cikin hamada a kan Mafi Ɗaukaka.
And they sinned yet more against him; they provoked the Most High in the wilderness.
18 Da gangan suka gwada Allah ta wurin neman abincin da suke kwaɗayi.
And they tempted God in their hearts, in asking meat for [the desire of] their souls.
19 Suka yi magana a kan Allah, suna cewa, “Allah zai iya shimfiɗa tebur a cikin hamada?
They spoke also against God, and said, Will God be able to prepare a table in the wilderness?
20 Sa’ad da ya bugi dutse, ruwa ya ɓulɓulo, rafuffuka suka yi gudu a yalwace. Amma zai iya ba mu abinci? Zai iya tanada wa mutanensa nama?”
Forasmuch as he struck the rock, and the waters flowed, and the torrents ran abundantly; will he be able also to give bread, or prepare a table for his people?
21 Sa’ad da Ubangiji ya ji su, ya yi fushi ƙwarai; wutarsa ta ɓarke a kan Yaƙub, hasalarsa kuwa ta tashi a kan Isra’ila,
Therefore the Lord heard, and was provoked: and fire was kindled in Jacob, and wrath went up against Israel.
22 gama ba su gaskata ga Allah ba ko su dogara ga cetonsa.
Because they believed not in God, and trusted not in his salvation.
23 Duk da haka ya ba da umarni ga sarari a bisa ya kuma buɗe ƙofofin sammai;
Yet he commanded the clouds from above, and opened the doors of heaven,
24 ya sauko da Manna wa mutanensa don su ci, ya ba su hatsin sama.
and rained upon them manna to eat, and gave them the bread of heaven.
25 Mutane suka ci burodin mala’iku; ya aika musu dukan abincin da za su iya ci.
Man ate angels' bread; he sent them provision to the full.
26 Ya saki iskar gabas daga sammai ya kuma saki iskar yamma ta wurin ikonsa.
He removed the south wind from heaven; and by his might he brought in the southwest wind.
27 Ya sauko da nama a kansu kamar ƙura, tsuntsaye masu firiya kamar yashi a bakin teku.
And he rained upon them flesh like dust, and feathered birds like the sand of the seas.
28 Ya sa suka sauka a cikin sansaninsu, ko’ina kewaye da tentunansu.
And they fell into the midst of their camp, round about their tents.
29 Suka ci har suka sami fiye da abin da ya ishe su, gama ya ba su abin da suka yi kwaɗayi.
So they ate, and were completely filled; and he gave them their desire.
30 Amma kafin su juyo daga abincin da suka yi kwaɗayi, kai tun ma yana a bakunansu,
They were not disappointed of their desire: [but] when their food was yet in their mouth,
31 fushin Allah ya ƙuna a kansu; ya karkashe waɗanda suka fi ƙiba a cikinsu, yana yankan matasan Isra’ila.
then the indignation of God rose up against them, and killed the fattest of them, and overthrew the choice men of Israel.
32 Duk da haka, suka ci gaba da yin zunubi; duk da abubuwan banmamakinsa, ba su gaskata ba.
In the midst of all this they sinned yet more, and believed not his miracles.
33 Saboda haka ya sa kwanakinsu suka ƙare a banza shekarunsu kuma cikin masifa.
And their days were consumed in vanity, and their years with anxiety.
34 A duk sa’ad da Allah ya kashe su, sai su neme shi; sukan juyo a natse gare shi.
When he killed them, they sought him: and they returned and called betimes upon God.
35 Sun tuna cewa Allah ne Dutsensu, cewa Allah Mafi Ɗaukaka ne Mai fansarsu.
And they remembered that God was their helper, and the most high God was their redeemer.
36 Amma sai su yi ta yin masa zaƙin baki, suna masa ƙarya da harsunansu;
Yet they loved him [only] with their mouth, and lied to him with their tongue.
37 zukatansu ba sa biyayya gare shi, ba su da aminci ga alkawarinsa.
For their heart [was] not right with him, neither were they steadfast in his covenant.
38 Duk da haka ya kasance mai jinƙai; ya gafarta laifofinsu bai kuwa hallaka su ba. Sau da sau ya janye fushinsa bai kuwa sa fushinsa yă ƙuna ba.
But he is compassionate, and will forgive their sins, and will not destroy [them]: yes, he will frequently turn away his wrath, and will not kindle all his anger.
39 Ya tuna cewa su naman jiki ne kawai, iska mai wucewa da ba ta dawowa.
And he remembered that they are flesh; a wind that passes away, and returns not.
40 Sau da yawa sun tayar masa a cikin hamada suka kuma ɓata masa rai a jeji!
How often did they provoke him in the wilderness, [and] anger him in a dry land!
41 Sau da sau suka riƙa gwada Allah; suka tsokane Mai Tsarki na Isra’ila.
Yes, they turned back, and tempted God, and provoked the Holy One of Israel.
42 Ba su tuna da ikonsa, a ranar da ya fanshe su daga mai danniya,
They remembered not his hand, the day in which he delivered them from the hand of the oppressor.
43 ranar da ya nuna mu’ujizansa a Masar abubuwan banmamakinsa a yankin Zowan ba.
How he had wrought his signs in Egypt, and his wonders in the field of Tanes:
44 Ya mai da kogunansu suka zama jini; ba su iya sha daga rafuffuka ba.
and had changed their rivers into blood; and their streams, that they should not drink.
45 Ya aika da tarin ƙudajen da suka cinye su, da kwaɗin da suka wahalshe su.
He sent against them the dog-fly, and it devoured them; and the frog, and it spoiled them.
46 Ya ba da hatsinsu ga fāra, amfanin gonakinsu ga ɗango.
And he gave their fruit to the canker worm, and their labours to the locust.
47 Ya lalace inabinsu da ƙanƙara itatuwan al’ul nasu kuma da jaura.
He killed their vines with hail, and their sycamores with frost.
48 Ya miƙa shanunsu ga ƙanƙara, tumakinsu ga aradun tsawa.
And he gave up their cattle to hail, and their substance to the fire.
49 Ya saki musu fushinsa mai zafi, hasalarsa, zafin rai da kuma ɓacin ransa, ƙungiyar mala’iku masu hallakarwa.
He sent out against them the fury of his anger, wrath, and indignation, and affliction, a message by evil angels.
50 Ya shirya hanya wa fushinsa; bai tsare ransu daga mutuwa ba amma ya miƙa su ga annoba.
He made a way for his wrath; he spared not their souls from death, but consigned their cattle to death;
51 Ya bugi kowane ɗan fari na Masar, mafari ƙarfin mazantakansu a tentunan Ham.
and struck every firstborn in the land of Egypt; the first fruits of their labours in the tents of Cham.
52 Amma ya fitar da mutanensa kamar garke; ya bi da su kamar tumaki ta cikin hamada.
And he removed his people like sheep; he led them as a flock in the wilderness.
53 Ya bi da su lafiya ƙalau, don kada su ji tsoro; amma teku ya cinye abokan gābansu.
And he guided them with hope, and they feared not: but the sea covered their enemies.
54 Ta haka ya kawo su iyakar ƙasa mai tsarki, zuwa ƙasar tudun da hannunsa na dama ya kame.
And he brought them in to the mountain of his sanctuary, this mountain which his right hand had purchased.
55 Ya kori al’ummai a gabansu ya rarraba ƙasashensu gare su a matsayin gādo; ya zaunar da kabilan Isra’ila a gidajensu.
And he cast out the nations from before them, and made them to inherit by a line of inheritance, and made the tribes of Israel to dwell in their tents.
56 Amma suka gwada Allah suka tayar wa Mafi Ɗaukaka; ba su kiyaye ƙa’idodinsa ba.
Yet they tempted and provoked the most high God, and kept not his testimonies.
57 Kamar kakanninsu suka zama marasa biyayya da marasa aminci, marar tabbas kamar tanƙwararren baka.
And they turned back, and broke covenant, even as also their fathers: they became like a crooked bow.
58 Suka ba shi haushi da masujadansu na kan tudu; suka tayar da kishinsa da gumakansu.
And they provoked him with their high places, and moved him to jealousy with their graven images.
59 Sa’ad da Allah ya ji su, ya yi fushi ƙwarai; ya ƙi Isra’ila gaba ɗaya.
God heard and lightly regarded [them], and greatly despised Israel.
60 Ya yashe tabanakul na Shilo, tentin da ya kafa a cikin mutane.
And he rejected the tabernacle of Selom, his tent where he lived amongst men.
61 Ya aika da akwatin alkawarin ƙarfinsa zuwa bauta, darajarsa zuwa cikin hannuwan abokin gāba.
And he gave their strength into captivity, and their beauty into the enemy's hand.
62 Ya ba da mutanensa ga takobi; ya yi fushi ƙwarai da gādonsa.
And he gave his people to the sword; and disdained his inheritance.
63 Wuta ta cinye matasansu maza,’yan matansu kuma ba su da waƙoƙin aure;
Fire devoured their young men; and their virgins mourned not.
64 aka karkashe firistocinsu, gwaurayensu kuwa ba su iya makoki ba.
Their priests fell by the sword; and their widows shall not be wept for.
65 Sa’an nan Ubangiji ya farka sai ka ce daga barcinsa, kamar yadda mutum kan farka daga buguwar ruwan inabi.
So the Lord awaked as one out of sleep, [and] as a mighty man who has been heated with wine.
66 Ya kori abokan gābansa; ya sa suka sha madawwamiyar kunya.
And he struck his enemies in the hinder parts: he brought on them a perpetual reproach.
67 Sa’an nan ya ƙi tentunan Yusuf, bai zaɓi kabilar Efraim ba;
And he rejected the tabernacle of Joseph, and chose not the tribe of Ephraim;
68 amma ya zaɓi kabilar Yahuda, Dutsen Sihiyona, wanda ya ƙaunaci.
but chose the tribe of Juda, the mount Sion which he loved.
69 Ya gina wurinsa mai tsarki kamar bisa, kamar duniyar da ya kafa har abada.
And he built his sanctuary as [the place] of unicorns; he founded it for ever on the earth.
70 Ya zaɓi Dawuda bawansa ya kuma ɗauke shi daga ɗakin tumaki;
He chose David also his servant, and took him up from the flocks of sheep.
71 daga kiwon tumaki ya kawo shi don yă kuma zama makiyayin mutanensa Yaƙub, na Isra’ila gādonsa.
He took him from following the ewes great with young, to be the shepherd of Jacob his servant, and Israel his inheritance.
72 Dawuda kuwa ya zama makiyayinsu da mutuncin zuciya; da hannuwa masu gwaninta ya bi da su.
So he tended them in the innocency of his heart; and guided them by the skilfulness of his hands.

< Zabura 78 >