< Zabura 73 >

1 Zabura ta Asaf. Tabbatacce Allah mai alheri ne ga Isra’ila, ga waɗanda suke masu tsabta a zuciya.
A Psalm by Asaph. Surely God is good to Israel, to those who are pure in heart.
2 Amma game da ni, ƙafafuna suna gab da yin santsi; tafin ƙafana ya yi kusan zamewa.
But as for me, my feet were almost gone. My steps had nearly slipped.
3 Gama na yi kishin masu girman kai sa’ad da na ga cin gaban da masu mugunta suke yi.
For I was envious of the arrogant, when I saw the prosperity of the wicked.
4 Ba sa yin wata fama; jikunansu lafiya suke da kuma ƙarfi.
For there are no struggles in their death, but their strength is firm.
5 Ba sa shan wata wahalar da sauran mutane ke sha; ba su da damuwa irin na’yan adam.
They are free from burdens of men, neither are they plagued like other men.
6 Saboda girman kai ya zama musu abin wuya; tā da hankali ya zama musu riga.
Therefore pride is like a chain around their neck. Violence covers them like a garment.
7 Daga mugayen zukatansu laifi kan fito mugaye ƙulle-ƙullen da suke cikin zukatansu ba su da iyaka.
Their eyes bulge with fat. Their minds pass the limits of conceit.
8 Suna ba’a, suna faɗin mugayen abubuwa; cikin girman kan suna barazana yin danniya.
They scoff and speak with malice. In arrogance, they threaten oppression.
9 Bakunansu na cewa sama na su ne, kuma harsunansu sun mallaki duniya.
They have set their mouth in the heavens. Their tongue walks through the earth.
10 Saboda haka mutanensu sun juya gare su suna kuma shan ruwa a yalwace.
Therefore their people return to them, and they drink up waters of abundance.
11 Suna cewa, “Yaya Allah zai sani? Mafi Ɗaukaka yana da sani ne?”
They say, “How does God know? Is there knowledge in the Most High?”
12 Ga yadda mugaye suke, kullum ba su da damuwa, arzikinsu yana ta ƙaruwa.
Behold, these are the wicked. Being always at ease, they increase in riches.
13 Tabbatacce a banza na bar zuciyata da tsabta; a banza na wanke hannuwa don nuna rashin laifi.
Surely I have cleansed my heart in vain, and washed my hands in innocence,
14 Dukan yini na sha annoba; an hukunta ni kowace safiya.
For all day long I have been plagued, and punished every morning.
15 Da na ce, “Zan faɗa haka,” da na bashe’ya’yanka.
If I had said, “I will speak thus”, behold, I would have betrayed the generation of your children.
16 Sa’ad da na yi ƙoƙari in gane wannan, sai ya zama danniya a gare ni
When I tried to understand this, it was too painful for me—
17 sai da na shiga wuri mai tsarki na Allah; sa’an nan na gane abin da ƙarshensu zai zama.
until I entered God’s sanctuary, and considered their latter end.
18 Tabbatacce ka sa su a ƙasa mai santsi; ka jefar da su ga hallaka.
Surely you set them in slippery places. You throw them down to destruction.
19 Duba yadda suka hallaka farat ɗaya, razana ta share su gaba ɗaya!
How they are suddenly destroyed! They are completely swept away with terrors.
20 Kamar yadda mafarki yake sa’ad da mutum ya farka, haka yake sa’ad da ka farka, ya Ubangiji, za ka rena su kamar almarai.
As a dream when one wakes up, so, Lord, when you awake, you will despise their fantasies.
21 Sa’ad da zuciyata ta ɓaci hankalina kuma ya tashi,
For my soul was grieved. I was embittered in my heart.
22 na zama marar azanci da jahili; na zama kamar dabba a gabanka.
I was so senseless and ignorant. I was a brute beast before you.
23 Duk da haka kullum ina tare da kai; ka riƙe ni a hannun damana.
Nevertheless, I am continually with you. You have held my right hand.
24 Ka bishe ni da shawararka, bayan haka kuma za ka kai ni cikin ɗaukaka.
You will guide me with your counsel, and afterward receive me to glory.
25 Wa nake da shi a sama in ba kai ba? Ba na kuma sha’awar kome a duniya in ban da kai.
Whom do I have in heaven? There is no one on earth whom I desire besides you.
26 Jikina da zuciyata za su iya raunana, amma Allah ne ƙarfin zuciyata da kuma rabona har abada.
My flesh and my heart fails, but God is the strength of my heart and my portion forever.
27 Waɗanda suke nesa da kai za su hallaka; kakan hallaka dukan waɗanda suke maka rashin aminci.
For, behold, those who are far from you shall perish. You have destroyed all those who are unfaithful to you.
28 Amma game da ni, yana da kyau in kasance kusa da Allah. Na mai da Ubangiji Mai Iko Duka mafakata; zan yi shelar dukan ayyukanka.
But it is good for me to come close to God. I have made the Lord Yahweh my refuge, that I may tell of all your works.

< Zabura 73 >